Aminiya:
2025-11-27@21:37:22 GMT

Matar aure mai ’ya’ya huɗu ta rataye kanta a Jigawa

Published: 8th, October 2025 GMT

Al’umma a kauyen Sumore da ke Ƙaramar Hukumar Dutse a Jihar Jigawa sun shiga cikin alhini bayan mutuwar wata mata mai shekaru 30, Adama Hannafi, wacce ake zargin ta rataye kanta.

Lamarin, wanda ya faru a ranar Talata, ya tayar da hankulan mazauna kan ƙalubalen da ke tattare da rashin lafiyar kwakwalwa a cikin al’umma, musamman a yankunan karkara.

‘Akwai ɗaliban da ke yin digiri yanzu ba tare da sun taɓa shiga ɗakin karatu ba saboda AI’ Joash Amupitan na iya zama sabon shugaban INEC

Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, SP Lawan Shi’isu Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an samu gawar matar a rataye a jikin wata bishiya a kauyen.

“Mun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3:00 na rana, kuma jami’anmu daga sashen Yalwawa sun garzaya wurin. Da suka isa, sun tarar da gawar matar a rataye,” in ji shi.

Shi’isu ya ƙara da cewa an kai gawar zuwa Asibitin Gwamnati na Dutse, inda likita ya tabbatar da mutuwarta.

Duk da cewa ba a samu cikakken bayani kan lamarin ba, majiyoyi sun ce marigayiyar ta dade tana fama da matsalar kwakwalwa kafin rasuwarta.

Da yake tsokaci a kan lamarin, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar ta Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici, yana mai kira ga al’umma da su ƙara wayar da kai kan batun lafiyar kwakwalwa.

“Muna roƙon iyalai da maƙwabta da su nuna kulawa ga duk wanda ke nuna alamun damuwa ko canjin hali. Neman taimakon likita da na ƙwararru da wuri na iya ceton rayuka,” in ji shi.

Kwamishinan ya kuma buƙaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani hali da ba a saba gani ba ga ofishin ’yan sanda mafi kusa ko cibiyar lafiya domin a samu matakin gaggawa.

Marigayiya Adama ta rasu ta bar mijinta da ’ya’ya hudu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jigawa Rataya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano

Rahotanni na cewa ’yan bindiga sun sace wasu mutum takwas a garin Biresawa da ke Karamar Hukumar Tsanyawa ta Jihar Kano a daren jiya na Litinin.

Wata majiyar da ta tabbatar da lamarin ta shaida wa Aminiya cewa maharan sun shiga garin tsakanin 11 na dare zuwa 12 na tsakar dare, inda suka yi awon gaba da maza biyu da mata shida.

’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai

Wani ɗan uwa ga waɗanda aka sace, Kabiru Usman, ya ce maharan sun zo ne a ƙafa ɗauke da makamai, suka kuma yi garkuwa da matarsa Umma, ɗiyarsa mai shekara 17, da matar ɗan’uwansa da wasu mata biyu daga Tsundu mai makwabtaka.

Ya ce al’ummar garin sun yi ƙoƙarin daƙile harin amma suka kasa saboda ƙarancin makamai, duk da cewa sun sanar da ’yan sanda da sojoji tun kafin faruwar harin bayan samun bayanan cewa ’yan bindigar na dosar yankin.

Ya roƙi gwamnati ta ɗauki mataki wajen ceto mutanen da aka sace da kuma kare rayukan mazauna yankin.

Aminiya ta yi ƙoƙarin ji ta bakin Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa, sai da har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja