Aminiya:
2025-09-24@11:17:40 GMT

Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700

Published: 25th, February 2025 GMT

Wani matashi ɗan shekara 32 ya soka wa ɗan uwansa wuƙa ya saboda Naira 700 a Unguwar Zara da ke Yankin Babban Birnin Tarayya.

Wani shaida a unguwar ya bayyana cewa lamarin ya faru ne bayan wanda ake zargin ya kutsa ɗakin yayan nasa ya ɗauke masa Naira 700 daga aljihunsa.

Ana zargin wanda a ya yi aika-aikan ya shiga dakin ne bayan wan nasa ya tafi Sallar Isha’i

Bayan ya dawo bai ga kuɗin ba, ya yi zargin ƙanin nasa da ɗaukar, ya bi sahunsa, inda ya riske shi a wata mashaya ya je sayen tabar wiwi.

Ba ni lokacin cacar baka da El-Rufai —Nuhu Ribadu NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi?

A nan ne taƙaddama ta ɓarke a tsakaninsu, inda ƙanin ya zaro wuƙa ya daɓa masa, sannan ya tsere bayan ya ga ’yan banga za su kawo ɗauki.

Sanusi ya ce ’yan banga da sauran mutane ne suka kai wan nasa asibiti.

Wani ɗan banga, Bala Suleiman, ya bayyana cewa ganin su ne ya sa wanda ake zargin ya tsere.

Ya ƙara da cewa wanda ake zargin sanannen ɗan shaye-shaye, kuma a baya ya taɓa kai wa wasu mutum uku farmaki.

Ya ce suna ci gaba da bin sawunsa, kuma wanda aka taka wa wukar yana samun sauƙi a asibiti.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: shaye shaye

এছাড়াও পড়ুন:

An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya

Tawagar jami’an diflomasiyyan Falasɗinu ta gudanar da bikin ɗaga tutar ƙasar a Litinin ɗin nan a birnin Landan kamar yadda kafar labarai ta DW ta ruwaito.

Bikin ɗaga tutar na zuwa ne kwana guda bayan da Birtaniya ta amince da Falasɗinu a matsayin kasa mai cin gashin kanta.

CAC ta soma yi wa kamfanoni rijista da fasahar AI Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai

Shugaban tawagar jami’an diflomasiyyan Falasdinawa a Burtaniya Husam Zomlot, ya daga wani allo mai ɗauke da rubutun ‘Ofishin jakadancin Falasɗinu’ sannan kuma ya ce nan ba da jimawa ba za a buɗe ofishin a hukumance bayan kammala wasu sharudda dangane da dokoki da kuma tsarin gudanarwa.

Mista Zomlot ya yi jinjina ta musamman ga matakin Burtaniya na amincewa da kasar Falasɗinu da aka daɗe ana jira.

Ya ƙara da cewa yin hakan zai kawo ƙarshen zalunci na dogon lokaci, a daidai gabar da Falasɗinawa ke fuskantar matsananciyar wahala.

Birtaniya wadda ta daɗe tana goyon bayan Isra’ila ta juya mata baya, sakamakon hare-haren da Isra’ilar take kai wa Zirin Gaza, wanda ya samo asali bayan da ƙungiyar Hamas ta kai wani mummunan hari a ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

Tun a watan Yulin wannan shekarar Firaministan Birtaniya, Keir Starmer ya ce zai goyi kafa ƙasar Falasɗinu yana mai gindaya wa Isra’ilar sharaɗin yanke wannan shawarar.

A wancan lokacin Starmer ya ce zai amince da ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ilar ba ta ɗauki wani ƙwaƙƙwaran mataki na cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da Hamas ba kafin babban taron Majalisar Dinkin Duniya na watan Satumba.

Sai dai a ranar Lahadi, Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya zargi ƙasashen da suka sanar da aniyar amincewa da ƙasar Falasɗinu a matsayin masu ƙarkafa wa ta’addanci gwiwa.

Haka kuma, Netanyahu ya sake nanata cewa muradin samar da ƙasar Falasɗinu ba zai taba cika ba, tare da yin barazanar faɗaɗa mamayar Gabar Yamma da Kogin Jordan.

A yayin da Birtaniya, Australia da kuma Canada suka bi sabun sauran ƙasashen duniya sama da 140 domin amincewa da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai ’yanci, a nahiyar Afirka kuwa, yanzu haka ƙasashe 52 daga cikin 54 ne suka amince da wannan ’yanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun ci ribar Naira biliyan 601 a watanni shidan farkon 2025 – Bankin GT
  • An ƙona al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • An ƙone al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya
  • Bayan Mutuwar Wani Matashi, An Kafa Dokar Ta Baci A Yauri
  • An rufe sansanin NYSC da kasuwanni saboda rashin tsaro a Kwara
  • APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027
  • ’Yan sanda sun kama mutane 5 kan zargin satar abincin yara a Borno
  • Babu Wanda Ya Jawo Ra’ayina  Zuwa Masana’antar Kannywood —Umar Hassan (2)
  • An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina