Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai
Published: 10th, October 2025 GMT
Kazalika, tarihin Dimokiradiyyar kasar ya sha cin karo da kwam gaba kwam baya kusan za a iya cewa, tun bayan dawowar mulkin Demokaradiyya a 1979 da kuma sake dora kasar a wata turbar ta Demokiradiyyar a 1999.
Alal misali, jamhuriyya ta hudu ta kasance ta jima sosai, amma kusan babu wasu ayyukan na inganta rayuwar ‘yan kasar da za a bigi Kirji a ce gasu an gani a kasar a zahiri.
Idan aka dubi bangaren samar da hasken wutar lantarki kusan za a iya cewa, karni da dama da suka bace, har zuwa yau Nijeriya ta gaza samar da karfin wutar da kuma rabar da ita da ta kai karfin Megawatts 5,000 musamman duba da cewa, wannan adadin bai wuce na wani can karamin birini ne, za a samar ba, idan aka yi la’kari da kasar, wadda ake mata kirari da uwa ga daukacin kasahen da ke a nahiyar Afirka.
Bugu da kari, an jibga dimbin biliyoyin Naira domin farfado da fannin, amma har zuwa yau, haka ba ta comma ruwa ba.
Wani karin abin takaicin shi ne, na kalubalen rashin tsaro da ya ke ci gaba da wata zama babbar barazana ga kasar, domin sama da rayukan ‘yan kasar 169,000 da ba su ji ba su kuma gani ba aka hallaka daga tsakanin 2006 zuwa 2021.
Sun rasa rayukansu ne, ko dai, sanadiyyar wasu tashe-tashen hankula ko na hare-haren Boko Haram ko na ‘yan bindiga daji ko a rikice-rikicen manoma da Fulani Makiyaya ko kuma a rikice-rikicen kabilanci.
A takaice, za a iya cewa, dubban mutane ne, suka rasa rayukansu kusan a karni biyu da suka bace, inda adadin ya rubanya na wadanda aka hallaka, a lokacin yakin basasa a kasar.
Hakazalika, a bangaren batun gudanar da sauye-sauye tare da yin amfani da fasahar zamani a harkar gudanar da zabe a kasar, musamman domin a gudanar da sahihin zabe da kuma dakile matsalar sayen kuri’u, amma har zuwa yau, babu abinda ya sauya wanda daga karshe, ‘yan takardar da aka yiwa wa kaci ka tashi a lokacin da aka tabka magudi a zabubbukan, ke garzaywa zuwa kotu, domin bin hakwinsu.
Kazalika, batun cin hanci da rashawa na daya daga cikin matsalar da ta daidaita kasar, an yi kiyasin cewa, a 2012, Nijeriya ta tabka asarar da ta kai ta sama da dala biliyan 400.
Wannan adadin sun isa ace, an yi amfani da su, wajen gina hanyotin Layin Dogo da makarantu da gina Asibiti da kuma masana’antu, amma abin bakin ciki, wasu sun yi kwaciyar Magirbi kan wadannan kudaden.
Amma duk da wadannan matsalolin, an gudanar da bikin na samun ‘ yancin kan kasar, musamman a yayin da, ake ci gaba da nuna damuwa a kasar .
A bangaren masana’antar kirkire-kirkiren fasaha, fannin ya samu daukaka har a idon duniya, inda misali, fitattun mawaka da kuma a bangaren masu shiyar Fina-Finai, a masana’antar Nollywood suka kai wani mataki a duniya, musamman wajrn birge masu bibiyarsu.
Alal misali, daga mawaki irinsu Dabido, Wizkid, Burna Boy, har ta kai ga, sun shahara a Nahiyar Turai.
Haka batun dai yake a fannin kimiyyar zamani na kasar, duba da cewa, Nijeriya ta kai matakin mamaye kasashen da ke Afirka a bangaren zuba kudade, a fannin.
Suma matasan ‘yan kasuwa, musamman a jihar Legas da kuma Abuja, inda suke kirirar manhajar zamani, ta hada-hadar kudade da da kuma samar da kayan fasahar zamani.
Karin wata matsalar da ke ci gaba da zamowa ruwan dare a kasar shi ne, na yawan samun karuwar kwararrun Likitoci, da ke ficewa zuwa kasashen duniya, domin neman aikin, ganin cewa, a kasashen ana tsoka, inda a Birtaniya suke ci gaba baza hajarsu, su kuma kwararrun Injinoyi na kasar nan nan da suka noma zuwa Amurka, ke ci gaba da zan akalar tsari na fannin na kasar.
Duk hakan na akuwa ne, saboda gazawar tsarin kasar wanda hakan ya sanya, aka gaza ci gaba rike irin wadannan zakakuran da ake da su a kasar.
Nigeriya ta kasance, ta na alumma sama da kaso 60, wanda kuma masu shekaru 25, suka kasance masu hazakar da za a iya amfani da ita wajen ciyar da kasar gaba.
Bugu da kari, kasar na kuma da dimbin marasa aikin yi wanda hakan ya kara haifar da samun aikata nau’ukan laifuka da dama.
Hakazalika, akwai da dama da suka haura har zuwa iyakokin kasar, misali ta hanyar amfani da kungiyar ECOWAS da kuma yarjejeniyar hada-hadar kasuwanci ta Afirka wato AfCFTA wanda hakan ya bai wa kasar damar wajen kara bunkasa fannin tattalin arzikinta.
Amma saboda rashin tafiyar da shugabanci yadda ya kamata da rashin ingantattun kayan aiki da rashin samar da kyakyawan yanayi a bangaren harkar tsaro, wadannan matsalolin, suna kasar cin gajiyar wannan damar.
Kasar ta cika shekaru 65 da samun ‘yancin kai, amma tana ci gaba da fuskantar kalubale iri-iri da suka hada da cin hanci da rashawa, matsalar rashin tsaro da ta hana yara ci gaba da zuba makaranta.
A nan, zamu iya cewa shekaru 65, sun isa ace an koyi darasi a kasar.
Kazalika, ra’ayinmu a nan shi ne, abinda ake bukata a bangaren masu rike da madafun iko, su mayar da hankali wajen wandar da tsare-tsaren da za su inganta rayuwar ‘yan kasar da kuma ciyar da kasar gaba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina
Duk da Najeriya na cikin yanayin damina, wanda ake ganin a lokacin ta fi samar da wutar lantarki ga ’yan ƙasarta, amma jama’a a jihohin Kaduna da Kano na ci gaba da kokawa kan ƙarancin wutar.
A duk shekara jama’a na more wutar lantarki a Nijeriya a lokacin damina saboda tashoshin ruwa na samar da wutar lantarki suna aiki da cikakken ƙarfinsu.
Amma, wasu masana a ɓangaren wutar sun shaida wa wakilinmu cewa duk da matsalolin masu nasaba da lalata kayan aiki da kuma ƙin biyan kuɗin wuta da wasu masu amfani da ita ke yi, kamfanonin rarraba wutar (DisCos) suna yin iya bakin ƙoƙarinsu wajen cike giɓin.
Masu ruwa da tsaki sun bayyana cewa ana ƙoƙarin daidaita rarraba wuta tsakanin yankunan masana’antu da wuraren da aka sanya wa mita da ke biyan kuɗin wuta, da kuma sauran gidaje.
’Yan Najeriya miliyan 60 na fama da taɓin hankali — Likita Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a BornoA Katsina, rashin daidaito a rarraba wuta ya kawo babban cikas ga kasuwanci inda dubban masu sana’o’i suka rasa ayyukansu, gidaje kuma ke yin kwanaki ba tare da wuta ba.
Masu shayi, gidajen masu burodi, masu walda da sauran ƙananan sana’o’ da ke dogaro da wuta su ne suka fi shan wahala.
Dakta Isma’il Balarabe ya ce, “Kasuwancinmu sun durƙushe, mun yi asarar dukiya saboda rashin wuta. Wani lokaci ma, ba mu samun wutar awa ɗaya a rana.”
Shi ma Dakta Muktar Alkasim ya ce, “A gaskiya babu wutar da za ta iya tafiyar da kowace irin kasuwanci a nan Katsina. Wurin da ake samu ma, sai dai lokaci-lokaci kuma ƙarfin ba ya isa a kunna kayan aiki.”
Haka ma wata ’yar kasuwa, Misis Ngozi Anosike, ta ce sana’arta ta tsaya. “Akwai lokutan da muke yin mako guda ko fiye babu wuta. Idan ma ta zo, kusan awa ɗaya ne, kuma ba ta da ƙarfi.”
Hajiya Hannatu ta ce, “Ba zan iya sayen nama ko kifi da yawa ba saboda idan na saka a firji, zai lalace. Idan ma an samu wuta, ƙarfin bai isa ya ɗauki firji ba.”
Kano: An fifita masu biyan kuɗi da yawaA Kano kuwa, rahotanni sun nuna akwai babban bambanci a yanyanin rarraba wutar lantarki tsakanin yankunan kasuwanci da na gidaje. Wuraren kasuwanci sun fi samun wuta saboda suna biyan kuɗin wuta mai tsada, yayin da gidaje da dama ke shafe mafi yawan lokaci babu wutar.
Jama’a na ƙorafi kan cewa kamfanin KEDCO na fifita wuraren kasuwanci a yayin da al’ummomi da dama ke kwana cikin duhu.
Wani mazaunin unguwar Na’ibawa, Ahmad Aminu, ya ce, “A da idan damina ta yi, mukan samu wuta sosai saboda tashoshin ruwa suna aiki da cikakken ƙarfi. Amma bana abin ya canza. Sai sa misalin ƙarfe 11 na dare ake kawo wuta, a ɗauke ƙarfe 5 na asuba.”
Yusuf Idris daga unguwar Kuntau ya ce, “A baya muna biyan kusan N5,000 a wata. Amma watanni biyu da suka gabata an ƙara zuwa fiye da N17,000. Amma duk da haka ba mu samun wutar sosai.”
Ya ƙara da cewa mutane da dama sun daina amfani da wutar gwamnati, sun koma mai amfani hasken rana.
Amma duk da haka, kwastomomi da ke biyan kuɗaɗe masu yawa, musamman masana’antu, suna amfana da ƙarin wuta bisa sabon tsarin.
Sama’ila Sulaiman, mai sana’ar ƙanƙara a yankin Farm Centre, ya ce, “Yanzu muna samun wuta har ta awa 22 a rana saboda mu muna biyan kuɗaɗe masu yawa.”
Martanin KEDCOKakakin Kamfanin KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce a zahiri akwai tsayayyiyar wuta a yankunan Kano da Katsina da Jigawa, sai dai iska da ruwan sama kan karya turakun wuta a wasu wurare.
Ya ce, “A wasu lokuta ana samun ɗan tsaiko saboda gyaran da Kamfanin Tura Wutar Lantarki ta Ƙasa (TCN) ke yi, haka nan yajin aikin ma’aikatan PENGASSAN ya shafi rarraba wutar.”
Ya bayyana cewa kamfanin yana zuba jari a sabbin kayan aiki da kuma samar da wuta daga hasken rana. “Mun fara amfani da Hasken Solar a Kano domin ƙara ƙarfinmu. Muna fatan kafin ƙarshen shekara mai zuwa mu samar da aƙalla megawatt 150 daga hasken rana.”
Kaduna: Al’umma na cikin duhuMazauna yankin Tudun Wada da ke Ƙaramar Hukumar Kaduna ta Kudu ta Jihar sun koka cewa tun watan Satumba aka rage ba su wuta.
Hadiza Adam, wadda ke sana’at sayar da ruwan leda ta ce, “Yawanci dai ciki dare ake kawo mana wuta, lokacin da kowa ke barci. Don haka ribar da nake samu kullum tana raguwa.”
Muhammad Ahmed ya ce, “Yanzu wutar sai da ƙarfe 1 na dare ake kawo ta su kuma ɗauke da safe. Mu ba masu gadi ba ne da za mu rika zama don jiran wuta. Amma duk wata sai sun kawo mana bill cewa suna bin mu dubban nairori.”
Unguwanni da dama a Kaduna—kamar Rigasa da Hayin Ɗan Mani da Zango da Sabon Gari da sauransu—sun kai watanni suna yin kwanaki babu wuta. Wasu sun koma yin rajista kai wayoyinsu wajen masu cajin ko amfani da injin janareta.
Badamasi Isa da ke yankin Hayin Ɗan Mani ya ce,
“Tun watan Fabrairu ba mu samun wuta da dare. Hakan ya rusa kasuwancin masu kayan sanyi da masu walda.”
Mustapha Baban Sultan daga yankin Millennium City ya ce, “Yanzu tsarin ya zama ‘iya kuɗinka iya shagalinka’. Masu arziki suna Band A, suna samun wuta sosai amma suna biyan kuɗaɗe masu yawa. Talakawa kuwa babu wuta amma ana cajin su.”
Wasu mazauna sun bayyana cewa saboda rashin wuta sai sun koma amfani da hasken rana wajen samun ruwan sha da gudanar da rayuwa.
Duk da haka, Kamfanin Wutar Lantarki na Kaduna ya alaƙanta matsalar da lalata layin wuta da iska mai ƙarfi ta yi a wannan daminar.
Rahoton Hukumar Rarraba Wuta ya nuna cewa daga cikin megawat 4,025 da ake samarwa a Nijeriya, yankin Arewa na samum kusan kashi ɗaya bisa huɗu ne kawai.
Masu ruwa da tsaki sun danganta hakan da matsalar rashin saka hannun jari a ɓangaren rarraba wutar da matsalar satar kayayyakin wuta da kuma rashin biyan kuɗin wuta daga jama’a.
Shugaban Ƙungiyar Kare Haƙƙodin Kwastomomi ta Nijeriya, Kunle Olubiyo, ya ce rushewar masana’antu a Arewa ta rage buƙatar wuta, sannan satar wuta da rashin kayan aiki na zamani su ma suna kawo cikas.
Ya ce, “A da masana’antu a Kano, Kaduna da Maiduguri suna jan wuta sosai. Amma yanzu sun lalace, sai Kano kawai ta rage. A Kanon ma akwai matsalar sata da kuma rashin isassun kayan aiki a layin rarrabawa.”
Ya ƙara da cewa, “Kamfanonin rarraba wuta kan fifita wuraren da za su iya dawo da kuɗaɗensu. Idan aka kai wuta wuraren ba a biyan kuɗi, sukan ki karɗar nauyin rabon. Wannan shi ne abin da ya fi dagula lamarin a Arewa, inda wasu wurare ke samun ƙarin wuta, wasu kuma ba su samu wutar ba,” in ji shi.