Gwamnatin Gombe ta kafa hukumar bunkasa fasahar zamani da tattalin arziƙi
Published: 8th, October 2025 GMT
Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya sanya hannu kan dokar kafa Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arziki ta Zamani (GITDEC), domin bunƙasa ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaban tattalin arziƙin jihar.
Gwamnan ya ce kafa wannan hukuma wani muhimmin mataki ne da zai taimaka wajen sanya Gombe cikin jihohin da ke tafiya da zamani a ɓangaren fasaha.
“Ayyukan hukumar sun haɗa da samar da cibiyar ƙirƙire-ƙirƙire, bunƙasa fasahar zamani, koyar da dabarun zamani, da kuma aiwatar da ayyukan gwamnati ta yanar gizo,” in ji gwamnan.
Haka kuma hukumar za ta tallafa wa matasa da masu ƙirƙira, ta samu hannun jari a fannin fasaha, da kuma tabbatar da tsaron bayanan gwamnati.
Sakataren Gwamnatin Jihar Gombe, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya miƙa kwafin dokar da aka amince da ita ga Kwamishinan Kimiyya, Fasaha da Ƙirƙire-ƙirƙire, Farfesa Abdullahi Bappah Garkuwa, domin fara aiwatarwa.
Farfesa Garkuwa, ya ce kafa hukumar babbar nasara ce ga ci gaban fasaha a jihar, kuma za ta kawo ayyukan yi ga matasa, mata, da ’yan kasuwa.
Wannan ci gaba na zuwa ne a lokacin da Gwamnatin Gombe ke ƙara haɗa kai da hukumomin fasaha na cikin gida da na ƙasashen waje, irin su NITDA da Uniccon Group, domin ƙara inganta kayan aikin fasaha da horaswa a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Tattalin Arziƙi
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
Jami’an tsaro a Jihar Kaduna, sun fara gudanar da babban samame domin kawar da ’yan ta’adda da ’yan bindiga a wasu ƙananan hukumomin jihar.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce an gudanar da aikin tare haɗin gwiwar sojoji, DSS, NSCDC, KADVS, da kuma ƙungiyoyin sa-kai da mafarauta.
Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000Aikin ya shafi ƙananan hukumomin Makarfi, Hunkuyi da Ikara.
Rundunar ta ce manufar wannan samame shi ne “share dukkanin maɓoyar miyagu, rushe sansanonin da suka kafa, da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.”
Wannan mataki ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, wanda ya umarci dukkanin rundunonin ’yan sanda a faɗin ƙasar nan su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da aikata laifuka.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Rabiu Muhammad, ya tabbatar wa jama’a cewa jami’an tsaro za su ci gaba da matsa wa miyagu lamba.
Ya ce za su ci gaba da yin gwiwa da rundunonin tsaro domin tabbatar da tsaro a jihar.