Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Published: 10th, October 2025 GMT
Rundunar ƴansanda ta Jihar Kano ta ce ta ceto mutane uku da aka sace a yayin wani aiki biyu da ta gudanar a Kano da Kaduna, tare da ƙwato babur da wasu shaidu. Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Juma’a.
A cewar Kiyawa, a ranar 7 ga Oktobar 2025, rundunar daƙile garkuwa da mutane (Anti-Kidnapping) tare da tawagar sa-ido daga ofishin ƴansanda na Bebeji sun gudanar da sumame bayan samun bayanan sirri kan wani mutum da ya tsere daga hannun masu garkuwa da mutane.
A wani sumame daban, rundunar ta ce a ranar 9 ga Oktoba 2025, ta kuma ceto wani matashi, Ashiru Murtala, mai shekaru 19, wanda aka sace daga Beli, a ƙaramar hukumar Rogo da ke Kano, a ranar 5 ga Oktoba. An same shi a gonar rake a Hunkuyi da ke ƙaramar hukumar Kudan ta Kaduna bayan masu garkuwar sun gudu.
Kwamishinan Ƴansanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya umurci a bai wa waɗanda aka ceto kulawar likita tare da ci gaba da bincike domin kama waɗanda ke da hannu a garkuwar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta samu nasara a wasan mako na 14 na Nigeria Premier Football League (NPFL), bayan da ta doke Ikorodu City da ci 2–1 a filin wasa na Muhammad Dikko, da ke birnin Katsina.
Wannan ita ce nasara ta uku da Pillars ta samu a kakar bana, cikin wasanninta 14, inda ta yi kunnen doki uku, sannan ta sha kashi shida.
’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun TuraiKafin wannan wasan, Kano Pillars ta yi wasanni takwas a jere ba tare da samun nasara ba.
Pillars ta zura kwallayenta ne ta hannun Rabiu Ali, wanda ya zura ta farko a minti na 3, sai Olakunle Alaka ya kara ta biyu a minti na 30.
A daidai minti na 45, kafin a je hutun rabin lokaci, Joseph Arumala ya rage tazara ga Ikorodu City.
Duk da wannan nasarar, Kano Pillars ta ci gaba da zama a matsayi na 20, inda take da maki 9 a ƙasan teburin gasar.
A wani labarin, ƙungiyar Katsina United ta samu nasarar doke Enyimba da ci 3–2 a birnin Ilorin, inda take buga wasanninta na gida bayan dakatar da ita daga yin wasa a filin gidan ta a Katsina.