Majalisar Wakilai Zata Dauki Mataki Akan Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba
Published: 9th, October 2025 GMT
Majalisar Wakilai za ta kaddamar da yakin kawo karshen Hakar Ma’adinai ba bisa ka’ida ba dake al’ummar kasar asarar sama da dalar Amurka biliyan 9 duk shekara.
Shugaban Kwamitin wucin gadi kan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, Sanni Abdulraheem, ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da jawabinsa a lokacin kaddamar da kwamitin a harabar majalisar dokokin tarayya Abuja.
Sanni Abdulraheem, wanda ya jaddada mahimmancin kwamitin ga tattalin arzikin kasa, ya bayyana hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a matsayin wani bala’i da ke gurgunta kudaden shiga na kasa, da rura wutar aikata laifuka, da kuma zubar da muhalli.
Shugaban kwamitin ya bayyana cewa, wani bangare na ayyukan kwamitin na toshe hanyoyin samun kudaden shiga, tabbatar da gaskiya, da kuma tabbatar da cewa arzikin ma’adinan kasa na bayar da gudummawa sosai ga ci gaban tattalin arziki.
“An kiyasta cewa Najeriya na asarar kusan dala biliyan 9 a duk shekara saboda ayyukan hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, wannan satar albarkatunmu da ya kamata ya ciyar da al’ummarmu ya dade da yawa, kuma lokaci ya yi da za a kawo karshensa,” in ji dan majalisar.
Abdulraheem ya bayar da tabbacin cewa, ta hanyar sa-ido, majalisar za ta karfafa hanyoyin bin diddigin kudaden shiga, da kuma tabbatar da cikkaken alfanun da ake samu daga bangaren ma’adinai na Nijeriya kai tsaye zuwa cikin asusun gwamnati, maimakon wasu tsirarun mutane ne.
Dangane da kamfanin karafa na Ajaokuta, shugaban kwamitin ya koka da cewa, a tsawon shekarun da suka gabata, ba a yi amfani da muhimman kadarorin masana’antu ba, yayin da sauran kasashe ke cin gajiyar irin wannan albarkatun, yana mai jaddada cewa tare da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, da ba a taba yin irinsa ba, za a farfado da masana’antar nan ba da jimawa ba.
Kwamandan hukumar tsaron farin kasa ta civil Defense ya ba da tabbacin cewa hukumar tsaro ta farin kaya ta Najeriya za ta baiwa kwamitin goyon baya da hadin kai don ganin an cimma dukkan muhimman harajin.
COV: TSIBIRI
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Majalisar Kasa
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ba Zata Halarci Zaman Taron Sharm El-Sheikh Ba Saboda Wasu Dalilai Da Ta Byyana
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana dalilin da ya sa Iran ba za ta halarci taron na Sharm el-Sheikh ba
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana dangane da rashin halartar jamhuriyar Musulunci ta Iran zuwa taron na Sharm el-Sheikh cewa, ba za su iya tunkarar wadanda suka kaddamar da hare-haren wuce gona da iri kan al’ummar Iran da kuma ci gaba da yi musu barazana da kuma sanya musu takunkumi ba.
Araqchi ya rubuta a shafinsa na yanar gizo a dandalin X da sanyin safiyar yau litinin cewa: “Iran ta nuna matukar jin dadin ta ga gayyatar da shugaba Sisi ya yi wa Iran na halartar taron na Sharm el-Sheikh. Duk da Muradin Iran din na tattaunawa ta diflomasiyya, Araqchi ya ce shi ko shugaba Pezeshkian ba za su iya tunkarar wadanda suka kai wa al’ummar Iran hari da kuma ci gaba da yi mata barazana da kuma sanya mata takunkumi.”
Ya kara da cewa: Duk da haka, Iran tana maraba da duk wani shiri da zai kawo karshen kisan kiyashin da gwamnatin mamayar Isra’ila ke yi a Gaza da kuma bukatar kai wa ga janye sojojin mamaya daga yankin.
Araqchi ya jaddada cewa: Falasdinawa suna da ‘yancin fahimtar ainihin hakkinsu na cin gashin kansu, kuma dukkan kasashe, fiye da kowane lokaci, suna da alhakin taimaka musu tare da goyon bayan wannan bukata ta doka da ta dace.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gayyaci Mukaddashin Jakadan Kasar Oman Zuwa Ma’aikatar Harkokin Wajenta October 13, 2025 Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta October 13, 2025 Cibiyar Lafiya Ta Nasser Ta Ce: Yaran Gaza 5,500 Suna Bukatar Agajin Gaggawa A Kasashen Waje October 13, 2025 Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk October 13, 2025 Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza October 12, 2025 ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar October 12, 2025 Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice October 12, 2025 Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine October 12, 2025 Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara October 12, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon October 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci