Amurka Ta Laftawa Iran Wasu Sabbin Takunkumai
Published: 25th, February 2025 GMT
Gwamnatin Trump ta saka sabbin takunkumai kan wasu mutane da ke da alaka da wani kamfanin fitar da mai na Iran.
Takunkuman sun shafi mutane 22 da jiragen ruwa 13 da ke da alaka da masana’antar mai ta Iran.
Wadannan takunkumin wani bangare ne na matsin lamba na shugaban Amurka Donald Trump kan Iran.
Ma’aikatar Baitulmali ta Amurka ta sanar da cewa, takunkumin na da nufin gurgunta harkokin hada-hadar kudi da kuma cinikin man fetur na Iran, da nufin takaita shirinta na nukiliya.
Iran dai na mai kakkausar suka kan takunkuman na Amurka, tana mai kallonsu a matsayin sabawa ka’idojin kasa da kasa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya sanar da sake haka sabbin rijiyoyin man fetur guda hudu yankin Kolmani na jihar Bauchi, kamar yadda Darakta a kamfanin, Yusuf Usman ya tabbatar.
Daraktan ya kuma sake jaddada aniyar kamfanin ta ganin ya fara aikin hako danyen man fetur a Arewacin Najeriya.
Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kuraYa bayyana hakan ne ranar Laraba a Kaduna a rana ta biyu ta taron tattaunawa tsakanin gwamnati da jama’a da Gidauniyar Tunawa da Ahmadu Bello ta shirya.
Daraktan ya ce, “Ya zuwa yanzu, NNPCL ya tono sabbin rijiyoyin danyen man fetur guda hudu a yankin Kolmani na jihar Bauchi, kuma yan kan aikin tantance fasahar da ta fi dacewa a yi aiki da ita a mataki na gaba a aikin.
“A wani yunkurinmu kuma na taimaka wa shirin Shugaban Kas ana komawa amfani da ababen hawa masu amfani da makamashin iskar gas a maimakon man fetur, yanzu haka ana can ana aikin gina tashoshin canza motoci zuwa masu amfani da gas na CNG da LNG,” in ji shi.
Ya ce da zarar an kammala aikinsu, ana sa ran tashoshin za su taimaka wajen bunkasa samuwar gas din kuma cikin sauki a Arewacin Najeriya.
Yusuf ya kuma zayyana wasu muhimman ayyuka da nasarorin da kamfanin ya samu a Arewacin Najeriya da ma sauran sassan kasar a karkashin mulkin Shugaban Kasa Bola Tinubu.