Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
Published: 30th, July 2025 GMT
Shugaba Bola Tinubu ya amince da naɗin Olumode Samuel Adeyemi a matsayin sabon Shugaban Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa.
Sabon shugaban hukumar zai fara aiki a hukumance daga ranar 14 ga watan Agusta, 2025.
Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a BornoAn sanar da wannan naɗin ne a ranar Laraba cikin wata sanarwa da Hukumar CDCFIB, ta fitar, wacce sakatarenta, Abdulmalik Jibrin, ya rattaba wa hannu.
Wannan naɗin na zuwa ne bayan da shugaban hukumar na yanzu, Injiniya Abdulganiyu Jaji Olola, ke shirin ritaya a ranar 13 ga watan Agusta, 2025, bayan cika shekaru 60 a duniya.
Olumode Samuel Adeyemi yana da ƙwarewa da gogewa a aikin kashe gobara.
Ya fara aikinsa a Hukumar Kashe Gobara ta Abuja, kafin daga bisani ya koma Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa, inda ya bi matakai har ya kai matsayin Mataimakin Shugaban Hukumar a sashen kula da ma’aikata.
A tsawon lokacin da ya shafe yana aiki, ya samu horo da ƙwarewar da ake buƙata a cikin gida da kuma waje.
Haka kuma ya riƙe muƙamai daban-daban a hukumar, kuma memba ne a ƙungiyoyi irin su ANAN, Cibiyar Gudanar da Harkokin Kamfanoni ta Ƙasa, Cibiyar Gudanar da Harkokin Jama’a ta Ƙasa, da kuma Cibiyar Kula da Kuɗaɗe ta Ƙasa.
Hukumar ta yaba wa shugaban da zai ritaya, bisa gudunmawar da ya bayar da kuma irin shirye-shiryen da ya jagoranta a lokacin da yake shugabancin hukumar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa Naɗi Ritaya shugaban hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
Mahara sun kashe akalla mutane biyar a Dajin Madam da ke yankin Karamar Hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi.
Wannan na zuwa ne bayan a makon jiya ’yan bindiga sun kutsa kauyukan da ke kusa da garin Mansur a karamar hukumar, inda suka kashe mutane hudu, suka kwashe kayayyaki a shagunansu.
Daga bisani ’yan sanda sun sun bi su, inda suka fatattake su suka gudu zuwa cikin kungurmin Dajin Madam.
Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed ne ya sanar da mutuwar mutanen a yayin taron zaman lafiya da aka gudanar a garin Nahutan Darazo a kokarinsa na sasanta rikicin baya-bayan nan tsakanin manoma da makiyaya da ya yi sanadin jikkatar wassu mutane a Darazo.
Gwamnan ya kuma nuna matuqar damuwarsa kan bisa yadda mafarauta da a baya suke goyon bayan ayyukan tsaro na kare dazuzzukan jihar a yanzu haka suka shiga cikin rikici da manoma.
Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata ’Yan sa-kai aƙalla 100 da ’yan sanda 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —GwamnatiGwamna ya ce gwamnatinsa tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro da kungiyoyin ’yan banga sun dukufa wajen kwato dabbobin da aka sace da kuma wanzar da zaman lafiya a yankunan karkara.
Ya yaba wa mafarautan yankin bisa ci gaba da goyon bayan da suke bayarwa wajen tabbatar da kare dazuzzukan. “Kun taimaka mana wajen kare dazuzzukanmu a Toro, Ningi, Duguri, Yankari, Kirfi, ba a Darazo kadai ba.
“A ranar Litinin ne ’yan bindiga suka kashe mutane biyar a Dajin Madam, wanda ke kan iyaka da Taraba, Filato, da Bauchi-Alkaleri.
“Me ya sa ba ku taimaka mana a can ba? Muna fuskantar kalubale sosai a dazuzzukanmu. Bauchi tana da dazuzzukan sama da hekta miliyan hudu da tsaunukan da ba kowa zai iya shiga ba, sai ku.”
Gwamna Bala ya alaqanta wannan tashin hankali da kwararowar jama’a daga wasu jihohi zuwa Bauchi, tare da qaruwar yawan jama’a, lamarin da ya qara matsin lamba ga kasa da albarkatun kasa.
Yace Yan bindigan yanzu Suna cikin Jihar Taraba ne,kuma Gwamnan Taraba munyi Magana dashi zamu Yi hadin guiwar Domin a fatattakesu a wurin”
Kan rikicin manoma da makiyaya a Darazo da Sade kuma, gwamna yya kaddamar da wani babban kwamiti da zai binciki rikicin na dajin Aliya, Yautare, da Farin Ruwa na Karamar Hukumar Darazo.
Mataimakin gwamnan jihar, Muhammad Auwal Jatau, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin ne ya kaddamar da kwamitin a gidan gwamnati da ke Bauchi, inda ya kuma bukaci ’yan kwamitin da su gudanar da ayyukansu cikin himma, adalci, da rashin son kai.