Aminiya:
2025-11-27@21:48:29 GMT

Yadda Obasanjo ya ƙaddamar da cibiyar taron ƙasa da ƙasa a Bauchi

Published: 8th, October 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya ƙaddamar da sabon ginin Cibiyar Taron Ƙasa da Ƙasa, wadda aka sanya wa sunan Sir Ahmadu Bello a Jihar Bauchi.

An ƙaddamar da cibiyar ne kafin babban taron zuba jari da nufin bunkasa kasuwanci da masana’antu a jihar.

Ban yi murabus don ina da laifi ba — Nnaji Kamfanonin rarraba lantarki sun tafka asarar biliyan 358 a cikin wata uku – NERC

A jawabinsa, Obasanjo ya yaba wa Gwamna Bala Mohammed, bisa irin ayyukan raya ƙasa da yake aiwatarwa, waɗanda ke inganta rayuwar jama’a.

“Na yi farin ciki da abin da na gani da kuma abin da na ji. Ban zata cewa zan dawo Bauchi cikin ƙanƙanin lokaci don buɗe irin wannan katafaren waje ba,” in ji tsohon shugaban.

Obasanjo, ya ce cibiyar alama ce ta ci gaba da hangen nesa, wacce za ta taimaka wajen ƙarfafa alaƙa tsakanin Bauchi da sauran sassan duniya.

Ya kuma jaddada cewa babu wata ƙasa da za ta ci gaba ba tare da hulɗa da sauran ƙasashen duniya ba.

Ya bayyana cewa irin wannan gini zai bai wa jihar damar karɓar taruka na ƙasa da ƙasa da kuma janyo hankalin masu zuba jari, wanda hakan zai ƙara bunƙasa tattalin arziƙin Bauchi.

“Idan aka ci gaba da gina wuraren da ke bunƙasa haɗin kai da tattalin arziƙi irin wannan, Najeriya za ta ci gaba da taka rawar gani a fannin ci gaban duniya,” in ji Obasanjo.

A nasa ɓangaren, Gwamna Bala Mohammed, ya gode wa tsohon shugaban ƙasar saboda goyon bayansa, tare da tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da jajircewa wajen bunƙasa ilimi, yawon buɗe ido da ci gaban tattalin arziƙi a jihar.

Ya ce cibiyar za ta zama wajen gudanar da taurkan ilimi, kasuwanci, al’adu da hulɗa tsakanin gida da waje, sannan ta zama shaida ga manufofin gwamnatinsa na mayar da Bauchi cibiyar zuba jari a Arewacin Najeriya.

Wannan katafaren gini na ɗauke da ɗakunan taro daban-daban da aka sanya sunayen tsofaffin gwamnonin Jihar Bauchi.

 

Ga hotunan yadda taron ya gudana:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Cibiya Ƙaddamar Da Aiki taro

এছাড়াও পড়ুন:

An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya

Sufeto Janar na ’Yan sandan Nijeriya, Olukayode Egbetokun, ya sanar da cewa sun aiwatar da umarnin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na janye dakarunsu daga gadin ɗaiɗaikun mutane da ake kira VIP.

IG Egbetokun ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai a yau Alhamis, yana mai cewa zuwa yanzu sun janye dakaru 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya.

Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da Olympiacos An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji

“Wannan karon za mu aiwatar da umarnin da kyau saboda umarnin shugaban ƙasa ne,” in ji shi.

“Babu wani gwamna, ko minista, ko abokaina da za su kira su takura min saboda sun san cewa umarnin shugaban ƙasa ne. Ina kuma da tabbacin cewa ba za su uzzura wa kwamashinonin ’yan sanda ba ma.”

Ya ƙara da cewa za su tura jami’an da aka janye zuwa “wuraren da aka fi buƙatarsu, musamman a wannan lokaci mai muhimmanci.”

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da aika ’yan sanda ga manyan mutane domin ba su tsaro na musamman, yana mai mayar da su zuwa aikin tsaro da ya shafi al’umma baki ɗaya.

Kazalila, a ranar Laraba, 26 ga watan Nuwamba ne Tinubun ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a faɗin ƙasar, inda ya bayar da umarnin a ɗauki matakan gaggawa domin magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.

Shugaban ya ce a ɗauki sababbin ’yan sanda 20,000, ƙari a kan guda 30,000 da ya fara amincewa a ɗauk, wanda za a yi amfani da sansanonin horar da masu yi wa ƙasa hidima wajen horar da sababbin ’yan sandan da za a ɗauka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • Najeriya : Ana ci gaba da alhinin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • Ramaphosa ya soki kalaman Trump na cewa ba zai gayyaci shi a taron G20
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa