Shugabar Cibiyar Nazarin Karatu da Ci Gaban Ilimi ta Najeriya (NCRRD) da ke Jami’ar Bayero Kano (BUK), Farfesa Amina Adamu, ta bayyana damuwa kan yadda dalibai ke ƙara gujewa amfani da dakunan karatu, tana danganta hakan da dogaro da kirkirarriyar fasaha ta AI. Da take jawabi a taron ƙasa da ƙasa karo na biyar kan nazarin karatu da nazari da aka gudanar a Jami’ar Bayero Kano, Farfesa Amina ta ce da dama daga cikin ɗalibai yanzu suna kammala karatun jami’a ba tare da sun taɓa shiga ɗakin karatu ko sau ɗaya ba.

Yadda zargin mallakar takardun bogi ya yi awon gaba da kujerar Ministan Tinubu Joash Amupitan na iya zama sabon shugaban INEC “Muna da daliban da ke yin rajista a shekarar farko kuma su kammala karatu ba tare da sun taɓa amfani da dakin karatu ko sau daya ba. Ba kamar da ba, lokacin da dalibai ke zuwa dakin karatu don neman bayanai da shiryawa jarrabawa, yanzu suna dogaro da fasajohin AI da sauran hanyoyin fasahar zamani,” in ji ta. Farfesa Amina ta yi gargadi cewa duk da amfanin da AI ke da shi, tana haifar da abin da ta kira “lalaci a fannin yin tunani” a tsakanin dalibai. “Suna saka duk aikin da aka ba su manhajar AI ta yi musu, sannan su miƙa amsar da suka samu ba tare da yin tunani da kansu ba. AI an ƙirƙire ta ne don taimakawa, ba don maye gurbin ƙirƙira da tunanin ɗan adam ba,” in ji ta. Ta bukaci malamai, iyaye da sauran masu ruwa da tsaki da su rungumi AI da kansu, sannan su koya wa dalibai yadda za su yi amfani da ita cikin hikima. “Ba za mu iya kawar da fuskarmu daga samuwar AI ba. Duniya na tafiya da ita, dole mu ma mu bi. Amma dole ne mu koya wa dalibai yadda za su yi amfani da AI ta hanyar haɗa amsoshin da ta bayar da nasu tunanin, ta hanyar yin nazari da zurfin tunani,” in ji ta. Shi kuwa a nasa jawabin, Shugaban Jami’ar BUK, Farfesa Haruna Musa, ya bayyana cewa jami’ar na shirin kafa cibiyar nazari kan AI da da fasahar mutum-mutumi, inda ya ce nan ba da jimawa ba za a fara koyar da darussa kan fasahar zamani a cikin kundin karatun jami’ar. “BUK ta shirya yin amfani da wannan fasaha don sauya tsarin karatu da bincike. Ba wai koyar da ita a matsayin darasi kaɗai ba, mun kuduri aniyar kafa cibiyar zamani ta AI da da fasahar mutum-mutumi. Taron yau ya nuna mana tasirin AI a fannin karatu, bincike da nazari,” in ji shi. Ya kuma bukaci malamai da su yi amfani da fasahar don sauya tsarin koyarwa da koyo a makarantunsu, da nufin inganta ilimi ga yara da al’umma gaba ɗaya. A jawabinsa na buɗe taro, Shugaban Hukumar Sadarwa ta Najeriya (NCC), Dr Aminu Maida, ya bayyana rawar da hukumar ke takawa wajen samar da kayan aiki da za su ba da damar amfani da AI a faɗin Najeriya. Dr Aminu, wanda, Daraktan Bincike da Ci Gaban Fasaha a hukumar, Ismail Adedigba, ya wakilta, ya ce NCC a matsayin hukumar gwamnati da ke kula da harkar sadarwa a Najeriya, ta ƙaddamar da cibiyoyin fasahar zamani a Kano da Lumu don samar da ingantaccen yanayi ga ci gaban AI. Ya bayyana cewa hukumar ta tallafa wa manyan makarantu guda shida da ayyukan binciken kan AI a shekarar 2024. Adedigba ya kuma jaddada muhimmancin amfani da tsare bayanan masu amfani da intanet, inda ya ce NCC tare da Hukumar Kare Bayanai ta Najeriya suna aiki tare don tabbatar da tsaron bayanai a cikin tsarin AI. Ya kuma ce shirin 3MTT na gwamnatin tarayya, wanda ke da nufin horar da ’yan Najeriya miliyan uku a muhimman fannonin fasaha ciki har da AI da tsaron intanet, tuni ya riga ya horar da sama da mutum 60,000 a cikin rukuni na farko, yayin da wasu rukunan ke tafe a nan gaba.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta

Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Dr Ali Larijan wanda ya ke ziyarar aiki na kwanaki uku a kasar Pakistan ya yabawa kasar saboda goyon bayan da ta bawa kasarsa a lokacin yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka dorawa kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Dr Ali Larijana yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Talata.  Sannan yace ya isar da sakon gaisuwa na Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khami’ae ga mutanen kasar Pakistan. Banda haka ya gana da Firai ministan kasar  Shehbaz Sharif da shugaban kasa Asif Ali Zardari da kuma kakakin majalisar dokokin kasar kasar Sardar Avaz Saadik.

A ganawar Larijani da Sharif sun tattauna kan dangantaka mai tsawo da ke tsakanin Iran da Pakisatan, da kuma bukatar a kara zurfafata.

Sharif a nasa bangaren ya bayyana cewa nan ba da dadewa waministan harkokin wajen kasar Mohammad Ishak Dar zai ziyarci Tehran inda ake saran zai rattaba hannu kan yarjeniyoyi na bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu, daga ciki har da batun kammala aikin shimfida bututun gas  daga kasar Iran zuwa Pakistan. Da kuma harkokin sadarwa.

A cikin wannan shekarar ne dai kasashen biyu suka rattaba hannu kan yarjeniyar bunkasa kasuwanci ta dalar Amurka billion 10 a tsakaninsu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru  Mafaka Ta Wucin Gadi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin November 25, 2025 An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila