Hukumar Kwastam shiyyar bodar Najeriya ta Seme da ke jihar Legas ta ce ta cafke motoci biyar da ke maƙare da buhuna 10,000 na lalatacciyar fulawa da darajarsu ta kai Naira biliyan 1.2.

Rundunar ta kuma ce ta tara jimillar kuɗin shigar da ya kai Naira biliyan daya da rabi a watan Satumba, wanda hakan ya nuna kari da kaso 182 cikin 100 idan aka kwatanta da Naira miliyan 531 da aka tara a watan Agustan da ya gabata.

NAJERIYA A YAU: Kalubalen Da Ke Gaban Sabon Shugaban Hukumar Zabe Ta Kasa Tinubu ya yi wa Mamman Vatsa, Farouk Lawan da wasu mutum 173 afuwa

Kwamandan rundunar a shiyyar, Wale Adenuga, ne ya bayyana hakan a taron manema labarai na farko da ya gudanar a ranar Alhamis a kan bodar Seme.

Adenuga ya ce kayan da aka kama sun fito ne daga ƙasar Masar ta hanyar iyakar Jamhuriyar Benin, kuma an kama su ne a wani haɗin gwiwar jami’an hukumar NAFDAC.

Kwamandan ya ce an samu nasarar cafke kayan ne bisa sahihan bayanan sirri da Babban Kwamandan Kwastam, Adewale Adeniyi, da Daraktan NAFDAC, Moji Adeyeye, suka bayar.

Yayin da yake nuna kayan da aka kama, Adenuga ya ce garin fulawar an sarrafa shi ne a watan Maris 2024, kuma wa’adin amfani da shi ya kare ne a watan Nuwamba bara, yana mai cewa yana da hatsari ga lafiya ga jama’a idan aka yi amfani da shi.

“Idan aka shigo da irin waɗannan kayayyaki ƙasar nan, suna sauya buhunan su, su shigar da su kasuwa… akwai hatsari ga lafiya tattare da cin kayayyakin da suka lalace saboda za su iya haifar da cututtuka masu tsanani da sauran matsalolin lafiya na dogon lokaci.”

“Baya ga barazanar lafiya, irin waɗannan kayayyaki marasa inganci na rage darajar masana’antu na cikin gida da kuma amincewar masu saye.”

Yayin da yake bayani kan wasu kayayyakin da rundunar ta kama a watan Satumba, Adenuga ya ce rundunar ta kama fakiti 1,104 na tabar wiwi bisa bayanan sirri da ta samu.

Ya ƙara da cewa rundunar ta kama mutane biyu da fakiti 120 na maganin Tramadol.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fulawa Kwastam rundunar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana kaduwa da rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci kuma jagoran Tijjaniyya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

Fitaccen malamin ya rasu a Bauchi ranar Alhamis yana da shekaru 101.

Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka

A cikin wata sanarwa da Kakakin shugaban, Bayo Onanuga, ya fitar, Tinubu ya bayyana Sheikh Dahiru Bauchi a matsayin jagoran da ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyarwa, wa’azi da jagorantar al’ummar Musulmi.

Tinubu ya ce rasuwar malamin ba wai asara ce ga iyalansa da almajiransa kawai ba, har ma ga ƙasa baki ɗaya.

“Sheikh Dahiru Bauchi malami ne, uba ne kuma murya ce ta daidaito da hikima. A matsayinsa na mai wa’azi kuma babban mai fassarar Alƙur’ani mai tsarki, ya kasance mai kira ga zaman lafiya da tsoron Allah. Rasuwarsa ta bar babban gibi,” in ji Shugaban Ƙasa.

Ya tuna da albarka da ya samu daga marigayin a lokacin shirye-shiryen zaɓen 2023.

Shugaban Ƙasa ya miƙa ta’aziyya ga almajiran malamin a faɗin Najeriya da wajen ƙasar, yana mai kira da su dawwamar da sunansa ta hanyar bin koyarwarsa ta zaman lafiya, tsoron Allah da kyautatawa ɗan adam.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci
  • Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi
  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe