2025-09-18@19:39:44 GMT
إجمالي نتائج البحث: 1068

«a safiyar yau»:

(اخبار جدید در صفحه یک)
    Iran ta yi kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa kuma a hukumance kan zaluncin ‘yan sahayoniyya da Amurka Mataimakin babban jami’in kula da harkokin kasa da kasa na ma’aikatar shari’a kuma sakataren hukumar kare hakkin bil’adama ta Iran ya yi la’akari da matakin wuce gona da iri na baya-bayan nan da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka yi kan cibiyoyin makamashin nukiliya, da kafofin yada labarai, da cibiyoyin kiwon lafiya na Iran, da kuma wuraren zama, gidajen yari da birane da kauyuka, a matsayin misali karara na keta dokokin kasa da kasa da hakkokin bil’adama. A cikin wata wasika da ya aike wa kwamishinan kare hakkin bil-Adama na Majalisar Dinkin Duniya Volker Türk Nasser Seraj mataimakin shugaban hukumar...
    A nata bangare hukumar CAEA ta ce za ta hada hannu da hukumar kula da makamashin nukuliya ta duniya IAEA da sauran abokan hulda daga kasashe masu tasowa, wajen inganta kirkire-kirkire da raya makamashin nukiliya. (Fa’iza Mustapha) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Matsalolin Da Muke Fuskanta:                     Bayan shekar 22 da kubutar da Nijeriya daga mulkin soja, dimokuradiyya na ci gaba da fama da rauni mai tsanani. Alamun cutar sun bayyana ne a cinikin baragurbin wakilai (delegates), amfani da kudin kasa da aka wawure ta hanyar haram wajen gudanar da yakin neman zabe, makudan kudin da ake ware wa Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), karancin yawan masu kada kuri’a, sayen kuri’u a bainar jama’a, tashin hankali yayin zabe, da kuma yaduwar fargaba, musamman a tsakanin matasa, cin amana na ’yan siyasa, canja sheka da zababbu ke yi, da dai sauran makamantansu.                                        Asalin matsalar ita ce, rashin shiga cikin gudanar da gwamnati a siyasance (edclusion) na masu gaskiya da rikon amana, matasa, mata, masu...
    Har yanzu dai gwamnatin Syriya ba ta komai ba game da barna da hasarar rayuka da makamai da kuma jiragen da ake amfani da su da ta sararin samaniyarta ke haifarwa ba. Shafin Intanet na kafar Enab na kasar Syria ya wallafa wani labari a ranar 15 ga watan Yuni game da shirun da gwamnatin Syriya ta yi kan karakainar da jiragen yaki da makamai masu linzami ke yi a sararin samaniyar kasar. Wani mai sharhi ya fada wa Enab cewa gwamnatin Syriya ta yanke shawarar tsayawa tsakiya kan lamarin ne kasancewar tana daukar Isra’ila da Iran a matsayin abokan gabarta. Ya ce: “Babu daya daga cikinsu da za ka bayyana shi a matsayin abokin al’ummar Syriya, kuma dukkaninsu sun...
    Mahaifin angon da ’yan uwan angon na jini da danginsa na daga cikin mutane 13 da aka yi wa kisan gilla a hanyar ɗaurin auren ango, inda aka ƙona gawarwarkin wasunsu a cikin motar da ta ɗauko su, a yankin Mangun da ke ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato. Mahaifiyar angon, Malama Faji Sani da ke zaune a ƙauyen ɗan Bami Anguwar Rimi a ƙaramar Hukumar Kudan ta Jihar Kaduna, ta shaida wa Aminiya cewa mijinta da ’ya’yanta biyu da ƙannenta biyu da kuma kishiyarta, na cikin mutanen da aka kashe su a harin na ranar Juma’a da dare. Ta ce mijin nata, Alhaji Sani, wanda da shi suka dogara, ya rasu ya bar ’ya’ya 13 da jikoki da dama....
    To sai dai ana bibiyar kwallon kafa tsakanin magoya baya a Nahiyar Turai da Kudancin Amurka, sannan kowacce takan samar da fitattun ‘yan wasan da suke fice a nahiyar da kuma duniya a fannin kwallon kafa. Wannan yana biyo bayan zuba hannun jari da bunkasa wuraren wasan kwallon kafa da gasa mai inganci da kayatarwa musamman a Nahiyar Turai. Nahiyar Turai ta lashe kofin duniya guda 12, idan ka kwanta da tara da Kudancin Amurka ta dauka a tarihi. Kungiyoyin Turai, musammam masu buga gasar English Premier League da Spanish La Liga da Bundesliga ko Serie A, sune suka mamaye lashe Champions League da kuma Club World Cup a tarihi. Sannan nahiyar Turai tana zuba kudi da hannun jari a...
    “Muna bayar da wannan a matsayin gargadi kai tsaye ga gwamnatin Nijeriya a matakin tarayya da na jihohi. Ka da a bari a zubar da jinin wadannan ‘yan Nijeriya marasa laifi ya tafi a banza.” Shittu, ya lura da cewa hakurin al’ummomin da ake ci gaba da yi wa kisan gilla ba shi da iyaka, ya kara da cewa rashin kamawa da gurfanar da masu aikata laifukan tare da hukuntansu yana nuna gazawar gwamnati. “Muna bukatar a gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa, kuma na gaskiya kan wannan kisan kiyashi da kamawa tare da gurfanar da duk wadanda ke da alhakin wannan danyen aikin.  “Muna san a biya isasshiyar diyya ga iyalan wadanda abin ya shafa, haka kuma a...
    Kamfanin Dillancin Labarun “Mehr” ya nakalto cewa;  Tun da jijjfin safiyar yau Asabar ne tasoshin jiragen kasa da na safa-safa su ka cika makil da masu son halarta babban filin Juyi na Tehran da can ne zai zama masonin rakiyar shahidan zuwa makwancinsu na karshe. Ana iya ganin dubun dubatar mutane da su ka fito daga kowane bangare na al’ummar Iran domin halartar jana’izar ,yara, mata, masana da kwamandojin soja,  wacce ta  fara da misalin karfe 8;00 na safiyar yau agogon Tehran. Adadin shahidan da ake jana’izar tasu a yau, sun kai 60, za kuma a rufe su ne a makabartar “Baheshti-Zahra” wacce take kunshe da shahidan juyin juya halin musulunci. A shirnmu na rana za a ji cikakken bayani...
    Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin aure da aka kashe a Jihar Filato. Tun da farko, Hakimin Basawa, Haruna Abubakar ne, ya wakilci Sarkin lokacin da lamarin ya faru, saboda Sarkin ya yi tafiya. Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC Sarkin, ya bayyana baƙin cikinsa bisa wannan mummunan lamari, inda ya roƙi iyalan da su ɗauki wannan a matsayin ƙaddara. Ya yaba da yadda suka yi haƙuri kuma suka bar komai ga hukuma, ba tare da ɗaukae doka a hannunsu ba. Sarkin ya kuma tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Kaduna na ƙoƙarin ganin an bi wa waɗanda abin...
    Aƙalla mutum ɗaya ne aka tabbatar da mutuwarsa tare da wasu biyar suna jinya bayan da wata babbar mota ƙirar tirela ta ƙwace ta kutsa cikin kasuwar Mile Six da ke Jalingo babban birnin Jihar Taraba. Shaidun gani da ido a wurin sun bayyana cewa, duk ƙoƙarin da direban motar ya yi na hana afkuwar lamarin ya ci tura. Ƙudan zuma ya tarwatsa ɗaliban da ke jarrabawar NECO ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe Aƙalla motoci biyu ne suka yi mummunan lalacewa a lamarin. Jami’an Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) da hukumar tsaro ta farin kaya sibil defens (NSCDC) da kuma rundunar ’yan sandan Najeriya (NPF) sun halarci wurin da jajantawa yankin...
    A wani mataki na ba-zata, shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya yi murabus daga muƙaminsa nan take. Ganduje, wanda tsohon gwamnan Jihar Kano ne, ya bayyana dalilan rashin  lafiyarsa ne ya sa ya  ɗauki matakin murabus, inda ya bayyana cewa yana buƙatar ya maida hankali kan lafiyarsa.
    Ban da haka kuma, wani babban dalilin da ya sa kasar Sin ke kokarin tallafa wa sauran kasashe a fannin aikin likitanci, shi ne akidarta ta “kafa al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai-daya”. A cikin gidan kasar, an yi nasarar kawar da talauci, da kokarin neman wadatar da dukkan al’ummun kasar, lamarin da ya sa ake samun jituwa a tsakanin al’umma, da ci gaban tattalin arziki mai dorewa. Saboda haka, kasar Sin na ganin cewa, kamata ya yi, a yi kokarin tabbatar da ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban na bai-daya, inda za a dinga rage gibin dake tsakanin kasashe, da na zaman rayuwar al’ummu daban daban, ta yadda za a iya daidaita matsalolin da dan Adam ke...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Kula da lafiya na nufin yin abubuwa da ke kare mutum daga kamuwa da cututtuka da kuma tabbatar da cewa jiki na aiki yadda ya kamata.   Wannan ya haɗa da cin abinci mai gina jiki, motsa jiki akai-akai, da dai sauran su. Sai dai a wannan zamani ‘yan Najeriya ba kasafai suke kula da lafiyar jikin su ba, a mafi yawan lokuta ma sai ciwo ya kwantar da mutum sannan yake tunawa da likita. Ko wadanne matakai ya kamata ‘yan Najeriya su ringa dauka wajen kare kan su da ma lafiyar jikin su? NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin...
    Dan wasan mai shekaru 40 ya zura kwallaye 93 sannan ya taimaka wajen zura 19 a wasanni 105 da ya buga a dukkanin wasannin da ya buga a kungiyar ta Saudiyya, amma har yanzu bai samu nasarar lashe kofi a gasar ba, a kakar wasan da aka kammala kwanan nan, Al Nassr ta kare a matsayi na uku a teburin, inda ta rasa gurbi a gasar cin kofin zakarun yankin Asia na shekara mai zuwa kuma a maimakon haka za ta buga gasar AFC Champions League 2.   Bugu da kari, Al Nassr a halin yanzu ba ta da koci tun bayan da ta raba gari da babban kocinta Stefano Pioli a ranar Laraba, wanda ya zama koci na uku...
    Arsenal na fatan sayen ɗan ƙwallon Brentford, Christian Norgaard, da zai maye gurbin Thomas Partey. Wasu majiya na cewa farashin da Arsenal za ta ɗauki ɗan wasan na tawagar Denmark mai shekara 31, zai kai £10m da karin £5m idan ya taka rawar gani da karin tsarabe-tsarabe. Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump ’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna Arsenal ta daɗe tana zawarcin Norgaard, wanda tanzu take fatan zai maye gurbin ɗan kasar Ghana, mai shekara 32, wanda bai amince da ƙunshin yarjejeniyar da Arsenal ta gabatar masa, domin ya ci gaba da taka mata leda. Kwantaragin Partey za ta kare a mako mai zuwa, idan...
    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce wakilan ƙasarsa za su gana da na Iran domin ci gaba da tattaunawa kan makaman nukiliyarta a mako mai zuwa. “Za mu tattauna da Iran a mako mai zuwa, ƙila mu ƙulla yarjejeniya ko kuma akasin haka, ba na ce ba,” in ji shi yayin jawabinsa a taron ƙasashe na ƙungiyar ƙawancen tsaro ta NATO da ake yi a ƙasar Netherlands. ’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano “Ba su daɗe da gama yaƙi ba, yanzu za su ci gaba da harkokinsu. Ban damu dole sai na ƙulla wata yarjejeniya da su ba,” a cewarsa. A jiya Talata...
    A yanzu haka, fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam ta AI na sauya zaman rayuwar dan Adam. Ga misalin, motoci mara matuki na saukaka tafiye-tafiye na dan Adam, samfurin binciken yanayi na iya hasashen hanyar guguwa a cikin dakika 10 kawai… Amma, fasaha ta zama kamar “takobi mai kaifi biyu”, wadda a lokaci daya take kuma kara haifar da matsaloli, kamar su fallasar sirri, yaudara ta hanyar amfani da AI, da hadarin rashin aikin yi. Bisa wannan yanayin da ake ciki na kasancewar alfanu‌ da ‌matsaloli tare, ‌’dan Adam na bukatar hadin gwiwa cikin gaggawa don daidaita ci gaban fasahar AI, da kafa tsarin gudanar da harkokin fasahar AI na duniya, da nemo daidaito tsakanin kirkire-kirkire da tsaro, da nufin tabbatar...
    Yaya girman neman fadadar kungiyar NATO yake? Alkaluma ne za su iya fayyacewa: Abun da aka kashe a duniya kan aikin soji a shekarar 2024 ya kai dala triliyan 2.72, inda kungiyar NATO ta dauki dala triliyan 1.5, wato kaso 55 na jimillar ta duniya. Duk da rashin daidaiton karfin soji tsakanin kasashen duniya, NATO na ci gaba da sanya mambobinta su kara abun da suke kashewa a bangaren tsaro zuwa kaso 5 na alkalumansu na GDP. Wani nazari da kafar CGTN ta gudanar ya nuna cewa, kaso 67.4 na wadanda suka bayar da amsa sun yi tir da yadda NATO ke gaggauta fadada karfinta na soji, suna gargadin hakan ka iya haifar da sabuwar takarar makamai da yin gagarumar...
    Da yake gabatar da kudirin, dan majalisar, Abdullahi ya nuna matukar damuwarsa kan kisan da aka yi wa matafiyan a ranar Juma’a, a lokacin da suka bata kan hanyarsu a yayin da suke tafiya don halartar wani daurin aure a karamar hukumar Mangu.   Ya ce, wadanda aka kashen, ba su dauke da wani makami, kawai suna kan hanyarsu ne ta zuwa daurin aure, wasu da ba a san ko su wanene ba suka kai musu hari tare da kashe su, lamarin da ya jefa ‘yan uwan matafiyan cikin jimami. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin...
    Shugaban Mali, Assimi Goita da takwaransa na Rasha, Vladimir Putin, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar makamashin nukiliya a fadar Kremlin da ke birnin Moscow. Wannan dai na cikin wasu yarjejeniyoyi da Mali da Rasha suka rattaba hannu waɗanda aka tsaro domin inganta alaƙar kasuwanci da tattalin arziki. Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya Shugaba Vladimir Putin ya shaida wa shugaban kasar ta Afirka ta Yamma da ke ziyara cewa akwai wasu fannoni na musamman da za a iya ƙara haɗin kai. Putin ya karbi bakuncin Kanal Assimi Goita a fadar Kremlin, inda suka tattauna tsawon awanni biyu, kamar yadda kafafen yaɗa labaran gwamnati...
    Shugaban Amurka Donald Trump ya soki Isra’ila da Iran, bayan zargin ƙasashen biyu da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da aka ƙulla. Lamarin na zuwa ne bayan ɓullar rahoton kai wa juna hari daga dukkan ƙasashen biyu, duk da ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta ’yan sa’o’in da suka gabata. Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya Trump ya ce ƙasashen sun daɗe suna faɗa da juna, kuma a wannan mataki ana iya cewa ba su ma san abin da suke yi ba. Ya ce: “Ba abin da muke so ke nan ba, ina tabbatar muku cewa ina fushi da abin da suka aikata.” Shugaba Trump ne mutum na...
    Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump ya zargi Iran da Isra’ila da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta. Da yake jawabi kafin tafiyar Babban Taron Ƙungiyar NATO, da zai gudana a birnin Hague, Trump, ya bayyana takaicinsa bisa yadda kasashen biyu game da saɓa yarjejeniyar, sa’o’i kaɗan bayan sun amince da ita. Tun da farko sai da ya buƙaci Isra’ila ta janye shirinta na kai wa Iran hari. A safiyar Litinin bayan sanarwar Trump cewa ɓangarorin sun amince su tsagaita wuta ne, Ministan Tsaron Isra’ila ya yi barazanar kai wa Iran hari mai tsanani bayan zargin ta da harbo wa ƙasarsa rokoki. Iran ta musanta zargin tare da cewa Isra’ila za ta yaba wa aya zaƙi idan kuskura ta kawo mata hari. Daga...
    A ranar 23 ga wata, Kirsty Coventry, wacce ta karbi ragamar shugabancin kwamitin wasannin Olympics ta kasa da kasa kwanan nan, ta yi hira ta musamman da wani shirin gidan talabijin na CCTV mai lakabin “High-End Interview” a birnin Lausanne na kasar Switzerland. Wannan ita ce hira ta farko da ta yi da kafar yada labarai tun bayan da ta karbi ragamar shugabancin kwamitin wasannin Olympics na duniya. Coventry ta ce ya zama wajibi a kiyaye kima da kuzarin wasannin motsa jiki na Olympics, tare da kara kiyaye su da kuma karfafa su. Ta ce, tana fatan yin mu’amala mai zurfi da dukkan masu ruwa da tsaki a watanni masu zuwa, tare da haduwa tare wajen tsara fasalin aiki na...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba A zamanin yau, ba kira da tura saƙo kawai ake yi da wayar hannu ba; baya ga haka, muhimmiyar hanya ce ta samun kuɗi da bunƙasa sana’o’i. Ko kun san dabarun amfani da wayoyinku don samun kuɗaɗen shiga? NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro? Idan ba ku sani ba, ko kuma kuna buƙatar ƙarin sani, ku biyo mu a shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci. Domin sauke shirin, latsa nan
    Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin ko kuma CMG a takaice, ya sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da gidauniyar Milano Cortina 2026, wanda aka dorawa alhakin shirya gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu ta Milano Cortina ta shekarar 2026 dake tafe. Yayin sanya hannu kan yarjejeniyar, sassan biyu sun amince su zurfafa hadin gwiwa a sassan yayatawa, da tsara ayyukan watsa gasar ta Olympics ta lokacin hunturu ta Milano Cortina, tare da aiwatar da musayar jami’ai. Sakamakon wannan hadin-gwiwa, CMG ya samu ikon watsa gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu ta Milano Cortina dake tafe a shekara mai zuwa a hukumance. An kafa gidauniyar Milano Cortina 2026 a watan Disamban shekarar 2019, domin ya tsara, da...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Matsalar tare fasinjoji da kashe su a hanyoyin Najeriya na ƙara tsananta, musamman a yankunan Arewa. Misali, a shekarun baya an sha tare matafiya a kashe su a hanyar Abuja zuwa Kano. A kwanakin baya ma an kashe wasu matafiya a garin Uromi da ke jihar Edo a hanyar su ta komawa Kano. Sai na kwanan nan da ya faru a Jihar Filato inda aka kashe wasu matafiya da ke kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure. NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro? Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne da...
    Idi ya kuma yi nazari kan matakin da bangaren kiwon dabbobin kasar yake, inda yawan Shanu suka kai miliyan 20.9, Tumaki miliyan 49.1, Awakai miliyan 88.2, Kajin gidan gona kuma miliyan  258.5. Kazalika, Maiha ya jaddada muhimmancin hadakar ta zuba hannun jari a fannin na kiwon dabbobin, wanda ya sanar da cewa; hakan zai taimaka matuka gaya wajen dakile yaduwar cututtukan da ke yi wa dabbobin illa. A nasa jawabin, Babban Shugaban Kamfanin Ricardo Lacerda ya bayyana cewa; kasar Brazil na shirin samar da wuraren kiwon dabbobi na zamani kimanin guda 200,000 a wasu daga cikin jihohin wannan kasa, musamman don kara samar da isasshen naman Shanu. Ya kara da cewa, kasar za kuma ta tabbatar da kokarin kara habaka...
    Yanzu haka ana shirye-shiryen gudanar da taron kasa da kasa na tattauna batutuwan raya tattalin arziki na Davos na yanayin zafi karo na 16, taron da aka fi sani da dandalin Davos. A bana za a gudanar da taron ne tsakanin ranakun Talata 24 zuwa Alhamis 26 ga watan nan na Yuni, a birnin Tianjin dake arewacin kasar Sin, bisa taken “sana’o’i a sabon zamani.” A bana taron zai mayar da hankali ne ga muhimman fannoni biyar, wadanda suka hada da warware batu game da tattalin arzikin duniya, da hange game da kasar Sin, da halin da masana’antun duniya suka fuskanta na taka musu birki, da zuba jari kan al’umma da duniyar bil’adama da batun sabbin makamashi da hajoji. Game...
    Gwamnatin yankin musamman na Hong Kong, ta gudanar da bikin murnar cika shekaru biyar da kafawa, da kaddamar da dokar tsaron kasa ta yankin. Yayin bikin da ya gudana a jiya Asabar, Xia Baolong, wanda shi ne shugaban ofishi mai lura da al’amuran yankunan Hong Kong da Macao a kwamitin kolin JKS, da ofishi mai lura da al’amuran yankunan Hong Kong da Macao a majalisar gudanarwa ta kasar Sin, ya ce dokar tsaron kasa ta yankin Hong Kong da aka kaddamar a ranar 30 ga watan Yunin shekarar 2020, ta samarwa yankin damar fita daga hargitsi zuwa yanayi na daidaito, tare da shigar da yankin sabon zamani na gudanar da tsarin “kasa daya tsarin mulki biyu”. Xia Baolong, ya ce...
    Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya zabi dan wasan tsakiya Bernardo Silba a matsayin sabon kyaftin din kungiyar, jaridar Daily Mail ta rawaito Guardiola ya yanke hukuncin da kan sa inda ya ki ya nemi shawarar sauran yan wasan kungiyar, Silba ya maye gurbin Kebin De Bruyne bayan dan kasar Belgium din ya bar Etihad a karshen kwantiraginsa. Guardiola ya kuma nada mataimakan kyaftin guda uku kafin fara gasar kakar wasa ta gaba da suka Ruben Dias, Rodri da Erling Haaland, Silba wanda kwantiraginsa zai kare a bazara mai zuwa, ka iya daura kambun kyaftin na Manchester City na kakar wasa daya kawai idan bai samu karin kwantiragi a kungiyar ba. Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun...
    Trump ya ce hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku, lallai zai kara rura wutar rikici a ci gaba da yakin da ake yi tsakanin Iran da Isra’ila.   Sai dai ministan harkokin wajen Iran Seyed Abbas Araghchi ya yi Allah wadai da harin da Amurka ta kai da cewa “abin takaici ne” sannan ya ce Iran ta tanadi “dukkan zabin kare ‘yancinta”, yana mai jaddada cewa Amurka za ta fuskanci “tsauraran sakamako”.   Araghchi ya kara da cewa, Amurka ta keta kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya a matsayinta na mamba a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya.   Bugu da kari, wani dan Majalisar kasar Iran, ya kara da cewa, “babu wani mummunan lahani...
    Hukumar kididdigar makamashi ta Amurka US Energy Information Administration (EIA) ta kiyasta cewa a farkon shekarar 2023 an yi dakon kusan ganga miliyan 20 na fetur a a kullum ta tekun. Wannan ke nufin ana kasuwancin kusan dala biliyan 600 na makamashi duk shekara ta tekun. Duk wani tsaiko a tekun zai iya jawo matsala a hada-hadar man fetur a duniya, wanda nan take za a iya gani ta hanyar tashin farashin man. Sai dai masana suna gargadin cewa daukar wannan matakin zai iya zafafa rikicin na Isra’ila da Iran. Wannan kuwa shi ne zai jawo wasu kasashen cikin rikicin, ciki har da Amurka, wadda take ta’allaka da man fetur daga kasashen Larabawa. Yaya girman mashigar Hormuz? Mashigar Hormuz na...
    Manyan kungiyoyin kwallon kafa a Turai Tottenham Hotspur da West Ham United na fafatawa wajen ganin sun dauki tauraron dan wasan Nijeriya dake buga kwallo a Club Brugge, Raphael Onyedika, ana alakanta Onyedika da barin kungiyar Club Brugge sakamakon rawar gani da ya taka a bana. Dan wasan na Nijeriya ya samu dimbin masu sha’awar raba shi da Brugge saboda bajintar da ya nuna a gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai ta bara, a cewar Transferfeed, kungiyoyin biyu na son siyan dan wasan tsakiyar a wannan bazarar, West Ham na son ya maye gurbin Tomas Soucek dan kasar Czech, wanda ke kan hanyarsa ta barin kungiyar. Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6 Diaz Ba Na...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Wakilin ƙasar Iran ya isa birnin Santanbul na ƙasar Turkiyya domin halartar taron Ƙungiyar Haɗin kan Kasashen Musulmi (OIC) a ranar Asabar. Kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ruwaito cewa, a yayin taron Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, zai gana da jami’an diflomasiyya na ƙasashen Larabawa don tattauna batun rikicin da ke ƙara ƙamari tsakanin ƙasarsa da Isra’ila. Kimanin jami’an diflomasiyya 40 ne ake sa ran za su halarci taron a daidai lokacin da Isra’ila da Iran ke ci gaba da musayar hare-haren makamai masu linzami. “Ministan harkokin wajen ya isa Istanbul a safiyar yau domin halartar taron ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan Musulunci,” in ji Tasnim. Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila Najeriya...
    Iran ta lalata cibiyar binciken kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila, wato cibiyar kimiyya ta Weizmann Institute of Science da ke birnin Tel Aviv. Cibiyar, wadda ke da alaƙa da binciken harkokin sojin Isra’ila, ta sanar da cewa harin da Iran ta kawo ɗin ya yi sanadiyar ɓarnar da ta kai kimanin Dala miliyan 500. Makaman Iran sun lalata gine-gine da dama a cibiyar, lamarin da ya sanya masu bincike faɗi-tashi don ceto samfurin bincike a cikin ɓaraguzan gini, a yayin da gobarar ke ci. Wani makami mai linzami ya tarwatsa wani gini mai ɗauke da ɗakunan gwaje-gwaje na zamani da dama, a yayin harin na ramuwar gayya, bayan da Isra’ila ta kashe masana kimiyyar nukiliya na Iran. 2027: Manyan ’Yan...
    Iran ta lalata cibiyar binciken kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila, wato cibiyar kimiyya ta Weizmann Institute of Science da ke birnin Tel Aviv. Cibiyar, wadda ke da alaƙa da binciken harkokin sojin Isra’ila, ta sanar da cewa harin da Iran ta kawo ɗin ya yi sanadiyar ɓarnar da ta kai kimanin Dala miliyan 500. Makaman Iran sun lalata gine-gine da dama a cibiyar, lamarin da ya sanya masu bincike faɗi-tashi don ceto samfurin bincike a cikin ɓaraguzan gini, a yayin da gobarar ke ci. Wani makami mai linzami ya tarwatsa wani gini mai ɗauke da ɗakunan gwaje-gwaje na zamani da dama, a yayin harin na ramuwar gayya, bayan da Isra’ila ta kashe masana kimiyyar nukiliya na Iran. 2027: Manyan ’Yan...
    Iran ta lalata cibiyar binciken kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila, wato cibiyar kimiyya ta Weizmann Institute of Science da ke birnin Tel Aviv. Cibiyar, wadda ke da alaƙa da binciken harkokin sojin Isra’ila, ta sanar da cewa harin da Iran ta kawo ɗin ya yi sanadiyar ɓarnar da ta kai kimanin Dala miliyan 500. Makaman Iran sun lalata gine-gine da dama a cibiyar, lamarin da ya sanya masu bincike faɗi-tashi don ceto samfurin bincike a cikin ɓaraguzan gini, a yayin da gobarar ke ci. Wani makami mai linzami ya tarwatsa wani gini mai ɗauke da ɗakunan gwaje-gwaje na zamani da dama, a yayin harin na ramuwar gayya, bayan da Isra’ila ta kashe masana kimiyyar nukiliya na Iran. Makamin ya faɗo...
    Mai bai wa Gwamna Uba Sani shawara kan harkokin kwadago, Adamu Samaila ne ya shaida wa wakilinmu cewa; nan bad a jimawa ba gwamnati za ta karbi rahotan tantance ma’aikatan da kuma yadda za a daidata albashin nasu. Samaila ya kara da cewa, “A mako mai zuwa ne za mu gana da wanda yake kula da aikin tantancewar, domin samun sakamakon rahoton albashin ma’aikatan.” Zamfara: Ba A Aiwatar Da Biyan Dari Bisa Dari Ba A Jihar Zamfara, gwamnati ba ta aiwatar da fara biyan sabon mafi karancin albashin ga ma’aikatanta ba. Guda daga cikin manyan jami’an gwamnatin da ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa wakilinmu cewa; mafi karancin albashin, zai fi mayar da hankali ne a kan ma’aikatan...
    Rundunar ’yan sandan Jihar Akwa Ibom ta kama wani mutum mai suna Alexander Peter bisa zarginsa da kashe mahaifiyarsa mai suna Madam Atiny Peter mai shekara 71 da adda. Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ikot Inyang da ke ƙaramar hukumar Oruk Anam a Jihar Akwa Ibom. Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Baba Mohammed Azare ne ya tabbatar da kamen a yayin ganawa da manema labarai a ranar Alhamis, a hedikwatar ’yan sanda da ke Ikot Akpan Abia, a Uyo. Kwamishinan ’yan sandan ya bayyana cewa, an kama wanda ake zargin Alexander ne a ranar...
    “An yi hasashen matsakaicin hadarin ambaliya ga al’ummomi 445 a cikin kananan hukumomi 116 daga Afrilu zuwa Yuni, 1,458 a kananan hukumomi 271 daga Yuli zuwa Satumba, da kuma 1,473 a kananan hukumomi 171 tsakanin Oktoba da Nuwamba,” in ji Ministan. Matakan aiki Da yake magana da wannan dan jarida, Shugaban Tsangayar Kimiyyar Muhalli na Jami’ar Jihar Nasarawa dake Keffi, Dokta Kante Pkantisawa, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su mai da hankali sosai kan hasashen yanayi da hukumar kula da yanayi ta Nijeriya (NiMET) da NHSA suka yi. Ya ce, “Ambaliyan da aka yi a Mokwa babbar tunatarwa ce game da tasirin sauyin yanayi da kuma bukatar daukar matakan da suka dace, babu wata fa’ida da ya wuce a ce...
    Wata kotun Majistare da ke zamanta a unguwar Nomansland a Kano ta tura wani matashin dan TikTok din nan da ya yi kaurin suna wajen tare titi yana wanka a Kano gidan kurkuku. Kotun dai ta sami matashin mai suna Umar Hisham Fagge, wanda aka fi sani da Tsulange, zuwa gidan yari har zuwa ranar 3 ga watan Yulin 2025. 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’ NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya Kotu, wacce ke karkashin Mai Shari’a Hadiza Muhammad Hassan, ta yanke hukuncin ne ranar Alhamis. Hukumar Tace Fina-finai ta jihar Kano ce dai ta gurfanar da Tsulange a gaban kotun biyo bayan kama shi...
    “Za a sauƙaƙe hakan ne ta hanyar Bankin Raya kasa na KfW da Asusun Kalubalan Kasuwancin Afirka.”   An gudanar da bikin sanya hannun ne a ofishin ministan kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Abubakar Bagudu, wanda ya wakilci Nijeriya.   Sakatare na farko kuma shugaban hadin gwiwar raya kasa a ofishin jakadancin Jamus a Nijeriya, Dr Karin Jansen, da wakilin bankin raya kasa na KfW, Gerald Keuhnemund, duk sun halarci rattaba hannun. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Dangane da sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta bayar na cewa za ta maido da yin tambayoyi ga dalibai kafin a ba su biza kuwa, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin ta lura da batun, kuma tana fatan Amurka za ta aiwatar da kalaman shugaba Trump na maraba da daliban kasar Sin da su zo Amurka don yin karatu. Dangane da wani rahoto da wata cibiyar bincike ta kasar Switzerland ta fitar, inda ta bayyana cewa, matsayin karfin yin takara na yankin Hong Kong na Sin ya karu zuwa matsayi na uku a duk fadin duniya, Guo Jiakun ya bayyana cewa, wannan na nuni da matsayin Hong Kong na musamman da kuma alfanun da ake da shi, da kuma...
    A shekaru biyu da suka wuce, shugaban kasar Sin da takwarorinsa na kasashen nan biyar sun dasa wasu bishiyoyin ruman guda shida a birnin Xi’an, wadanda yanzu haka cike suke da furanni tare da alamanta hadin gwiwar kasashen mai cike da kyawawan nasarori, wadanda kuma suka shaida cewa, “hannu daya ba ya daukar jinka”, hada karfi da karfe ne zai kai ga inda aka dosa, kuma ba wanda ke iya cin nasara daga faduwar wasu, kuma za a iya tabbatar da nasara ga juna ne kurum idan aka zama tsintsiya madaurinki guda. Yanzu haka, duniyarmu na fama da rikice-rikice da kariyar ciniki da ra’ayi na kashin kai da kuma siyasar nuna fin karfi. Amma bai kamata a mai da hannun...
    Wata kotu a kasar Amurka ta yanke wa wasu ’yan Najeriya su biyar hukuncin daurin shekaru 159 bisa samun su da da laifin damfarar Amurkawa sama da 100. Kotun dai ta sami mutanen ne da laifin damfarar kamfanoni da hukumomin gwamnatin kasar kudin da yawansu ya kai Dala miliyan 17, kwatwankwacin Naira biliyan 27 da miliyan 200. Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sashen shari’a na kasar ya wallafa a shafinsa na intanet ranar Laraba, mai dauke da sa hannun mai rikon mukamin Babban Lauyan gwamnati na gundumar gabashin Texas, Ray Combs. ’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara Sanarwar ta ce mutanen da aka yanke...
    A watan Afrilun bana, wata farar mota kirar bas mai tsawo mita 12, ta yi tafiya a kan titunan Ashgabat, hedkwatar kasar Turkmenistan. Bas din da kamfanin Yutong na kasar Sin ya kera ta dace da ma’aunin kiyaye muhalli da kasar ta tanada, kuma tana dauke da na’urar ba da jagorancin sufuri mai amfani da tauraron dan Adam, da na’urar biyan kudi ta yanar gizo, matakin da ya bullo da sabuwar hanyar zirga-zirga ga jama’ar wurin. A wannan shekara, Sin za ta samar da irin wannan bas har 700 ga Ashgabat, matakin da zai biya bukatun zirga-zirgar jama’ar kasar da yawansu ya zarce miliyan 1. Tun da aka bude taron koli na Sin da kasashen shiyyar tsakiyar Asiya karon farko...
    An cimma jerin yarjejeniyoyin hadin gwiwa a taron koli na biyu na kasar Sin da tsakiyar Asiya da aka gudanar a birnin Astana na kasar Kazakhstan a ranar 17 ga watan nan agogon kasar. Shugabannin kasashen biyar na tsakiyar Asiya sun yaba wa kasar Sin a matsayin babbar abokiyar hadin gwiwa kuma kawa ta gaskiya da kasashen yankin tsakiyar Asiya za su iya amincewa da ita har abada. Ana iya sa ran cewa, hadin gwiwar da Sin za ta yi da tsakiyar Asiya ba wai kawai za ta inganta manyan ayyukan hadin gwiwa ba ne, har ma za ta kara karfafa kokarin “neman sabbin abubuwa masu dadi” da “sabbin kirkire-kirkire”, da sa kaimi ga kasashen shida wajen cimma zamanantarwa tare...
    An gayyaci shugaban kasar Sin Xi Jinping zuwa kasar Kazakhstan, daga ranar 16 zuwa 18 ga watan Yunin shekarar 2025, don halartar taron koli karo na biyu na Sin da tsakiyar Asiya. A karshen ziyarar, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi wa manema labarai karin haske game da lamarin. Wang Yi ya ce, babban abin da ya fi daukar hankali a wannan taro shi ne sanarwar da shugaba Xi Jinping ya yi ta “Ruhin Sin da Tsakiyar Asiya”. Inda shugabannin kasashen yankin tsakiyar Asiya suka amince baki daya kan kiyaye wannan ruhi, da inganta tsarin kasar Sin da tsakiyar Asiya don samun sabon babban ci gaba. Bugu da kari, dangane da halin da ake ciki a yankin...
    Shugaba Bola Tinubu ya kai ziyara asibiti da ke Makurdi, Babban Birnin Jihar Benuwe, domin duba waɗanda da suka jikkata a hare-haren da ‘yan bindiga suka jihar. Shugaban ya je ne domin ganin irin ɓarnar da aka yi, tare da nuna alhini da goyonnsa baya ga al’ummar jihar. Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti  Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato Hotunan ziyayar sun nuna Tinubu yana duba da waɗanda abin ya shafa. Go hotunan a ƙasa:
    Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya kai ziyara Jihar Benuwe domin jajanta wa mutanen jihar bisa hare-haren da suka faru a wasu ƙauyuka kwanan nan. Ya je ne domin nuna alhininsa ga waɗanda abin ya shafa da kuma tattaunawa da shugabanni don nemo mafita mai ɗorewa. Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi A yayin ziyarar tasa ta yini guda, Shugaba Tinubu ya fara ne da ziyartar Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Benuwe, inda ta duba waɗanda suka jikkata. Shugaban ya shirya ganawa da iyalan waɗanda aka kashe, da waɗanda suka rasa muhallansu, da kuma shugabannin al’umma. Hakazalika, Shugaba Tinubu zai gana da manyan masu ruwa da tsaki s jihar,...
    Kungiyoyin ma’aikata na Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna da ke Gidan Waya, Kafanchan sun bayyana aniyarsu na fara yajin aikin gargadi na kwanaki uku. Sun ce za su shiga yajin aikin ne daga ranar Alhamis, 19 ga watan Yuni, 2025. Wannan matakin ya biyo bayan karewar wa’adin kwanaki 14 da suka yi bai wa gwamnatin jihar, wanda zai kare ranar Laraba, 18 ga watan Yuni. Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu Ambaliyar Mokwa: Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja Aminiya ta rawaito cewa kungiyoyin da suka hada da na Kungiyar Malaman Kwalejojin Ilimi (COEASU), SSUCOEN da Kungiyar Manyan Ma’aikatan Kwalejojin Ilimi ta Najeriya (SSUCOEN) da Kungiyar Ma’aikatan da ba na...
    Gwamnatin jihar Neja ta ce har yanzu akwai sama da mutum 700 da suka bace ba gan su ba tun bayan mummunar ambaliyar ruwan da aka yi a karamar hukumar Mokwa da ke jihar. Gwamnan jihar, Mohammed Umar Bago ne ya bayyana hakan lokacin da ya karbi babban dogarin tsohon Shugaban Kasa marigayi Janar Sani Abacha, Manjo Hamza Al-Mustapha yayin ziyarar jaje kan ambaliyar a Minna ranar Talata. Gwamnan, wanda mataimakinsa, Yakubu Garba ya wakilta ya kuma ce akalla mutum 207 ne aka tabbatar da mutuwarsu sannan gidaje sama da 3,000 ne suka rushe. DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro? Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom “Sama da...
    A yau, shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugabannin kasashe biyar na tsakiyar Asiya sun halarci bikin rattaba hannu tare da sanya hannu kan yarjejeniyar Astana ta taron kolin kasar Sin da yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, da kuma yarjejeniyar kyakkyawar makwabtaka da abota da kuma hadin gwiwa na dindindin. Har ila yau, sun kuma halarci bikin kaddamar da cibiyar hadin gwiwa da dandalin tattaunawa na tsakiyar Asiya da kasar Sin. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Kasar Sin ta cimma nasarar aikin gwajin tserewa lokacin da ake gamu da matsala a matakin farko na harbar kumbo mai dauke da mutane na “Mengzhou” a yau Talata, a cibiyar harbar taurori dan Adam dake birnin Jiuqiu, abin da ya alamanta cewa, Sin ta cimma sabuwar nasara a aikin binciken duniyar wata tare da kumbo mai daukar mutane. Wannan ita ce nasara irinta ta biyu da Sin ta samu a wannan bangare, bayan shekaru 27 da suka gabata, da samun nasara ta farko a aikin gwajin da ta gudanar a shekarar 1998. Aikin gwajin tserewar da aka gudanar ya kasance muhimmin mataki na ba da tabbaci ga rayukan ’yan saman jannati, wato idan an gamu da hadari ko matsala...
      Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    A yau Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da muhimmin jawabi a taron koli na kasar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu. A cikin jawabinsa, Xi ya ce, yayin da kasar Sin da kasashe biyar na yankin tsakiyar Asiya ke tafiya kan hanyar samun ci gaba a cikin dogon lokaci, sun kafa “Ruhin Sin da kasashen tsakiyar Asiya” na “Mutunta juna, da amincewa da juna, da moriyar juna, da taimakon juna, da inganta zamanantarwa tare ta hanyar samun ci gaba mai inganci”. Yayin da ya ambaci yanayin rashin kwanciyar hankali da duniya ke fama da shi, ya ce ta hanyar tabbatar da adalci ne za a iya cimma burin kare zaman lafiya, da samun ci...
    A yau Litinin, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da takwaransa na kasar Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev gabanin taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na biyu. Kazalika, daga bisani duk dai a yau shugabannin biyu za su halarci bikin musayar rubutaccen daftarin hadin gwiwa tsakanin Sin da Kazakhstan. Xi ya isa Astana, babban birnin Kazakhstan yau Litinin, domin halartar taron koli karo na biyu tsakanin kasar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na...
      Dan wasan mai shekaru 27 ya zura kwallaye 20 sannan ya taimaka wajen zura bakwai daga wasanni 40 da ya buga a duk wasannin da ya buga a kakar wasan data gabata, Lookman ya ci kwallaye 17 kuma ya taimaka wajen zura 10 a kakar wasanni ta shekarar 2023/24. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Iran ta zartar da hukuncin kisa kan jami’an leken asirin Hukumar leken asirin yahudawan sahayoniyya “Mossad” a safiyar yau Litinin A wani gagarumin farmaki da aka kai kan cibiyar leken asirin yahudawan sahayoniyya a cikin kasar Iran, an kama wani mutum tare da yi masa shari’a bisa zargin hadin kai da hukumar leken asirin ‘yan sahayoniyya, bisa tuhumarsa a matsayin maci amana da gudanar da barna a kan doron kasa. An zartar da hukuncin ne bayan kammala shari’ar laifuka da kuma tabbatar da hukuncin da kotun koli ta yanke. A cikin wani hadadden aikin fasaha da leken asiri a cikin kasar, an kama Isma’il Fakri a watan Disamban shekara ta 2023 yayin da yake da alaka da hukumar leken asiri...
    Gwamnatin Amurka ta rufe Ofishin Jakadancinta da ke haramtacciyar kasar Isra’ila Jakadan Amurka a haramtacciyar kasar Isra’ila Mike Huckabee ya sanar a yau Litinin cewa: Wani makami mai linzami na Iran ya fado kusa da ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Tel Aviv, wanda ya yi barna kadan amma ba a samu rauni a tsakanin ma’aikatan ba. A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce: Daga yau Litinin ofishin jakadancin da sauran ofisoshin Amurka da suke haramtacciyar kasar Isra’ila za su ci gaba da kasancewa a rufe a matsayin matakin riga-kafi. Jakadan ya kara da cewa: Babban abin da ya sa a gaba shi ne kare lafiyar jami’an diflomasiyyar kasarsa, kuma za su ci gaba da sanya ido kan...
    Wani jami’in ɗan sanda, SP Mustapha Garba Gumau, ya yi gamo ajalinsa a wani hatsarin mota yayin da ya rage aƙalla sa’a ɗaya a ɗaura masa aure. Aminiya ta ruwaito cewa, ajali ya katse hanzarin jami’in ne a kan hanyar Gumau zuwa Magaman-Gumau da ke Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi, inda za a ɗaura masa aure. Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina SP Gumau wanda hatsarin ya rutsa da shi da abokansa ya rasu ne da misalin ƙarfe 9 yayin da ake shirin ɗaura masa aure da misalin ƙarfe 10 na safiyar ranar Asabar. Wata sanarwa da mai magana da yawun...
    Martanin Iran game da ta’addancin haramtacciyar kasar Isra’ila na ci gaba a rana ta biyu Ana ci gaba da mayar da martani mai girma na Iran game da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila take kaiwa da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki. ‘Yan mintoci da suka gabata a zaman wani bangare na biyu na “Alkawarin Gaskiya Na 3”, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta harba daruruwan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka kan haramtacciyar kasar Isra’ila. An harba wadannan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki da kuma jiragen sama masu saukar ungulu daga Tehran da sauran garuruwan kasar Iran a matsayin wani mataki na murkushe laifuffukan da yahudawan sahayoniyya suka aikata a kan...
    Kungiyar ‘Abokan Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya’ ta yi Allah wadai da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan Iran Kasashe mambobin kungiyar aminan yarjejeniyoyin Majalisar Dinkin Duniya sun fitar da wata sanarwa ta musamman inda suka yi kakkausar suka kan wuce gona da irin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Sanarwar ta yi la’akari da harin hadin gwiwa ta sama da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar a ranar 13 ga watan Yuni a kan wasu wurare da dama a Iran, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkata wasu daruruwa da suka hada da mata da kananan yara da masana kimiyya, matakin da ya saba wa Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Yayin da taro na biyu na tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya ke kara matsowa, sakamakon kuri’un jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, sun nuna gamsuwa da hadin gwiwa bisa matsayin koli dake tsakanin Sin da kasashen nan biyar na yankin tsakiyar Asiya, a matsayin wata hadaka ta al’umma mai kyakkyawar makomar bil’Adama, wadda ke kara shigar da sabon kuzari, na daidaito cikin yanayin duniya dake kara shiga yanayin tangal-tangal. Tun dai taro na farko na tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya, hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen biyar ya shiga wani sabon zango na ci gaba. Har ma kuri’un na jin ra’ayin jama’a suka nuna yadda kaso 90.4...
    Ba tare da saninmu ba, yawancin al’ummar Afirka musamman ma naYammacin Afirka suna fama da abinda ake kira da suna irin hali ko yanayin da aka shiga sanadiyar lamarin cinikin Bayi.Bayan shekara 100 da aka yi daga shekarar 1801 zuwa 1901, an yi wani kokarin da ake yi ma kallon tamkar wani takune na yadda za’a kubuta daga irin cin fuskar da ake yi kowace rana. Kafin dai a tsunduma sosai cikin lamarin cinikin Bayi, yana da matukar kyau a fara yin bayani kan yadda abin ya fara:Lamarin cinikin Bayi ba manufa bace ta Yammacin Turai.Duk lamarin ya zarce wani hasashen da za’a iya yi ko wani rubutun,da aka yi aka aje.Idan kuma aka duba ta bangaren nahiyar Afirka ita...
    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya yi karin haske game da taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, wanda shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarta a Kazakhstan, yana mai cewa, Sin na da yakininta hanyar taro, ita da sauran kasashen yankin tsakiyar Asiya biyar, za su zurfafa dunkulewa, da amincewa da juna, da gina matsaya guda ta fuskar hadin gwiwa, da zurfafa daidaiton dabarun ci gaba, da daga matsayin hadin gwiwarsu a fannoni daban daban, da kara kuzarin gina al’umma mai makomar bai daya ta Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya.   Bisa gayyatar da shugaban jamhuriyar Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev ya yi masa, shugaba Xi Jinping zai halarci taron koli na...
    Babu abin da ya rage yanzu, illa babatun zantukan siyasa da ‘yan siyasar ke ta fama yi a kasar, wadanda suka jarabtu da matukar son mulki. Wannan abu da ke faruwa yanzu, ko shakka babu zai canja, zai canja din ne kuwa yayin da ‘yan siyasar ke aiwatar da tsare-tsarensu, sai masu jefa kuri’u a Nijeriya kuma su yanke hukunci. Shekarar 2027, za ta kasance mai ban mamaki tare da kalubale ga ‘yan Nijeriya. A bisa dukkan alamu, jam’iyyar APC ta dukufa wajen kara habaka karfinta ne kawai da ganimar ‘yan adawa. Tana ta faman sa kanta cikin rigingimu, har wadanda ba su shafe ta ba a cikin shekaru biyun da ya rage mata ta yi gaba na kunci da...
    Da yake magana kan muhimmancin bikin Ranar Dimokiraɗiyya ta bana, Idris ya ce wannan ba lokacin murna kaɗai ba ne, har ma lokaci ne na nazari kan cigaban ƙasar wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya da farfaɗowar tattalin arziki.   Ya bayyana cewa ana amfani da kuɗaɗen da aka tara daga cire tallafin man fetur wajen gina muhimman ababen more rayuwa, ciki har da manyan tituna guda biyu da za su haura kilomita 1,700, waɗanda za su taimaka wajen bunƙasa harkokin kasuwanci da haɗa yankuna daban-daban.   Ya ce: “Manufar ba wai haɗa yankuna ba ce kawai, amma samar da damarmakin tattalin arziki.   “Nijeriya na ƙoƙarin komawa kan sahihiyar hanyar ta. Tana sake zama ƙasa mai daraja a idon duniya.   “Martabar...
    A sandiyyar harin da ‘yan sahayoniya su ka kawo wa Iran da asubahin yau, masana fasaahr Nukiliya da dama sun yi shahada. Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya ambaci cewa: Daga cikin wadanda su ka yi shahadar da akwai tsohon shugaban hukumar makamashin Nukiliya ta Iran; Faridun Abbasi. Shugaban jami’ar Azad, Muhammad Mahdi Dahranji. Shugaban Kwalejin fasahar Nukiliya, Abdulhamid Minochehri. Hakan nan kuma Malamin fasahar Nukiliya Ahmda Riza Zulfiqar, sai mataimakin shugaban hukumar  makamashin Nukiliya Amir Husain Fiqhi.
    Kwamandan  sararin samaniya na dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Janar Amir Ali Haji Zadeh yana cikin wadanda su ka yi shahada sanadiyyar harin da sojojin HKI su ka kawo wa  da asubahin yau Juma’a. Kamfanin dillancin labarun “Mehr” ya nakalto majiyar juyin juya halin musulunci ta Iran tana tabbatar da shahadar Janar  Amir Ali Haji Zadeh.
    Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta Lebanon Sheikh Na’im Kassim ya yi Allawadai da harin da HKI ta kai wa Iran, wanda ya bayyana shi da cewa; Yana da hatsarin gaske, kuma ‘yan sahayoniyar sun yi hakan ne bisa cikakken goyon bayan Amurka. Sheikh Na’im Kassim ya kuma bayyana cewa; Harin na ‘yan sahayoniya ba shi da wani dalili da ya wuce a rufe bakin gaskiya wanda yake taimakawa al’ummar Falasdinu a Gaza da ake yi wa kisan kiyashi, haka nan kuma taimakawa da goyon bayan gwgawarmayar Lebanon da dukkanin wannan yankin. Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma kara da cewa; Wannan harin da wuce gona da irin za iyi tasiri mai girma a cikin wannan yankin, sannan ya kara...
    Sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Birgadiya Muhammad Pakphur ya aike wa da jagoran juyin musulunci na Iran wasika da a ciki ya bayyana cewa: ” Laifukan ta’addanci da HKI ta aikata, wanda ya yi sanadiyyar shahadar manyan kwamandojin  da kuma  malaman Nukiliya, haka nan  mata da kananan yara da ba su ji ba su gani ba, ba zai wuce ba tare da mayar da martani ba.” Bugu da kari sabon kwamandan dakarun kare juyin musuluncin ya ce; Ba da jimawa ba, Za a buwa wa wannan haramtacciyar kasa kofofin jahannama.” Birgeriya Muhamad Pakphur ya kuma kaddamar da ta’aziyya da kuma taya murnar shahadar kwamandojin, ya kuma yi godiya ga jagora da ya gaskata dakarun juyin....
    Rundunar ’yan sandan ƙasar Australia ta kama wata ’yar asalin Najeriya da ke ƙasar Australia, Binta Abubakar bisa zarginta da safarar ɗalibai daga ƙasar Papua New Guinea tare da tilasta musu yin aikin da ba a biya a gonaki a faɗin jihar Ƙueensland da sunan bayar da tallafin karatu. Binta mai shekara 56, an kama ta ne a ranar Laraba a filin jirgin saman Brisbane a lokacin da ta isa ƙasar Papua New Guinea, inda take zaune. Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8 Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi Kamen nata ya biyo bayan wani bincike na tsawon shekaru biyu da ƙungiyar masu fataucin bil-Adama ta AFP ta...
    Gabanin tafiyar shugaban kasar Sin Xi Jinping birnin Astana na kasar Kazakhstan, inda zai halarci taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, an kaddamar da bikin gabatar da jerin shirye-shiryen shirye-shiryen telebijin da fina-finai, na babban gidan rediyo da telebijin na kasar Sin wato CMG na shekarar 2025 a birnin Astana. Za a gabatar da shirye-shiryen CMG guda 12, ciki har da alakar dake tsakanin shugaba Xi Jinping da al’adun kasar Sin, da hanyar zamanintar da kasa mai salon kasar Sin na musamman da sauransu, a manyan kafofin watsa labaru na kasashen Kazakhstan, da Kyrgyzstan, da Tajikistan, da Turkmenistan, da Uzbekistan da dai sauransu. Shugaban gidan CMG Shen Haixiong ya bayyana cewa, a ta bakin...
    Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai matsayin cin ribar cikakkiyar dimokuraɗiyya ba, duk da cewa an dawo mulkin farar hula shekaru 26 da suka gabata. Yayin wata tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya, Fayemi ya bayyana cewa duk da cewa ana gudanar da zaɓe a kai a kai a ƙasar, har yanzu an rasa muhimman abubuwan da suka kamata su kasance a tsarin dimokuraɗiyya na gaskiya. Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna “Bai kamata mu rikita gudanar da zaɓe da aiwatar da dimokuraɗiyya ba,” in ji shi. “Abin da muka...
    Bayan harin da gwamnatin Sahayoniya ta kai kasarmu, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya aike da sako ga al’ummar Iran. Ga sakon kamar haka Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai Al’ummar Iran masu daraja! Gwamnatin yahudawan sahyoniya ta hanyar aikata wani laifi da sanyin safiyar yau, ta sake bayyana munanan dabi’arta da fasadi. Ta hanyar kai hari dole ne wannan ya fuskanci hukunci mai tsanani. A wannan harin makiya, kwamandoji da masana kimiyya da dama sun yi shahada. Wadanda suka gaje su kuma da abokan aikinsu za su ci gaba da aiki nan take akan wannan tafarki, godiya ta tabbata ga Allah. Ta hanyar wannan danyen aiki, gwamnatin Sahayoniya ta kaddara akan ta cewa...
    Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta ce mayar da martani ga gwamnatin Isra’ila hakki ne na shari’a ga Iran kamar yadda doka ta 51 ta kundin tsarin mulkin MDD ta tanada. Da farko dai ma’aikatar ta mika ta’aziyyar shahadar wasu kwamandoji da jami’an kasar Iran a harin da Isra’ila ta kai wa kasar. “Hare-haren da gwamnatin sahyoniyawan ta kai wa Iran sun sabawa doka ta 4 sakin layi na 2 na kundin tsarin mulkin majalisar dinkin duniya a matsayin wani mataki na wuce gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma Iran tana da hakki na shari’a na halal ta mayar da martani kan wannan zalunci kamar yadda yake a cikin sashe na 51 na kundin tsarin mulkin majalisar...
    Kungiyar kwallon kafa ta Galatasaray a wannan Alhamis din ta sanar da daukar dan wasan Jamus, Leroy Sane daga Bayern Munich. Kungiyar ta Turkiyya ta dauki dan wasan ne kyauta bayan kwantaraginsa ya kare a Munich. Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane Sane mai shekaru 29 ya rattaba hannu kan kwantaragin shekaru uku inda zai rika daukar albashin Yuro miliyan 9 — kwantankwacin Dala miliyan 10.4 — duk shekara kamar yadda kulob din bayyana. Sane ya buga wa kasarsa ta Jamus wasanni 70, inda kuma ya lashe kofunan Bundesliga guda hudu a Bayern Munich tun bayan raba gari da Manchester...
    Majiyar tsaron kasar ta Kamaru sanar da cewa, da dama daga cikin sojojin kasar sun rasa rayukansu sanadiyyar wani hari da kungiyar Bokoharam ta kai musu ta hanyar amfani da manyan bindigogi da kuma jirgin sama maras matuki akan iyaka da Najeriya. Majiyar ta ce an kai harin ne a yankin Sagami dake kusa da tafkin Chadi a gundumar Logun mai iyaka da kasar Najeriya. Ita dai kungiyar Bokoharam ta addabi kasashen Najeriya, Kamaru da kuma jamhuriyar Nijar. Yankun arewacin kasar ta Kamaru ya fara fuskantar kai hare-hare daga wannan kungiyar ne tun a 2014 wanda kuma har yanzu yana ci gaba da faruwa daga lokaci zuwa lokaci.
    Jami’in tafiyar da sha’anin Mulki a yankin Cape ya fada a jiya Laraba  cewa; An sami karuwar wadanda su ka rasa rayukansu ya karu zuwa 49. Shugaban tafiyar da sha’anin Mulki a yankin na garin Cape, Oscar Mobyan  ya bayyana haka ne a wani taron manema labaru,kamar yadda kamfanin dillancin labarun Reuters ya nakalto. Wasu yankuna na kasar ta Afirka Ta Kudu sun fuskanci saukar ruwa kamar da bakin kwarya, haka nan kuma saukar kankara, da hakan ya sa aka shiga cikin yanayin sanyi mai tsanani da kuma yankewar wutar lantarki a wasu yankunan. Ambaliyar ruwan da aka samu a kusa da wata makaranta ya ja motar da take dauke da dalibai 13, da hakan ya yi sanadiyyar rasuwarsu. Tuni...
    Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Inganta sinadarin Uranium da ɗage takunkumai na iya sa tattaunawar ta yi amfani Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya rubuta cewa: A bayyane yake cewa cimma yarjejeniyar da za ta tabbatar da zaman lafiya na dindindin na shirin makamashin nukiliyar Iran abu ne mai yiyuwa, kuma ana iya cimma shi cikin sauri. Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya rubuta a shafinsa na Twitter game da sabon zagayen tattaunawa tsakanin Iran da Amurka da kuma matsayin Iran a kansu yana mai cewa: Shugaba Trump ya bayyana a lokacin da ya shiga fadar White House cewa ba lallai ne Iran ta mallaki makamin nukiliya ba, wannan matsayi ya yi daidai da akidar Iran...
    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Sake kunna ‘hanyar tayar da hankali’ zai gamu da martani mai ƙarfi na Iran Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya jaddada cewa: Fitar da kudiri kan Iran da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta yi ba zai shafi kudurin al’ummar Iran ba ko kuma ci gaban shirinta na makamashin nukiliya na zaman lafiya. A wata hira da ya yi da gidan talabijin na Iran a yammacin ranar Talata, Baqa’i ya yi la’akari da dukkanin rahotanni da kudurorin da suka shafi siyasa. Ya kuma kara da cewa Iran ba ta keta hurumin da ya rataya a wuyanta ba, kuma kasashen yammacin turai suna dora barazanarsu ne kan...
    Mataimakin firaministan Sin He Lifeng, ya bukaci Amurka da ta warware takaddamar cinikayya da Sin ta hanyar tattaunawa, da hadin gwiwa da zai iya haifar da moriyar bai daya. He, ya ce Sin na jaddada burin ganin Amurka ta yi aiki da bangaren Sin, ta yadda za a martaba alkawura da matakai da aka amince, da nuna sahihanci wajen yin aiki tukuru, da aiwatar da gaskiya da kwazo wajen aiwatar da matsayar da aka cimma, ta yadda za a kai ga kare nasarorin da aka cimma ta hanyar shawarwari. He, ya yi tsokacin ne yayin taron farko na shawarwari game da harkokin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, wanda ya gudana a ranakun Litinin da Talata a birnin...
    Ana zargin wata mata mai suna Khadija kan zargin kashe ’yarta mai shekaru 11, Fadila, saboda Naira 100 da ta samu a yawon Sallah a unguwar Tukur Tukur da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna. Lamarin ya faru ne a ranar Asabar kafin sallar Magariba, inda lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce a unguwar har maƙwabta suka ƙi yi wa gawar yarinyar sallah saboda tsoron abin da zai biyo baya. Ranar Dimokuraɗiyya: Tinubu zai yi wa ’yan Najeriya jawabi Majalisar Dokokin Kuros Riba ta dakatar da shugabar ƙaramar hukuma na wata 3 Wasu maƙwabta sun bayyana cewa Khadija ta doke Fadila da taɓarya ne saboda ta zargi yarinyar da satar Naira 100. Sun ce irin wannan ɗabi’a na duka da tsangwama...
    Cherki ya buga wasansa na farko a Lyon yana da shekara 16 a watan Oktoban 2019 kuma ya bar kungiyar inda ya ci kwallaye 29 sannan ya taimaka aka jefa 45 a wasanni 185 da ya bugawa kungiyar ta Faransa. Cherki ya wakilci kasar Faransa kuma ya lashe lambar azurfa a gasar Olympics da aka gudanar a birnin Paris na kasar Faransa a bara.   Daraktan kwallon kafa na Manchester City, Hugo Viana ya ce, “Babu shakka a yanzu Cherki yazo inda ya dace kuma zai cigaba a karkashin jagorancin Guardiola, kuma na yi imani zai iya zama babban dan wasa a duniya tare da goyon bayan abokan wasa da masu horarwa”. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya...
      Gwamnan ya jajanta wa gwamnati da al’ummar Neja kan mummunar barnar da ambaliyar ruwan ta yi, na salwantar da rayuka da barnata dukiya da dama.   Gwamna Umar Bago na jihar Neja, ya yabawa takwaransa na Borno bisa wannan ziyarar da kuma bayar da gudunmawar, inda ya ce lokaci ya yi da za a nuna soyayya ga juna. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Iran ta bayyana cewa: Tace sinadarin Uranium wani bangare ne na bunkasa masana’antar nukiliya kuma ba zata amince kan tattaunawa ko yin sulhu kansa ba Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana cewa: Sarrafa sinadarin Uranium wani bangare ne na masana’antar nukiliya, kuma batu ne da ba za a tattaunawa kansa ko yin sulhu kansa ba, kasancewarsa masana’antar cikin gida ne kuma an shefe tsawon shekaru da dama ana sarrafa shi a cikin kasa, sakamakon kokarin da masana kimiyya suka yi. babu wata kasa da ke da ikon bayyana ra’ayi kan wannan hakkin. A cikin taron manema labarai na mako-mako, Baqa’i ya yi ishara da abubuwan da ke faruwa a duniya a halin yanzu, yana mai jaddada...
    Jami’in makamashin nukiliyar Iran ya jaddada cewa: Zarge-zargen da ake yi wa Iran kan shirinta na makamashin nukiliya, siyasa ne tsantsa Kakakin Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran Behrouz Kamalvandi, ya ce: Zargin da ake yi wa Iran game da batun Shirin makamashin nukiliya na zaman lafiya, tsagwaron siyasa ne, ba bisa ka’ida ko na fasaha ba. Kakakin Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran ya kara da cewa: Kudurorin da suka biyo baya da kuma kara matsin lamba a kan Iran suna share fagen fuskantar al’amura a nan gaba. Yayin da yake ishara da cikas iri-iri da ke kawo sarkakiya ga ci gaban shirin makamashin nukiliyar Iran, Behrouz Kamalvandi ya bayyana cewa: Wadannan kalubalen da suka kara ta’azzara a cikin ‘yan shekarun...
    Babban darektan hukumar IAEA ya zama tamkar wata yar tsana ce a hannun kasashen Yamma don dakile shirin nukiliyar Iran An fara taron kwata-kwata na hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa a birnin Vienna, wanda ya samu halartar wakilan kasashe 35 mambobi hukumar Bisa la’akari da rahoton da babban daraktan ya fitar game da sa ido da tabbatar da shirin nukiliyar Iran karkashin yarjejeniyar kare kai da kuma tsarin aiwatar da ayyukan hadin gwiwa ta (JCPOA) na daya daga cikin batutuwan da za a tattauna. Babban darektan hukumar ta IAEA Rafa’el Grossi ya sanar a wani rahoto da ya fitar a makon da ya gabata cewa; Yawan sinadarin uranium da Iran ke da shi ya ninka har...
    Al’ummu daga dukkan sassan duniya suna mayar da martaninsu cikin fushi bayan sace jirgin ruwa Madeleine mai dauke kayayyakin jin kai zuwa Gaza Kwamandojin sojojin mamayar Isra’ila sun yi garkuwa da jirgin ruwan farare hula Madeleine, wanda ke yunkurin karya killace yankin Zirin Gaza da aka yi a kokarinsu na shigar da kayan agaji ga al’ummar yankin da suka rage. Sojojin mamaya sun garkuwa da masu fafutuka tare da kai su tashar ruwan Ashdod. Majalisar Dinkin Duniya da hukumomin yankin sun yi tir da laifin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta aikata. Kungiyar Hamas ta bayyana shi a matsayin ta’addancin kasa da kasa. A wani sabon laifin da ya saba wa dukkanin ka’idojin kasa da kasa da na jin kai, sojojin...
    Gwamnatin Sudan ta zargi ‘yan tawayen kasar na dakarun kai daukin gaggawa da kai hari kan ayarin motocin agaji kai a yankin Darfur Gwamnatin Sudan ta sanar da cewa: “Dakarun kai daukin gaggawa sun kai hari kan ayarin motocin agajin jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a yankin Darfur ta Arewa ta hanyar jiragen sama marasa matuka ciki.” A cikin wata sanarwa da ta fitar, gwamnatin Sudan ta bayyana matukar bacin ranta tare da tofin Allah tsine da Allah wadai kan wannan mummunan lamari, tana mai jaddada cewa: “Yunkuri ne na ganganci na nufin toshe kungiyoyin agaji da dakile ayyukansu na kai kayan agaji ga fararen hula da suka makale a birnin El Fasher da sansanonin gudun hijira.” Sanarwar ta...
    “Mun bi tsarin mulki kuma mun ƙi rashin adalci. Da PDP ta yi haka, ba za ta fuskanci wannan matsala ba.” Taron ya haɗa da tsoffin gwamnonin jihohi Samuel Ortom (Benue) da Okezie Ikpeazu (Abia), da sauran shugabannin jam’iyyar. Wike ya soki shugabannin PDP saboda sanya son rai fiye da haɗin kan jam’iyyar. Ya ce jam’iyyar sai ta koma tubalinta na asali don samun ci gaba. “Wasu shugabanni suna karkatar da dokoki don amfanin kansu,” in ji Wike, yana ambaton yadda gwamnan Taraba ya tsaya takarar gwamna ba tare da ya yi murabus a matsayinsa na shugaban jam’iyyar ba. “Dole ne a daina wannan.” Tsohon Gwamna Ortom ya yarda da maganar Wike, ya amince cewa PDP ta yi manyan kurakurai....
    Ma’aikatar kiwon lafiya na kasar Iran ta bayyana cewa kasar a halin ayanzu tana daga cikin kasashe uku na gaba a kan abinda ya shafi samun isasshen abinci mai lafiya da kuma wadatacce a cikin kasar. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan kiwon lafiya Muhammad Reza Zafarkandi yana fadar haka a jiya litinin a taron raya ranar abinci da duniya wanda aka gudanar a dakin taro na hukumar gidajen radio da talabijin a nan birnin Tehran. Ministan ya kara da cewa, samun abinci mai gina jiki da kuma bada sinadaran da jiki yake bukata yana daga cikin abubuwan da suke bada lafiya ga jiki. Har’ila yau wannan yana kwantar da hankalin mutanen ko wace kasa wacce...
    Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewacin Nijeriya ACF ta bukaci Shugaba Bola Tinubu da manyan muƙarraban gwamnatinsa da su daina gaggawar shige-da-fice wajen neman tazarce a Zaɓen 2027. ACF ta ce zai fi dacewa gwamnatin Tiinubun ta mayar da hankali wajen ganin ta kyautata rayuwar ’yan Nijeriya maimakon gangamin yaƙin neman a sake zaɓensa a 2027, lamarin da ƙungiyar cewa hakan ya yi wuri. NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Fara Sana’a Ba Tare Da Jari Ba Ɓarawon waya ya kashe babban jami’in soja da wuƙa a Kaduna Wannan kira dai na kunshe cikin wata sanarwar yi wa musulmi barka da Sallah Babba da kakakin ƙungiyar na ƙasa, Farfesa Tukur Muhammad-Baba ya fitar. Ƙungiyar ta bayyana rashin jin daɗinta dangane da taɓarɓarewar tsaro da...
    Tare da cewa giwaye suna cikin dabbobin da masu yawon bude ido suke son gani, said ai gwamantin kasar Zimbabwe ta yanke hukunci yanka 50 daga cikinsu domin rabawa mutanen karkara namansu. Wannan matakin na gwamnatin Zimbabwe ya zo ne saboda yadda giwayen suke kara yawa sosai a cikin shekarun bayannan. Haka nan kuma wuraren da ake killace su, sun yi kadan. Majiyar dake kula da gandun dajin kasar ta ce; adadin giwayen ya rubanya har sau uku, wannan ne ya sa mahukuntar kasar su ka yanke shawarar yanka 50 daga cikinsu saboda a rabawa mutanen karkara. A baya gwamnatin na Zimbabwe ya yi kokarin warware matsalar karuwar dabbobin ta hanyar sauya musu gandun daji da wuraren da aka killace...
    A daidai lokacin da kungiyar kasashen  tsakiyar Afirka ta tattalin arziki        ( ECCAS) take yin taro, kasar Rwanda ta sanar da ficewa daga cikinta. Bayanin da gwamnatin kasar ta Rwanda ta fitar ya kunshi cewa; Kasar Rwanda tana nuna takaicinta akan yadda kasar DRC take amfani da kungiyar tattalin arziki ta  tsakiyar Afirka a matsayin wani makamin a hannunta.” Bayanin gwamnatin ta Rwanda ya kara da cewa: Yadda DRC take amfani da wannan kungiyar ya sake fitowa fili a yayin taron kungiyar karo na 26 a Malabo, ta yadda aka kau da kai akan hakkin Rwanda na shugabancin karba-karba,kamar yadda yake a cikin doka ta shida ta kundin kungiyar. Hakan kuma ya faru ne sanadiyyar shiftar DRC ga kungiyar.” A...
    Ma’aikatar harkokin waje ta kasar Sin, ta sanar a jiya Asabar cewa bisa gayyatar da gwamnatin Birtaniya ta yi masa, memba a hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS, kana mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng, zai ziyarci Birtaniya tun daga yau Lahadi har zuwa Juma’a 13 ga watan nan na Yuni.   Ana sa ran yayin ziyarar tasa a Birtaniya, He Lifeng zai halarci taron farko na tattauna batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka. (Saminu Alhassan) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe ...
    Kafofin yada labarai daga Isra’ila na tabbatar da kutsen da akayi wa kasar akan wasu takardun bayyanan sirrin shirinta na nukiliya. Wannan na zuwa ne kwana guda bayan da Iran ta ce ta samu tarin takardun sirri da suka shafi ayyukan nukiliyar Isra’ila. Ministan leken asirin kasar Iran Esmail Khatib ya ce tarin takardun sirri na Isra’ila da kasar ta samu na da alaka da makaman nukiliyar gwamnatin kuma za su kara karfi ga tsarin garkuwa daga hare-haren sama na Iran. “Takardun da muka samu na da alaka da bayanai game da cibiyoyin nukiliyar su,” kamar yadda Khatib ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na IRIB. Kafafen yada labaran Isra’ila sun tabbatar da hakan, tare da bayyana shi a matsayin “babban...