Manchester United ta soma tattaunawa da Paris St-Germain kan golan Italiya Gianluigi Donnarumma, mai shekara 26, amma Chelsea da Manchester City na cikin masu sha’awar golan. (Telegraph – subscription required, external)

Yayin da ɗanwasan gaba na Sweden Alexander Isak, mai shekara 25, ya amince ya koma LiverpoolNewcastle ta saka ɗanwasan Brazil Rodrigo Muniz, mai shekara 24 cikin lissafinta.

 (Mail – subscription required, external)

Crystal Palace ta sanar da Arsenal cewa sai ta fara biya aƙalla fam miliyan 35 kafin ta ɗauko Eberechi Eze, daga baya ta cike sauran kuɗin. (Guardian, external)

Palace a shirye take ta biya fam miliyan 27.6 domin ɗauko ɗanwasan baya na Jamus Yann Bisseck, mai shekara 24 daga Inter Milan domin maye gurbin Marc Guehi, da ake alaƙantawa da Liverpool. (Gazzetta dello Sport – in Italian, external)

Chelsea na ci gaba da matsi kan Alejandro Garnacho amma Manchester United na son ta biya ta fam miliyan 40 kan ɗanwasan gaban na Argentina. (Talksport, external)

Lyon ta cimma matsaya tsakaninta da ɗanwasan tsakiya na Liverpool da Ingila Tyler Morton, mai shekara 22, amma kudin da Liverpool ta nema zai iya kawo cikas ga yarjejeniyar. (L’Equipe – in French, external)

AS Roma na nazarin ɗauko ɗanwasan gaba na Wolves Portugal Fabio Silva, mai shekara 23, yayin da kuma take da sha’awar ɗanwasan Argentina da Manchester City mai shekara 19 Claudio Echeverri. (Sky Sports, external)

Matashin ɗanwasan Ingila mai shekara 19 Leo Castledine na shirin zuwa Huddersfield Town a matsayin aro daga Chelsea. (Athletic – subscription required, external)

Ɗanwasan baya na Ingila Rob Holding, mai shekara 29, na shirin barin Crystal Palace domin komawa ƙungiyar Amurka ta Colorado Rapids. (Sky Sports, external)

Middlesbrough ta amince da tayin fam miliyan 20 da Ipswich ta yi kan ɗanwasan Ingila Hayden Hackney, mai shekara 23. (Northern Echo)

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Wasani fam miliyan mai shekara

এছাড়াও পড়ুন:

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

Yau Talata, kwamitin kwaskwarima da raya kasar Sin, ya fitar da kudin Sin RMB yuan miliyan 200, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 28, domin tallafawa wajen farfado da sassan birnin Beijing da bala’in ambaliyar ruwa ya shafa, musamman ma fannin sake gina ababen more rayuwar jama’a na sufuri, da samar da ruwan sha, da kiwon lafiya, da na hidimomin al’umma a gundumomin Miyun da Huairou, a kokarin ganin rayuwa ta dawo kamar yadda take a wuraren, an kuma dawo da ayyuka kamar yadda aka saba.

Ban da haka kuma, ma’aikatar kudi, da ma’aikatar lura da ayyukan gaggawa ta kasar sun zuba kudin Sin yuan miliyan 350, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 49 don tallafawa biranen Beijing, da Tianjin, da lardunan Hebei, da Shanxi, da Jilin, da Shandong, da Guangdong, da Shaanxi da jihar Mongolia ta Gida, ta yadda za su samu zarafin gudanar da ayyukan ceto, da rage radadin bala’u, da kuma taimakawa wadanda bala’in ya shafa. (Tasallah Yuan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara
  • Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
  • Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai