Wata Kotun Majistare da ke Kano ta bayar da umarnin a tura Ashiru Idris, wanda aka fi sani da Mai Wushirya, gidan gyaran hali na tsawon mako biyu saboda wallafa bidiyon batsa da ya shafi budurwa (dwarf) da ba a bayyana sunanta ba, a dandalin sada zumunta.

Mai shari’a Halima Wali ta Kotun Majistare mai lamba 7 ce ta bayar da wannan umarni, tana mai cewa a ci gaba da tsare shi a gidan gyaran hali kafin a dawo da ƙarar don ci gaba da sauraro.

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da MutunciSin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Hukumar kula finafinai da ɗab’i ta jihar Kano ce ta kama Mai Wushirya makon da ya gabata bayan da wasu bidiyoyi na rashin kunya suka yaɗu a intanet, inda aka gan shi ba tare da riga ba yana aikata abin da hukumomi suka bayyana a matsayin “abin kunya da rashin mutunci.”

Mai magana da yawun hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya ce kotu ta umarci a kawo matar da ta fito a cikin bidiyon kafin a ci gaba da shari’ar, yana mai bayyana cewa hukumar ta samu rahoton cewa matar ta gudu zuwa Jihar Zamfara, amma ana ci gaba da ƙoƙarin dawo da ita zuwa Kano domin ta fuskanci shari’a tare da Mai Wushirya.

Tags: 'Yan Matan tiktokMai wushiryaTikTokShareTweetSendShare Abubakar Sulaiman

Related NishadiAn Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana 2 days agoNishadiDaga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa 1 week agoNishadiBabu Wanda Ya Jawo Ra’ayina  Zuwa Masana’antar Kannywood —Umar Hassan (2) 2 weeks ago

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Matan tiktok Mai wushirya

এছাড়াও পড়ুন:

Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan yadda shugaba Bola Tinubu ya yi wa wasu mutane afuwa, ciki har da waɗanda suka aikata manyan laifuka.

A cikin saƙon da Atiku ya wallafa a shafinsa na X, ya ce ana yin afuwa ne ga waɗanda aka yi wa rashin adalci ko waɗanda suka nema gafara bayan sun shafe wani lokaci a gidan yari.

Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna

Ya ce a wannan karon an yi wa masu safarar ƙwayoyi, masu garkuwa da mutane, masu kisan kai, da kuma masu cin hanci da rashawa afuwa.

Atiku, ya ce abin mamaki ne yadda gwamnati ke yafewa irin waɗannan mutane, a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsaro da lalacewar tarbiyya, musamman tsakanin matasa masu shan miyagun ƙwayoyi.

Ya ce bincike ya nuna cewa kashi 29 na waɗanda aka yi wa afuwa suna da alaƙa da hakrar miyagun ƙwayoyi, yayin da Najeriya ke ƙoƙarin wanke sunanta a idon duniya kan yaƙi da miyagun ƙwayoyi.

Atiku, ya ce maimakon wannan afuwa ta zama darasi ga masu laifi, ta zama hanyar durƙusa da ɓangaren shari’a da jami’an tsaro da ke sadaukar da rayukansu wajen kamawa da hukunta masu aikata laifuka.

Ya ƙara da cewa idan gwamnati ta fara yafe wa masu laifi, hakan zai rage ƙimar shugabanci kuma ya ƙarfafa wa masu aikata laifuka su ci gaba da aikata su.

Atiku ya jaddada cewa Najeriya tana buƙatar  shugabanci na gari wanda zai tabbatar da adalci a shari’a, ba tare da nuna bambanci ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano
  • Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya