Yadda Obasanjo ya ƙaddamar da cibiyar taron ƙasa da ƙasa a Bauchi
Published: 8th, October 2025 GMT
Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya ƙaddamar da sabon ginin Cibiyar Taron Ƙasa da Ƙasa, wadda aka sanya wa sunan Sir Ahmadu Bello a Jihar Bauchi.
An ƙaddamar da cibiyar ne kafin babban taron zuba jari da nufin bunkasa kasuwanci da masana’antu a jihar.
Ban yi murabus don ina da laifi ba — Nnaji Kamfanonin rarraba lantarki sun tafka asarar biliyan 358 a cikin wata uku – NERCA jawabinsa, Obasanjo ya yaba wa Gwamna Bala Mohammed, bisa irin ayyukan raya ƙasa da yake aiwatarwa, waɗanda ke inganta rayuwar jama’a.
“Na yi farin ciki da abin da na gani da kuma abin da na ji. Ban zata cewa zan dawo Bauchi cikin ƙanƙanin lokaci don buɗe irin wannan katafaren waje ba,” in ji tsohon shugaban.
Obasanjo, ya ce cibiyar alama ce ta ci gaba da hangen nesa, wacce za ta taimaka wajen ƙarfafa alaƙa tsakanin Bauchi da sauran sassan duniya.
Ya kuma jaddada cewa babu wata ƙasa da za ta ci gaba ba tare da hulɗa da sauran ƙasashen duniya ba.
Ya bayyana cewa irin wannan gini zai bai wa jihar damar karɓar taruka na ƙasa da ƙasa da kuma janyo hankalin masu zuba jari, wanda hakan zai ƙara bunƙasa tattalin arziƙin Bauchi.
“Idan aka ci gaba da gina wuraren da ke bunƙasa haɗin kai da tattalin arziƙi irin wannan, Najeriya za ta ci gaba da taka rawar gani a fannin ci gaban duniya,” in ji Obasanjo.
A nasa ɓangaren, Gwamna Bala Mohammed, ya gode wa tsohon shugaban ƙasar saboda goyon bayansa, tare da tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da jajircewa wajen bunƙasa ilimi, yawon buɗe ido da ci gaban tattalin arziƙi a jihar.
Ya ce cibiyar za ta zama wajen gudanar da taurkan ilimi, kasuwanci, al’adu da hulɗa tsakanin gida da waje, sannan ta zama shaida ga manufofin gwamnatinsa na mayar da Bauchi cibiyar zuba jari a Arewacin Najeriya.
Wannan katafaren gini na ɗauke da ɗakunan taro daban-daban da aka sanya sunayen tsofaffin gwamnonin Jihar Bauchi.
Ga hotunan yadda taron ya gudana:
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Cibiya Ƙaddamar Da Aiki taro
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna
Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa wannan titin ba na yankin Arewa kadai ba ne, ya bayyana shi a matsayin jijiyar ƙasa da ƙasa ne wadda ke haɗa yankuna daban-daban tare da ƙarfafa haɗin kai da bunƙasar tattalin arziki.
Ya kara da cewa titin Abuja- Kaduna da Kano na ɗaya daga cikin manyan ayyukan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ƙarƙashin Manufar Sabon Fata na (Renewed Hope Agenda), wadda ke nufin sabunta manyan gine-ginen ƙasa da inganta tattalin arziki.
Yace “Wannan titi ba hanya ce kawai ba inda yace wata hanya ce ta tattalin arziki wadda ke haɗa mutane, kasuwanni, da dama a fadin Arewacin Nijeriya da ma bayan haka,”
A nasa jawabin, Sanata Umahi ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa yadda yake kaiwa da komowa domin kare muradun al’ummar Kaduna, tare da tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta kuduri aniyar kammala aikin cikin lokaci. Ya bayyana cewa an umarci kamfanonin da ke aikin da su rika aiki sau biyu a rana domin hanzarta cigaba ba tare da rage inganci ba.
Ministan ya kara da cewa amfani da fasahar siminti mai ɗorewa wanda zai tabbatar da cewa titin zai dawwama tare da rage kudin gyara nan gaba.
Kamfanonin da ke aikin sun yi alkawarin ƙara gaggautawa musamman a yankin Jere dake jihar Kaduna, inda ake sa ido sosai kan ci gaban aiki. Gwamnatin Jihar Kaduna ta kuma tabbatar da ci gaba da haɗin kai da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya domin magance ƙalubalen da ke iya janyo tsaiko.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA