Aminiya:
2025-10-13@13:41:36 GMT

Tinubu ya yi wa Mamman Vatsa, Farouk Lawan da wasu mutum 173 afuwa

Published: 10th, October 2025 GMT

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da afuwar Shugaban Kasa ga mutane 175.

Daga ciki har da wadanda aka yi wa afuwar bayan mutuwa ga marigayi Manjo Janar Mamman Jiya Vatsa da ɗan gwagwarmayar kwato ’yancin kan Najeriya, Herbert Macaulay.

An dauki wannan mataki ne bayan amincewa da shawarwarin da Majalisar Tsofaffin Shugabannin Ƙasa ta bayar a taronta da aka gudanar a ranar Alhamis a Abuja.

Gwamnatin Kano ta shirya ɗaurin auren ma’aurata 2,000 Tinubu ya naɗa Amupitan a matsayin Shugaban INEC

A cewar sanarwar da mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin bayanai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya kuma yi afuwa ga tsohon ɗan majalisa Farouk Lawan da wasu mutum uku, Misis Anastasia Daniel Nwaobia, Lauya Hussaini Umar, da Ayinla Saadu Alanamu, bayan an tabbatar da cewa sun nuna nadamarsu da shirin komawa cikin al’umma.

Vatsa, wanda marubuci ne kuma tsohon jami’in soja da aka kashe a shekarar 1986 bayan tuhumarsa da cin amanar ƙasa, ya samu afuwa bayan mutuwa kusan shekaru arba’in bayan kasha shi.

Haka kuma, Herbert Macaulay, ɗaya daga cikin fitattun ’yan gwagwarmayar Najeriya da kuma wanda ya kafa jam’iyyar NCNC, ya samu afuwa kan hukuncin da hukumomin mulkin mallaka suka yanke masa a shekarar 1913.

Sanarwar ta kuma tabbatar da cewa Shugaba Tinubu ya yi afuwa ga fursunoni 82, ya rage wa wasu 65 zaman gidan yari, sannan ya sauya hukuncin kisa na wasu mutum bakwai zuwa ɗaurin rai da rai.

Bugu da ƙari, Shugaban Ƙasa ya yi afuwa ga ’yan gwagwarmayar Ogoni tara da aka kashe, Ken Saro-Wiwa, Saturday Dobee, Nordu Eawo, Daniel Gbooko, Paul Levera, Felix Nuate, Baribor Bera, Barinem Kiobel, da John Kpuine, tare da ba wa wasu huɗu lambar yabo ta ƙasa bayan mutuwa: Cif Albert Badey, Cif Edward Kobani, Cif Samuel Orage, da Theophilus Orage.

Wannan mataki ya biyo bayan shawarwarin da Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Hakkin Yin Afuwa (PACPM) ya bayar, ƙarƙashin jagorancin Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari’a, Prince Lateef Fagbemi (SAN).

Kwamitin ya duba bukatu 294, inda ya ba da shawarar yin afuwa ga fursunoni 82, afuwar kai tsaye ga mutum biyu, rage zaman gidan yari ga mutum 65, sauya hukuncin kisa ga mutum bakwai zuwa ɗaurin rai da rai, da kuma afuwa bayan mutuwa ga tsofaffin masu laifi 15.

Ka’idojin da kwamitin ya yi amfani da su sun haɗa da shekaru (60 zuwa sama), ciwon da ba ya warkewa, ƙuruciya (16 zuwa ƙasa), nuna kyakkyawan hali a gidan yari na tsawon lokaci, da nuna nadama, da sauransu.

Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ne ya ƙaddamar da kwamitin na PACPM a watan Janairu 2025 don inganta adalci, gyaran hali da kare haƙƙin ɗan adam a ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Afuwa Farouk Lawan bayan mutuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

Ministar wadda ta je kamfanin domin daukar sabuwar motarta ta alfarma kirar Nord Demir SUB da kamfanin ya hada nataimakin Shugaban jami’ar na sashen kula da ilimi da gudanar da bincike Farfesa Bola Oboh da kuma Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi ne, suka karbi bakuncinta.

 

A jawabin da ta gabatar a lokacin ziyarar ministar ta bayyana cewa,Duba da yarjejeniyar hada-hadar kasuwanci wajen fitar da kaya zuwa ketare kamfanin zai iya yin amfani da wannan samar waken fitar da motocinsa zuwa ketare.

 

Ta kara da cewa, Nijeriya na da gurare biyu ne da ake hada motoci da suka hada da, na wannan jami’ar da kuma na EPs, inda ta yi nuni da cewa, karfin da kamfanin ya ke da shi, zai iya cike gibin bukatar da ake da ita, ta ‘yan kasar na bukatar motocin.

 

Ya ci gaba da cewa, za mu ci gaba da kara karfafa kwarin guwair ‘yan kasar domin da kuma sauran kamfanoni masu zaman kansu domin su rinka sayen kayan da kamfanonin kasar, suka sarrafa da kuma hada su.

 

Ta ce, wannan babban abin alhari ne, ganin cewa, a wannan jami’ar ce, aka hada wannan mortar.

 

Shi kuwa a na sa jawabin Farfesa Oboh ya bayyana cewa, muna Myrna da wannan shirin na Gwamnatin Tarayya wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ke jagorantar bai wa ‘yan kasar kwarin guwair sayen kayan da aka sarrafa a cikin kasar

A cewarsa, jami’ar ta UNILAG, ba wai kawai na yin alfahari da samun wannan wajen hada motocin ba ne, kadai amma ta na alharin da cewa, an samar da wajen a jami’ar.

Shi ma, Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi, a yayin da ya ke nuna jin dadinsa kan gudunmwar da ministar ke bai wa kamfanin ya a bayyana cewa, na yi matukar farin ciki ganin cewa, ministar ta kasance daya daga cikin abokan cinikayyar mu

Kazalika, Shugaban ya kuma gode wa mahukunta jami’ar ta UNILAG kan yin hadaka da kamfanin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tattalin Arziki Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho October 10, 2025 Tattalin Arziki An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi  October 10, 2025 Tattalin Arziki Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida