Leadership News Hausa:
2025-11-27@21:15:55 GMT

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Published: 10th, October 2025 GMT

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Rundunar ƴansanda ta Jihar Kano ta ce ta ceto mutane uku da aka sace a yayin wani aiki biyu da ta gudanar a Kano da Kaduna, tare da ƙwato babur da wasu shaidu. Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Juma’a.

A cewar Kiyawa, a ranar 7 ga Oktobar 2025, rundunar daƙile garkuwa da mutane (Anti-Kidnapping) tare da tawagar sa-ido daga ofishin ƴansanda na Bebeji sun gudanar da sumame bayan samun bayanan sirri kan wani mutum da ya tsere daga hannun masu garkuwa da mutane.

Wanda aka sace, Abdul Hamid Bello, mai shekaru 21, ya taimaka wajen kai jami’an tsaro inda aka ceto wani mutum mai suna Musa Idris, mai shekaru 65, a Saya-Saya, Ikara LGA ta Kaduna, yayin da masu garkuwar suka tsere.

Ma’aikatan Jinya Sun Yaba Wa Gwamnatin Kaduna Kan Aiwatar Da Sabon Tsarin Albashi ‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

A wani sumame daban, rundunar ta ce a ranar 9 ga Oktoba 2025, ta kuma ceto wani matashi, Ashiru Murtala, mai shekaru 19, wanda aka sace daga Beli, a ƙaramar hukumar Rogo da ke Kano, a ranar 5 ga Oktoba. An same shi a gonar rake a Hunkuyi da ke ƙaramar hukumar Kudan ta Kaduna bayan masu garkuwar sun gudu.

Kwamishinan Ƴansanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya umurci a bai wa waɗanda aka ceto kulawar likita tare da ci gaba da bincike domin kama waɗanda ke da hannu a garkuwar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi October 10, 2025 Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC  October 9, 2025 Manyan Labarai Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta October 9, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta samu nasara a wasan mako na 14 na Nigeria Premier Football League (NPFL), bayan da ta doke Ikorodu City da ci 2–1 a filin wasa na Muhammad Dikko, da ke birnin Katsina.

Wannan ita ce nasara ta uku da Pillars ta samu a kakar bana, cikin wasanninta 14, inda ta yi kunnen doki uku, sannan ta sha kashi shida.

’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai

Kafin wannan wasan, Kano Pillars ta yi wasanni takwas a jere ba tare da samun nasara ba.

Pillars ta zura kwallayenta ne ta hannun Rabiu Ali, wanda ya zura ta farko a minti na 3, sai Olakunle Alaka ya kara ta biyu a minti na 30.
A daidai minti na 45, kafin a je hutun rabin lokaci, Joseph Arumala ya rage tazara ga Ikorodu City.

Duk da wannan nasarar, Kano Pillars ta ci gaba da zama a matsayi na 20, inda take da maki 9 a ƙasan teburin gasar.

A wani labarin, ƙungiyar Katsina United ta samu nasarar doke Enyimba da ci 3–2 a birnin Ilorin, inda take buga wasanninta na gida bayan dakatar da ita daga yin wasa a filin gidan ta a Katsina.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano