Aminiya:
2025-10-13@13:35:11 GMT

Gwamnatin Gombe ta kafa hukumar bunkasa fasahar zamani da tattalin arziƙi

Published: 8th, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya sanya hannu kan dokar kafa Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arziki ta Zamani (GITDEC), domin bunƙasa ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaban tattalin arziƙin jihar.

Gwamnan ya ce kafa wannan hukuma wani muhimmin mataki ne da zai taimaka wajen sanya Gombe cikin jihohin da ke tafiya da zamani a ɓangaren fasaha.

’Yan bindiga sun sace shugaban malamai da wasu a Zamfara Yadda Obasanjo ya ƙaddamar da cibiyar taron ƙasa da ƙasa a Bauchi

“Ayyukan hukumar sun haɗa da samar da cibiyar ƙirƙire-ƙirƙire, bunƙasa fasahar zamani, koyar da dabarun zamani, da kuma aiwatar da ayyukan gwamnati ta yanar gizo,” in ji gwamnan.

Haka kuma hukumar za ta tallafa wa matasa da masu ƙirƙira, ta samu hannun jari a fannin fasaha, da kuma tabbatar da tsaron bayanan gwamnati.

Sakataren Gwamnatin Jihar Gombe, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya miƙa kwafin dokar da aka amince da ita ga Kwamishinan Kimiyya, Fasaha da Ƙirƙire-ƙirƙire, Farfesa Abdullahi Bappah Garkuwa, domin fara aiwatarwa.

Farfesa Garkuwa, ya ce kafa hukumar babbar nasara ce ga ci gaban fasaha a jihar, kuma za ta kawo ayyukan yi ga matasa, mata, da ’yan kasuwa.

Wannan ci gaba na zuwa ne a lokacin da Gwamnatin Gombe ke ƙara haɗa kai da hukumomin fasaha na cikin gida da na ƙasashen waje, irin su NITDA da Uniccon Group, domin ƙara inganta kayan aikin fasaha da horaswa a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tattalin Arziƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa

Kungiyar ‘Yan Dako ta kasa reshen jihar Jigawa ta kaddamar da Malam Muhammad Tajudeen Maigatari a matsayin sakataren kungiyar na jihar.

Da yake jawabin a lokacin bikin kaddamawar a garin Maigatari, Shugaban kungiyar na jihar Malam Nasiru Idris Sara, ya bayyana shugabanci a matsayin rikon amana a maimakon hanyar tara dukiya da alfahari, a don haka akwai bukatar sakataren ya yi aiki tukuru dan kare martabar sana’ar dako da masu yin ta.

Yana mai cewar shugabancin kungiyar zai hada kai da shugabannin kananan hukumomi da masu rike da sarautu da jami’an tsaro a matsayin abokan kawo cigaba wajen daga likkafar sana’ar dako.

Nasiru Idris Sara ya kuma yi kira ga daukacin ‘yan dako a fadin jihar da su yi rijista da kungiyar domin kasacewa a karkashin inuwa daya ta yadda za su ci moriyar tanade tanaden ta, sannan su kasance masu mutunta shugabanci da kuma bin doka da oda domin inganta rayuwar su.

Ya ce yayin da kungiyar ta ke da ‘yan dako kimanin dubu 20 a karkashin ta, akwai bukatar duk ‘yan dakon da ba su da katin zabe su karbi sabo ko kuma su sabunta wanda ya bata ko ya lalace domin amfani da damar su wajen zaben shugabanni.

A sakon sa, Hakimin Maigatari Alhaji Sani Alhassan Muhammad wanda ya sami wakilcin Sarkin Kasuwar Maigatari Alhaji Muhammadu Sarkin Kasuwa, ya bukaci sabon sakataren kungiyar Malam Muhammad Tajudeen ya kasance mai nuna gaskiya da adalci wajen huldar sa da ‘yan dako da sauran masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci, inda ya bayyana murnar samun wannan mukamin.

Cikin wadanda suka halarci taron sun hada da Sarkin hatsin Maigatari, Malam Mu’azu Bako da Shugaban leburorin Dingas na Jamhuriyar Nijar Malam Lawwali Hassan.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano
  • Ɗan Majalisa ya nemi ɗaukar mataki kan dorinar ruwa a Gombe