Aminiya:
2025-11-27@21:56:08 GMT

Gwamnatin Gombe ta kafa hukumar bunkasa fasahar zamani da tattalin arziƙi

Published: 8th, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya sanya hannu kan dokar kafa Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arziki ta Zamani (GITDEC), domin bunƙasa ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaban tattalin arziƙin jihar.

Gwamnan ya ce kafa wannan hukuma wani muhimmin mataki ne da zai taimaka wajen sanya Gombe cikin jihohin da ke tafiya da zamani a ɓangaren fasaha.

’Yan bindiga sun sace shugaban malamai da wasu a Zamfara Yadda Obasanjo ya ƙaddamar da cibiyar taron ƙasa da ƙasa a Bauchi

“Ayyukan hukumar sun haɗa da samar da cibiyar ƙirƙire-ƙirƙire, bunƙasa fasahar zamani, koyar da dabarun zamani, da kuma aiwatar da ayyukan gwamnati ta yanar gizo,” in ji gwamnan.

Haka kuma hukumar za ta tallafa wa matasa da masu ƙirƙira, ta samu hannun jari a fannin fasaha, da kuma tabbatar da tsaron bayanan gwamnati.

Sakataren Gwamnatin Jihar Gombe, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya miƙa kwafin dokar da aka amince da ita ga Kwamishinan Kimiyya, Fasaha da Ƙirƙire-ƙirƙire, Farfesa Abdullahi Bappah Garkuwa, domin fara aiwatarwa.

Farfesa Garkuwa, ya ce kafa hukumar babbar nasara ce ga ci gaban fasaha a jihar, kuma za ta kawo ayyukan yi ga matasa, mata, da ’yan kasuwa.

Wannan ci gaba na zuwa ne a lokacin da Gwamnatin Gombe ke ƙara haɗa kai da hukumomin fasaha na cikin gida da na ƙasashen waje, irin su NITDA da Uniccon Group, domin ƙara inganta kayan aikin fasaha da horaswa a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tattalin Arziƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna

Jami’an tsaro a Jihar Kaduna, sun fara gudanar da babban samame domin kawar da ’yan ta’adda da ’yan bindiga a wasu ƙananan hukumomin jihar.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce an gudanar da aikin tare haɗin gwiwar sojoji, DSS, NSCDC, KADVS, da kuma ƙungiyoyin sa-kai da mafarauta.

Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000

Aikin ya shafi ƙananan hukumomin Makarfi, Hunkuyi da Ikara.

Rundunar ta ce manufar wannan samame shi ne “share dukkanin maɓoyar miyagu, rushe sansanonin da suka kafa, da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.”

Wannan mataki ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, wanda ya umarci dukkanin rundunonin ’yan sanda a faɗin ƙasar nan su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da aikata laifuka.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Rabiu Muhammad, ya tabbatar wa jama’a cewa jami’an tsaro za su ci gaba da matsa wa miyagu lamba.

Ya ce za su ci gaba da yin gwiwa da rundunonin tsaro domin tabbatar da tsaro a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe
  • Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi