Kwastam ta kama buhunan lalatacciyar fulawa 10,000 ana ƙoƙarin shigo da ita Najeriya
Published: 10th, October 2025 GMT
Hukumar Kwastam shiyyar bodar Najeriya ta Seme da ke jihar Legas ta ce ta cafke motoci biyar da ke maƙare da buhuna 10,000 na lalatacciyar fulawa da darajarsu ta kai Naira biliyan 1.2.
Rundunar ta kuma ce ta tara jimillar kuɗin shigar da ya kai Naira biliyan daya da rabi a watan Satumba, wanda hakan ya nuna kari da kaso 182 cikin 100 idan aka kwatanta da Naira miliyan 531 da aka tara a watan Agustan da ya gabata.
Kwamandan rundunar a shiyyar, Wale Adenuga, ne ya bayyana hakan a taron manema labarai na farko da ya gudanar a ranar Alhamis a kan bodar Seme.
Adenuga ya ce kayan da aka kama sun fito ne daga ƙasar Masar ta hanyar iyakar Jamhuriyar Benin, kuma an kama su ne a wani haɗin gwiwar jami’an hukumar NAFDAC.
Kwamandan ya ce an samu nasarar cafke kayan ne bisa sahihan bayanan sirri da Babban Kwamandan Kwastam, Adewale Adeniyi, da Daraktan NAFDAC, Moji Adeyeye, suka bayar.
Yayin da yake nuna kayan da aka kama, Adenuga ya ce garin fulawar an sarrafa shi ne a watan Maris 2024, kuma wa’adin amfani da shi ya kare ne a watan Nuwamba bara, yana mai cewa yana da hatsari ga lafiya ga jama’a idan aka yi amfani da shi.
“Idan aka shigo da irin waɗannan kayayyaki ƙasar nan, suna sauya buhunan su, su shigar da su kasuwa… akwai hatsari ga lafiya tattare da cin kayayyakin da suka lalace saboda za su iya haifar da cututtuka masu tsanani da sauran matsalolin lafiya na dogon lokaci.”
“Baya ga barazanar lafiya, irin waɗannan kayayyaki marasa inganci na rage darajar masana’antu na cikin gida da kuma amincewar masu saye.”
Yayin da yake bayani kan wasu kayayyakin da rundunar ta kama a watan Satumba, Adenuga ya ce rundunar ta kama fakiti 1,104 na tabar wiwi bisa bayanan sirri da ta samu.
Ya ƙara da cewa rundunar ta kama mutane biyu da fakiti 120 na maganin Tramadol.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fulawa Kwastam rundunar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
Daga cikin wadanda shugaban kasar ta Nigeria ya yi wa afuwa da kawai Maryam Sanda ‘yar shekaru 37 wacce aka yankewa hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda samunta da kashe mijinta da wuka a 2017.
Mai Magana da yawun shugaban kasa Bayo Onangua ya saki bayanin afuwar da shugaban kasar ya yi, wacce kuma ta hadad a Faruka Lawan tsohon dan majalisa da aka samu da laifin cin hanci da rashawa a 2021.
Sai kuma Ken Saro-wiwa wanda dan fafutuka ne mai rajin kare muhalli a yankin Ogoni da aka zartarwa hukuncin kisa a 1995.
Har ila yau afuwar ta shugaba Tunibu ta shafi Manjo Janar Mamman Jiya Vatsa wanda aka zartarwa da hukuncin kisa a 1986 saboda juyin Mulki.
Haka nan kuma shugaba Tinibu ya yafewa Sir Herbert Macaly dan kishin kasa da ya yi fada da ‘yan mulkin mallaka. ‘Yan mulkin mallaka ne su ka yanke masa hukunci a 1913.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga ‘Yar Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa October 11, 2025 Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref October 11, 2025 Iran Ta Bukaci HKI Ta Aiwatar Da Yarjeniya Da Gaza Kamar Yadda Take October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci