2027: Atiku, Jonathan da Obi ba za su iya kayar da Tinubu ba — Kalu
Published: 8th, October 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Abiya, kuma Sanata mai wakiltar Abiyanta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne, zai sake lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Ya bayyana hakan a shirin siyasa na gidan talabijin na Channel a daren ranar Lraba.
An kashe ɗan shekara 13 da shanu 36 a wani sabon hari a Filato ’Yan sanda sun kama ɗan bindiga a kan iyakar Najeriya da KamaruKalu, ya ce babu wanda zai iya kayar da Tinubu a tsakanin Goodluck Jonathan, Atiku Abubakar, ko kuma Peter Obi.
Kalu, wanda ke ɗan jam’iyyar APC, ya ce gwamnatin Tinubu ta samu nasarori wajen farfaɗo da tattalin arziƙi.
A cewarsa, irin tagomashin da Tinubu ya shimfiɗa zai sa ’yan Najeriya su sake zaɓarsa a karo na biyu.
A gefe guda Kalu ya gargaɗi tsohon Shugaban ƘasaJonathan da kada ya tsaya takara, inda ya ce dokar ƙasa ta hana shi sake tsayawa takara.
Jonathan, ya shugabanci Najeriya daga shekarar 2010 zuwa 2015, bayan rasuwar tsohon shugaban ƙasa Umaru Musa Yar’Adua.
Wasu masana doka suna cewa kundin tsarin mulki bai ba shi damar sake tsayawa takara ba.
Kalaman Kalu na zuwa ne daidai lokacin da harkokin siyasar Najeriya suke ƙara ɗaukar zafi yayin da ake shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027.
Jam’iyyar APC mai mulki tana ƙoƙarin kare matsayinta, yayin da jam’iyyun adawa irin su PDP da LP da jam’iyyar haɗaka ADC ke ƙoƙarin farfaɗowa bayan shan kaye a zaɓen 2023.
A zaɓen 2023, Tinubu ya lashe shugaban ƙasa ƙarƙashin jam’iyyar APC, inda ya doke Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP.
Dukkaninsu sun soki sakamakon zaɓen ta hanyar kai ƙara kotu, amma Kotun Ƙoli ta tabbatar da nasarar Tinubu.
Yanzu ’yan Najeriya na jiran ganin ko jam’iyyun adawa za su iya haɗa kai don ƙalubalantar APC a 2027, ko kuma Tinubu da jam’iyyarsa za su yi nasara duk da matsalolin tattalin arziƙi da tsaro da ake fuskanta a ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
’Yan bindiga sun yi garkuwa da aƙalla mutum 11 mazauna garin Isapa da ke kusa da Eruku a Ƙaramar Hukumar Ekiti ta Jihar Kwara.
Harin ya faru ne sa’o’i kadan bayan sakin wasu masu ibada da aka yi garkuwa da su suna tsaka da ibada a coci.
An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a KebbiA cocin CAC da ke Ekuru, ana gudanar da bikin godiya domin murnar ’yantar da mambobi 18 da aka yi garkuwa da su kusan wata guda da ya gabata, sai ’yan bindiga suka kutsa suka yi garkuwa da mutum 38 bayan sun harbe uku har lahira.
Sabon harin, wanda ya faru da misalin ƙarfe 6:00 na yammacin Litinin, an ce ’yan bindiga kimanin 20 zuwa 30 ne suka kai shi.
Bayanai sun una cewa maharan su rika yin harbi ta ko’ina yayin da suke kutsa cikin garin, lamarin da ya sa mutane suka ranta a na kare.
Wata tsohuwa ta ji rauni sakamakon harbin kan mai uwa da wabi.
Wani jagoran al’umma da bai amince a bayyana sunansa ba, ya tabbatar da lamarin, inda ya ce: “Mutane 11 aka yi garkuwa da su, bakwai daga cikin su ’yan gida ɗaya. Waɗanda aka sace sun haɗa da mace mai juna biyu, masu shayarwa biyu da kuma kananan yara.”
Shaidar y ace sunaye mutanen sun hada da Talatu Kabiru, 20, Magaji, 6, Kande, 5, Hadiza, 10, Mariam, 6, Saima, 5, Habibat (mahaifiya), Fatima Yusufu (mahaifiya), Sarah Sunday, 22 (mai juna biyu), Lami Fidelis, 23 (uwa mai shayarwa) da kuma Haja Na Allah, ita ma uwa mai shayarwa.
Shaidun gani da ido sun ce ’yan bindigar sun bi wasu sassa na garin, inda suka bar alamun ramukan harsashin harbe-harbe a bangon gidaje da ƙofofi.
An gano harsashin bindiga AK-47 da aka harba daga wurare da dama bayan ’yan bindigar sun ja da baya tare da mutanen da suka yi garkuwa da su.
Lamarin ya haifar da tsananin tashin hankali a yankin da makotan garuruwa, yayin da jami’an tsaro da ’yan sa-kai ke ƙara ƙoƙari wajen gano maharan da ceto waɗanda aka sace.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kwara, Adekimi Ojo, ya tabbatar da lamarin ga yana mai cewa: “Eh, lamarin ya faru, amma ba zan iya cewa komai da yawa ba yanzu ba. Ina gab da shiga Isapa daga Ilorin. Zan ba da rahoto idan na isa.”
A yanzu haka dai Najeriya na fuskantar ɗaya daga cikin mafi munin matsalolin tsaro a tarihin ta. Hakan dai ya haifar da rufe makarantu da dama, musamman a Arewacin ƙasar.