Bayan da jami’an tsaro a kasar Burtania suka kama wani fitaccen mai gwagwarmayar kare hakkin Falasdinawa da kuma goya masu baya, a kwanakin da suka gabata. Wasu yan kasar sun gudanar da taro don tattaun makomar incin fadin albarkacin baki a kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wadanda suka yi magana a taron a yau Lahadi, suna cewa batun encin fadin albarkacin baki, da kuma kare hakkin b il’adama yana kara tabarbarewa a kasar.

Labarin ya kara da  cewa a ranar asabar da ta gabata ce, masu zanga-zanga a manya manyan  birana a kasar Burtaniya suna fito kan tituna inda suke, goyon bayan al-ummar Falasdinu, sun bukaci a kawo karshen mamayar kasar Falasdinu, a kawo karshen goyon bayan da kasashen yamma suke bawo HKI kan Falasdinawa. A kawo karshen mamayar kasashen larabawa sannan a sake gida zirin gaza bayan rusashi wanda HKI a cikin watanni 15 da suka gabata.

A birnin londan kadai, yawan masu zanga-zanga ta lumana sun kai kimani 80,000, sun bukaci a kawo karshen takurawar da suke wa kasashen Lebanon da Iran.

A yayin zanga-zangar dai yansanda sun kama mutane kimani 77 suka kuma gurfanar da su a gaban Kotu. Sanan sun bukaci fitattun yan siyasar kasar wadanda suke cikin zanga zangar wato Jeremy Corbyn tsohon shugaban  jam’iyyar Labo da kuma dan majalisa John McDonnell duk su kai kansu gaban jami’an tsaro don amsa tambayoyi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Dickson ya goyi bayan buƙatar gudanar da bincike kan jinkirin aiwatar da kasafin yana mai jaddada cewa matsalar ba ta shafi rashin kudi ba tare da kira ga majalisar ta umarci kwamitocin kasafin kudi su gudanar da bincike cikin mako guda su kuma kawo rahoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City
  • Bincike Ya Tabbatar da Cewa HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 Tun Bayan Fara Yaki A Gaza
  • Kalibof Ya Mayarwa Shugaban Kasar Amurka Martani Kan Mummunan Kalamansa
  • Mummunan Hatsari Ya Lashe Rayukan ‘Yan Mata 18 A Kasar Masar Dukkaninsu ‘Yan Kasa DA Shekara 21
  • An Fara Gudanar Da Jana’izar Shahidan Yakin Kwanaki 12 A nan Tehran
  • Jiniyoyin Gargadi Sun Tashi A HKI A Lokacinda Mayakan Ansarallah Suka Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kasar
  • Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
  • Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC
  • WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
  • Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson