Aminiya:
2025-10-13@17:54:12 GMT

Ɗan sanda ya harbe kansa da bindiga bisa kuskure a Kano

Published: 29th, September 2025 GMT

Wani jami’in ’yan sanda a Jihar Kano, Aminu Ibrahim, ya rasu bayan ya harbi kansa bisa kuskure da bindiga a yayin aiki a unguwar Hotoro.

Lamarin ya faru ne da safiyar Asabar ranar da misalin ƙarfe 5:40, a cikin harabar kamfanin Basnaj Global Resources Limited, Hotoro.

Limami ya rasu a hannun ’yan sanda a Kano 2027: APC za ta ƙwace Kano ba tare da taimakon Kwankwaso ba – Jigon APC

Rahotanni sun nuna cewa jami’in, wanda yake aiki a ofishin ’yan sanda na Hotoro, ya shiga bayan gida ne lokacin da abin ya faru.

Wata majiya ta ce, yayin da bindigarsa ƙirar AK-47 ke rataye a wuyansa, sai ya matsa kunamar bindigar bisa kuskure.

“An samu bindigar, mai lambar rajista GT 4177, tare da harsashi ɗaya da aka harba. An lissafa harsashi 29 daga cikin 30 da aka ba shi,” in ji majiyar.

An garzaya da shi Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, inda likita ya tabbatar da rasuwarsa.

An ajiye gawarsa a ɗakin ajiye gawarwaki na asibitin domin yin bincike.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa har yanzu ana bincike kan lamarin, kuma za su bayyana sakamakon nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Sanda harbi

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta

 

Rundunar ‘yansanda ta tabbatar da cewa ana gudanar da cikakken bincike domin gano ainihin musabbabin mutuwarta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara October 5, 2025 Tsaro Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ October 4, 2025 Tsaro Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina September 22, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta
  • ’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi 
  • CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara