Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-13@17:47:12 GMT

Sardaunan Ikulu Ya Nemi Matasa da Mata su Shiga Siyasa Cikakke

Published: 6th, October 2025 GMT

Sardaunan Ikulu Ya Nemi Matasa da Mata su Shiga Siyasa Cikakke

Daga Abdullahi Usman, Kaduna

Sardaunan Ikulu, Alhaji Dr. Isma’īl Yusuf Ashafa, ya kira mata da matasa a garin Ikulu da su shiga harkokin siyasa domin kawo ci gaba a yankinsu.

Ya fadi hakan ne a lokacin Taron Ikulu da aka shirya a Kaduna karkashin jagorancin Ikulu Political Forum (IPF). Ya jaddada cewa babu wata al’umma da za ta bunkasa sai an samu hadin kai tsakanin jama’a da kuma cikakkiyar rawar da matasa da mata ke takawa a siyasa.

Ya kara da cewa wajibi ne a wayar da kan matasa da mata, a ilimantar da su, sannan a motsa su su gane muhimmancin jagoranci ta hanyar jam’iyyun siyasa. Hakazalika, ya gargadi ‘yan siyasa a yankin da su guji “siyasar do ko mutu,” domin tabbatar da ci gaba da zaman lafiya a yankin.

Ya ce, soyayya, kishin ƙasa, da burin zaman lafiya ya kamata su kasance ginshiƙan jama’ar Ikulu.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Ci Gaban Ikulu (Ikulu Development Association – IDA), Mista Bature S. Likoro, ya jaddada muhimmancin zaman lafiya da ɗorewar haɗin kai a ƙasar Ikulu, tare da kiran shugabanni su mai da hankali kan ci gaban matasa da mata.

Sarauniyar Ikulu, Mrs. Lorentia Bature, ta bayyana cewa idan mata suka nesanta kansu daga siyasa, al’umma ba za ta ci gaba ba. Ta yabawa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, saboda ayyukan ci gaba da yake aiwatarwa, tare da godewa Sardaunan Ikulu, Dr. Isma’īl Yusuf Ashafa, saboda jajircewarsa wajen tallafawa jama’arsa.

Comrade Moses Obadiah, Shugaban Kwamitin Shirya Taro, ya gargadi ‘yan siyasa da su guji siyasar addini, kabilanci da son kai, domin wadannan abubuwa suna haifar da rabuwar kai da koma-baya. Ya bayyana cewa Ikulu Youths Political Forum ta kafa haɗin kai da jam’iyyun siyasa domin inganta dimokuradiyya mai zaman lafiya.

Shugaban Ikulu Youths Political Forum, Mista Mathew Makama, ya bayyana cewa ƙasar Ikulu tana da mutanen kirki, masu gaskiya da kwazo, waɗanda ke son haɗin kai da gaskiya. Ya jaddada cewa zaman lafiya shi ne ginshiƙin ci gaban al’umma.

Mrs. Martina Sunday, shugabar mata, ta ƙarfafa mata da su yi sana’o’in halal domin dogaro da kai. Ta kuma yabawa Ikulu Youths Political Forum saboda ƙoƙarinsu na bunƙasa zaman lafiya da haɗin kai.

Honourable Justina Joseph Usman, Kansilan Ikulu Ward a karamar hukumar Zangon Kataf, ta gode wa Gwamna Uba Sani saboda ƙoƙarinsa na haɗa kan al’umma, tare da bayyana fatan cewa taron zai ƙara ɗaure zumunci da kawo ci gaba a yankin.

Mista Destiny Madaki, jami’i a Ikulu Political Forum, ya ce taron an shirya shi ne domin haɗa ‘ya’yan ƙasar Ikulu don ci gaban al’umma.

Mrs. Asabaru Yaro, memba a Kwamitin Amintattu na Ikulu Development Association, ta bukaci mata su ci gaba da kasancewa masu haɗin kai da tallafawa juna, sannan ta roƙi matasa su kasance masu zaman lafiya, haƙuri da fahimta domin ƙara ɗaukaka yankin.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sardauna zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa: Iran tana goyon bayan duk wani Shirin zaman lafiya da ya hada da dakatar da kisan kiyashi a Gaza

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta tabbatar da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana goyon bayan duk wani mataki ko wani yunkuri da ya hada da kawo karshen yakin kisan kiyashi a Gaza, janyewar sojojin mamayar Isra’ila, shigar da kayan agajin jin kai, sakin fursunonin Falastinawa, da kuma tabbatar da dukkanin hakkokin Falasdinawa.

Haka kuma ta kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran a matsayinta na mai goyon bayan halastacciyar gwagwarmayar al’ummar Falastinu samun tabbatar da ‘yancin kai, ta yi amfani da dukkanin karfinta na diflomasiyya a cikin shekaru biyun da suka gabata, musamman a matakin yanki, kungiyar hadin kan kasashen musulmi, da Majalisar Dinkin Duniya, wajen matsin lamba ga yahudawan sahayoniyya da magoya bayansu da su dakatar da kisan kiyashi da kuma janyewar ‘yan mamaya daga Gaza.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta yi juyayin tunawa da manyan shahidan gwagwarmaya, inda ta jaddada nauyin da ke wuyan kasashen duniya na hana duk wani cin zarafi daga ‘yan mamaya, tare da yin kira ga dukkan bangarorin da su yi taka tsantsan da yaudara da karya alkawari da sahayoniyya suke yi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka  Rusa A Arewacin Yankin October 10, 2025 Rahotanni : Isra’ila ta fara janye dawa wasu yankuna na Gaza October 10, 2025 Amurka ta kakaba wa wasu kamfanoni 50 takunkumi saboda sayen man Iran October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
  • Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a Masar ranar Litinin  
  • Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi
  • Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza
  • Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
  • Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza
  • Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya