Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-27@21:15:36 GMT

Sardaunan Ikulu Ya Nemi Matasa da Mata su Shiga Siyasa Cikakke

Published: 6th, October 2025 GMT

Sardaunan Ikulu Ya Nemi Matasa da Mata su Shiga Siyasa Cikakke

Daga Abdullahi Usman, Kaduna

Sardaunan Ikulu, Alhaji Dr. Isma’īl Yusuf Ashafa, ya kira mata da matasa a garin Ikulu da su shiga harkokin siyasa domin kawo ci gaba a yankinsu.

Ya fadi hakan ne a lokacin Taron Ikulu da aka shirya a Kaduna karkashin jagorancin Ikulu Political Forum (IPF). Ya jaddada cewa babu wata al’umma da za ta bunkasa sai an samu hadin kai tsakanin jama’a da kuma cikakkiyar rawar da matasa da mata ke takawa a siyasa.

Ya kara da cewa wajibi ne a wayar da kan matasa da mata, a ilimantar da su, sannan a motsa su su gane muhimmancin jagoranci ta hanyar jam’iyyun siyasa. Hakazalika, ya gargadi ‘yan siyasa a yankin da su guji “siyasar do ko mutu,” domin tabbatar da ci gaba da zaman lafiya a yankin.

Ya ce, soyayya, kishin ƙasa, da burin zaman lafiya ya kamata su kasance ginshiƙan jama’ar Ikulu.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Ci Gaban Ikulu (Ikulu Development Association – IDA), Mista Bature S. Likoro, ya jaddada muhimmancin zaman lafiya da ɗorewar haɗin kai a ƙasar Ikulu, tare da kiran shugabanni su mai da hankali kan ci gaban matasa da mata.

Sarauniyar Ikulu, Mrs. Lorentia Bature, ta bayyana cewa idan mata suka nesanta kansu daga siyasa, al’umma ba za ta ci gaba ba. Ta yabawa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, saboda ayyukan ci gaba da yake aiwatarwa, tare da godewa Sardaunan Ikulu, Dr. Isma’īl Yusuf Ashafa, saboda jajircewarsa wajen tallafawa jama’arsa.

Comrade Moses Obadiah, Shugaban Kwamitin Shirya Taro, ya gargadi ‘yan siyasa da su guji siyasar addini, kabilanci da son kai, domin wadannan abubuwa suna haifar da rabuwar kai da koma-baya. Ya bayyana cewa Ikulu Youths Political Forum ta kafa haɗin kai da jam’iyyun siyasa domin inganta dimokuradiyya mai zaman lafiya.

Shugaban Ikulu Youths Political Forum, Mista Mathew Makama, ya bayyana cewa ƙasar Ikulu tana da mutanen kirki, masu gaskiya da kwazo, waɗanda ke son haɗin kai da gaskiya. Ya jaddada cewa zaman lafiya shi ne ginshiƙin ci gaban al’umma.

Mrs. Martina Sunday, shugabar mata, ta ƙarfafa mata da su yi sana’o’in halal domin dogaro da kai. Ta kuma yabawa Ikulu Youths Political Forum saboda ƙoƙarinsu na bunƙasa zaman lafiya da haɗin kai.

Honourable Justina Joseph Usman, Kansilan Ikulu Ward a karamar hukumar Zangon Kataf, ta gode wa Gwamna Uba Sani saboda ƙoƙarinsa na haɗa kan al’umma, tare da bayyana fatan cewa taron zai ƙara ɗaure zumunci da kawo ci gaba a yankin.

Mista Destiny Madaki, jami’i a Ikulu Political Forum, ya ce taron an shirya shi ne domin haɗa ‘ya’yan ƙasar Ikulu don ci gaban al’umma.

Mrs. Asabaru Yaro, memba a Kwamitin Amintattu na Ikulu Development Association, ta bukaci mata su ci gaba da kasancewa masu haɗin kai da tallafawa juna, sannan ta roƙi matasa su kasance masu zaman lafiya, haƙuri da fahimta domin ƙara ɗaukaka yankin.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sardauna zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus

’Yan wasan tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya ta Mata, Super Falcons, sun yi barazanar ƙaurace wa wasannin sada zumunta da Najeriya za ta buga a watan Disamba mai kamawa.

’Yan wasan sun ce za su ƙaurace wa wasannin ne idan har Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta ci gaba da jinkirta biyan kuɗaɗen alawus-alawus da suke biyo tun na Gasar Olympics da aka yi a birnin Paris a 2024.

Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro

Wasu majiyoyi daga ƙungiyar sun tabbatar cewa ’yan wasan na ci gaba da jiran a biya su haƙƙoƙinsu na wasannin da suka buga, ciki har da alawus na nasarar da suka samu a gasar Olympics, duk da cewa Najeriya ta fice tun a matakin rukuni bayan shan kashi a hannun Brazil da Spain da Japan.

Wani jami’in tawagar, wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya ce ’yan wasan gaba ɗaya sun amince cewa ba za su halarci kowanne wasa ba muddin ba a biya su haƙƙoƙinsu ba.

Ana sa ran Najeriya za ta buga jerin wasannin sada zumunta daga ranar 2 zuwa 10 ga watan Disamba, a wani ɓangare na shirye-shiryen Super Falcons domin tunkarar gasar cin Kofin Afrika ta Mata na 2026.

A halin yanzu, NFF ba ta fitar da jerin sunayen ’yan wasan da za su wakilci Najeriya a wasannin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe
  • Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Tsirin Trump Na Zaman Lafiya