Aminiya:
2025-10-13@13:35:13 GMT

Matar aure mai ’ya’ya huɗu ta rataye kanta a Jigawa

Published: 8th, October 2025 GMT

Al’umma a kauyen Sumore da ke Ƙaramar Hukumar Dutse a Jihar Jigawa sun shiga cikin alhini bayan mutuwar wata mata mai shekaru 30, Adama Hannafi, wacce ake zargin ta rataye kanta.

Lamarin, wanda ya faru a ranar Talata, ya tayar da hankulan mazauna kan ƙalubalen da ke tattare da rashin lafiyar kwakwalwa a cikin al’umma, musamman a yankunan karkara.

‘Akwai ɗaliban da ke yin digiri yanzu ba tare da sun taɓa shiga ɗakin karatu ba saboda AI’ Joash Amupitan na iya zama sabon shugaban INEC

Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, SP Lawan Shi’isu Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an samu gawar matar a rataye a jikin wata bishiya a kauyen.

“Mun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3:00 na rana, kuma jami’anmu daga sashen Yalwawa sun garzaya wurin. Da suka isa, sun tarar da gawar matar a rataye,” in ji shi.

Shi’isu ya ƙara da cewa an kai gawar zuwa Asibitin Gwamnati na Dutse, inda likita ya tabbatar da mutuwarta.

Duk da cewa ba a samu cikakken bayani kan lamarin ba, majiyoyi sun ce marigayiyar ta dade tana fama da matsalar kwakwalwa kafin rasuwarta.

Da yake tsokaci a kan lamarin, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar ta Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici, yana mai kira ga al’umma da su ƙara wayar da kai kan batun lafiyar kwakwalwa.

“Muna roƙon iyalai da maƙwabta da su nuna kulawa ga duk wanda ke nuna alamun damuwa ko canjin hali. Neman taimakon likita da na ƙwararru da wuri na iya ceton rayuka,” in ji shi.

Kwamishinan ya kuma buƙaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani hali da ba a saba gani ba ga ofishin ’yan sanda mafi kusa ko cibiyar lafiya domin a samu matakin gaggawa.

Marigayiya Adama ta rasu ta bar mijinta da ’ya’ya hudu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jigawa Rataya

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa

Kungiyar ‘Yan Dako ta kasa reshen jihar Jigawa ta kaddamar da Malam Muhammad Tajudeen Maigatari a matsayin sakataren kungiyar na jihar.

Da yake jawabin a lokacin bikin kaddamawar a garin Maigatari, Shugaban kungiyar na jihar Malam Nasiru Idris Sara, ya bayyana shugabanci a matsayin rikon amana a maimakon hanyar tara dukiya da alfahari, a don haka akwai bukatar sakataren ya yi aiki tukuru dan kare martabar sana’ar dako da masu yin ta.

Yana mai cewar shugabancin kungiyar zai hada kai da shugabannin kananan hukumomi da masu rike da sarautu da jami’an tsaro a matsayin abokan kawo cigaba wajen daga likkafar sana’ar dako.

Nasiru Idris Sara ya kuma yi kira ga daukacin ‘yan dako a fadin jihar da su yi rijista da kungiyar domin kasacewa a karkashin inuwa daya ta yadda za su ci moriyar tanade tanaden ta, sannan su kasance masu mutunta shugabanci da kuma bin doka da oda domin inganta rayuwar su.

Ya ce yayin da kungiyar ta ke da ‘yan dako kimanin dubu 20 a karkashin ta, akwai bukatar duk ‘yan dakon da ba su da katin zabe su karbi sabo ko kuma su sabunta wanda ya bata ko ya lalace domin amfani da damar su wajen zaben shugabanni.

A sakon sa, Hakimin Maigatari Alhaji Sani Alhassan Muhammad wanda ya sami wakilcin Sarkin Kasuwar Maigatari Alhaji Muhammadu Sarkin Kasuwa, ya bukaci sabon sakataren kungiyar Malam Muhammad Tajudeen ya kasance mai nuna gaskiya da adalci wajen huldar sa da ‘yan dako da sauran masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci, inda ya bayyana murnar samun wannan mukamin.

Cikin wadanda suka halarci taron sun hada da Sarkin hatsin Maigatari, Malam Mu’azu Bako da Shugaban leburorin Dingas na Jamhuriyar Nijar Malam Lawwali Hassan.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
  • China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100%
  • Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola