Aminiya:
2025-11-27@18:38:21 GMT

Yadda zargin mallakar takardun bogi ya yi awon gaba da kujerar Ministan Tinubu

Published: 8th, October 2025 GMT

Uche Nnaji, Ministan Ƙirƙira, Kimiyya da Fasaha, ya yi murabus daga mukaminsa.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar da yammacin ranar Talata.

Joash Amupitan na iya zama sabon shugaban INEC Jerin ministocin da zargin takardun bogi ya tabaibaye su

Nnaji na fuskantar zarge-zarge kan sahihancin takardun karatunsa, inda binciken da jaridar Premium Times ta gudanar ya gano cewa Jami’ar Najeriya da ke Nsukka (UNN) ta ce ba ta ba shi takardar kammala digiri ba.

A cewar jami’ar, tsohon Ministan bai kammala karatunsa a cikinta ba, kuma ba ta taɓa ba shi takardar shaidar kammala ta ba.

A cewar jaridar, Simon U. Ortuanya, Shugaban Jami’ar UNN, ya bayyana cewa duk da cewa an ɗauki Nnaji a jami’ar a shekarar 1981, bai kammala karatunsa ba kuma ba a ba shi takardar kammalawa ba.

Haka kuma, jaridar ta ƙara da cewa Hukumar Kula da Matasa Masu yi wa Ƙasa Hidima (NYSC) ta tabbatar cewa takardar shaidar hidimar ƙasa da Nnaji ke nunawa ta bog ice a wajen hukumar, kuma ba za a iya tabbatar da sahihancinta ba.

A cikin sanarwarsa, Onanuga ya tabbatar da cewa Nnaji ya sauka daga mukamin minister kuma mamba a Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC).

Ya ce Shugaba Bola Tinubu ya amince da murabus ɗin ministan kuma ya yi masa fatan alheri.

“Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da murabus ɗin Geoffrey Uche Nnaji, Ministan Ƙirƙira, Kimiyya da Fasaha, sakamakon wasu zarge-zarge da ake yi masa.”

“Shugaba Tinubu ne ya naɗa Nnaji a watan Agustan 2023. Ya yi murabus yau ta hanyar rubuta wasiƙa yana gode wa Shugaban Ƙasa da ya ba shi damar yin wa ƙasa hidima.”

“Nnaji ya ce ya kasance wanda abokan ahamayyar siyasa ke yi wa bita-da-kulli.”

“Shugaba Tinubu ya gode masa bisa gudunmawar da ya bayar, kuma ya yi masa fatan alheri a duk inda ya dosa,” in ji sanarwar Onanuga.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Takardun bogi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya kaddamar da titi mai tsawon kilomita 13 da rabi, da ya tashi daga Sada zuwa Danakari zuwa Unguwar Malam Kuda, zuwa Magina, a Karamar Hukumar Yankwashi ta jihar.

A  jawabinsa wajen bikin kaddamarwar, Namadi ya bayyana kudirin gwamnatinsa na ci gaba da samar da muhimman abubuwan more rayuwa a karkara domin inganta harkokin tattalin arzikinsu.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa Gwamna Umar Namadi ya ce titin, wanda aka gina akan kudi Naira biliyan 1 da miliyan 690, na daga cikin manyan ayyukan gine-ginen hanyoyi 48 da gwamnatinsa ta bayar a shekarar 2024.

A cewarsa, titin zai hada al’ummomin karkara na Sada, Danakari, Unguwar Malam Kuda da Magina.

 

Ya jaddada cewa mutanen wadannan yankuna sun daɗe suna bukatar wannan aiki na hanyar.

Malam Umar Namadi ya ce titin zai ba su damar kai amfanin gonakinsu kasuwanni mafi kusa cikin sauki.

Ya kuma ce yawancin wadannan hanyoyi sun kai matakin kammaluwa, kuma nan ba da dadewa ba za a gudanar da jerin bukukuwan kaddamar da su gaba daya.

Ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da hanyoyin sufuri a karkara domin saukaka samun hanyoyin shiga kasuwanni da birane.

Namadi ya bayyana cewa shirin tuntubar jama’a ya bai wa al’umma damar tattaunawa kai tsaye da gwamnati.

Tun da farko, Kwamishinan Ayyuka da Sufuri na jihar, Injiniya Gambo Malam, ya ce titin na daga cikin hanyoyi 48 masu dauke da jimillar tsawon kilomita 977 da aka bayar a 2024 a kan kudi Naira biliyan 304.

Wasu daga cikin mazauna yankin, Malam Abdullahi Musa da Malam Muhammad Gata, sun yaba wa gwamnatin jihar bisa wannan aiki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • ’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi