Man Utd Na Tattaunawa Da Golan PSG, Chelsea Ta Nace Wa Garnacho
Published: 31st, July 2025 GMT
Manchester United ta soma tattaunawa da Paris St-Germain kan golan Italiya Gianluigi Donnarumma, mai shekara 26, amma Chelsea da Manchester City na cikin masu sha’awar golan. (Telegraph – subscription required, external)
Yayin da ɗanwasan gaba na Sweden Alexander Isak, mai shekara 25, ya amince ya koma Liverpool, Newcastle ta saka ɗanwasan Brazil Rodrigo Muniz, mai shekara 24 cikin lissafinta.
Crystal Palace ta sanar da Arsenal cewa sai ta fara biya aƙalla fam miliyan 35 kafin ta ɗauko Eberechi Eze, daga baya ta cike sauran kuɗin. (Guardian, external)
Palace a shirye take ta biya fam miliyan 27.6 domin ɗauko ɗanwasan baya na Jamus Yann Bisseck, mai shekara 24 daga Inter Milan domin maye gurbin Marc Guehi, da ake alaƙantawa da Liverpool. (Gazzetta dello Sport – in Italian, external)
Chelsea na ci gaba da matsi kan Alejandro Garnacho amma Manchester United na son ta biya ta fam miliyan 40 kan ɗanwasan gaban na Argentina. (Talksport, external)
Lyon ta cimma matsaya tsakaninta da ɗanwasan tsakiya na Liverpool da Ingila Tyler Morton, mai shekara 22, amma kudin da Liverpool ta nema zai iya kawo cikas ga yarjejeniyar. (L’Equipe – in French, external)
AS Roma na nazarin ɗauko ɗanwasan gaba na Wolves Portugal Fabio Silva, mai shekara 23, yayin da kuma take da sha’awar ɗanwasan Argentina da Manchester City mai shekara 19 Claudio Echeverri. (Sky Sports, external)
Matashin ɗanwasan Ingila mai shekara 19 Leo Castledine na shirin zuwa Huddersfield Town a matsayin aro daga Chelsea. (Athletic – subscription required, external)
Ɗanwasan baya na Ingila Rob Holding, mai shekara 29, na shirin barin Crystal Palace domin komawa ƙungiyar Amurka ta Colorado Rapids. (Sky Sports, external)
Middlesbrough ta amince da tayin fam miliyan 20 da Ipswich ta yi kan ɗanwasan Ingila Hayden Hackney, mai shekara 23. (Northern Echo)
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Wasani fam miliyan mai shekara
এছাড়াও পড়ুন:
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
A yau Litinin ne tawagogin kasashen Sin da Amurka, suka sake tattaunawa a rana ta biyu, game da batutuwan tattalin arziki da cinikayya a birnin Madrid na kasar Sifaniya. A jiya Lahadi, sassan biyu sun gudanar da zaman farko ne a fadar Santa Cruz, inda ofishin ministan harkokin wajen kasar ta Sifaniya yake.
A cewar kakakin ma’aikatar cinikayyar kasar Sin, sassan biyu za su tattauna batutuwan da suka hada da matakin Amurka na kakaba jerin haraji daga bangare guda, da keta matakan kayyade fitar da hajoji, da batun dandalin TikTok. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp