Aminiya:
2025-11-27@21:15:56 GMT

2027: APC za ta ƙwace Kano ba tare da taimakon Kwankwaso ba – Jigon APC

Published: 28th, September 2025 GMT

Jigon jam’iyyar APC a Jihar Kano, Seyi Olorunsola, ya ce jam’iyyar za ta iya samun nasara a jihar a zaɓen 2027 ba tare da taimakon Rabiu Musa Kwankwaso ba.

A baya-bayan nan an yi ta raɗe-raɗin cewa Kwankwaso zai fice daga NNPP tare da komawa jam’iyyar APC.

Sojoji sun kama mai yi wa Boko Haram safarar man fetur a Borno Jami’ar Bayero ta sallami ɗalibai 57 kan maguɗin jarrabawa

A taron manema labarai da ya yi a Kano ranar Lahadi, Olorunsola, ya ce Shugaba Tinubu da shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, sun bai wa Kwankwaso kulawa fiye da ƙima.

Ya ce APC na da manyan ’yan siyasa a Kano da za su iya tabbatar da nasarar jam’iyyar.

Ya bayyana cewa Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, Ƙaramin Ministan Harkokin Gidaje, Yusuf Abdullahi Atah, da Sanata Kawu Sumaila za su iya kayar da Gwamna Abba Kabir Yusuf a zaɓen 2027.

A cewarsa, Atah, zai ƙalubalanci Gwamna Abba a Kano ta Tsakiya, yayin da Barau Jibrin da tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje za su jagoranci Kano ta Arewa, sannan Kawu Sumaila ya kula da Kano ta Kudu.

Olorunsola, ya bayyana cewa ƙungiyarsu, wato Tinubu/Barau/Atah Movement, ta shirya tsayar da Barau Jibrin a matsayin ɗan takarar gwamna na APC a 2027.

A gefe guda kuma, ya zargi Kwankwaso da yunƙurin shiga APC, domin karya shirinsu tare da bai wa Abba damar sake zama gwamna.

Ya kuma jaddada cewa APC ta lashe zaɓen gwamna na 2023, inda ta yi nasara a kotun sauraron ƙorafe-ƙorafe da kotun ɗaukaka ƙara, amma daga baya kotun ƙoli ta yanke hukunci akasin abin da yake na gaskiya.

Olorunsola, ya gargaɗi Shugaba Tinubu da kada ya dogara da Kwankwaso wajen samun nasara a Kano.

Ya ce Kwankwaso ba shi da wani cikakken iko a jam’iyyarsa ta NNPP.

Ya ce idan Kwankwaso na son shiga APC da gaske, dole ne ya fara daga matakin unguwa, Ƙaramar Hukumar da jiha tare da bin kundin tsarin mulkin jam’iyyar da ƙa’idojinta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwankwaso Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Gombe ta ƙaddamar da sabbin matakan ƙarfafa tsaro a makarantu bayan wani taron tattaunawa da aka gudanar tsakanin Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar, Bello Yahaya, da shugabannin Ƙungiyar Malaman Sakandare reshen jihar.

An gudanar da taron ne a Hedikwatar Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Gombe, bisa umarnin Sufeton ’Yan Sanda na Ƙasa, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, na ƙara tsaurara tsaro a makarantu a faɗin ƙasar nan.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya bayyana cewa tattaunawar ta mayar da hankali kan duba tsarin tsaro na yanzu a makarantu, musamman waɗanda ke yankunan da ke da ƙalubale, tare da gano wuraren da ake buƙatar gaggawar gyara.

CP Bello Yahaya ya tabbatar da kudirin Rundunar ’Yan Sanda ta Najeriya na ci gaba da kare cibiyoyin ilimi, yana mai cewa makarantu dole ne su kasance wurare masu aminci domin koyo da koyarwa.

Ya jaddada muhimmancin yin nazarin tsaro a kai a kai, tsara matakan rigakafi, da kuma tabbatar da ci-gaba da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin makarantu, Ma’aikatar Ilimi da hukumomin tsaro.

Kwamishinan ya bayyana cewa rundunar ta ƙara karfafa sintiri, sa ido, da kuma gaggawar amsa kira a yankunan makarantu da aka fi ganin haɗarin tsaro.

Ya kuma bukaci shugabannin makarantu su riƙa kasancewa a shirin tuntuɓar ofisoshin ’yan sanda mafi kusa, tare da hanzarta ba da rahoton duk wani abin da ya haifar da zargi.

Ya yaba wa shugabannin ANCOPSS bisa jajircewarsu wajen aiki tare da hukumar ’yan sanda domin ƙarfafa tsaro a makarantu.

A nasu ɓangaren, shugabannin ANCOPSS sun gode wa rundunar ’yan sanda bisa ƙoƙarin da take yi na tabbatar da lafiyar dalibai da malamai, tare da alƙawarin yin aiki kafada da kafaɗa da rundunar da Ma’aikatar Ilimi domin ƙarfafa duk tsare-tsaren tsaro a makarantun sakandare.

Rundunar ta kuma yi kira ga iyaye, malamai, shugabannin al’umma, da mazauna unguwanni da su kasance masu lura da faɗakarwa, tare da tallafa wa duk wani yunƙurin inganta tsaro a makarantu, domin kiyaye rayuwar ɗalibai nauyi ne da ya rataya a kan kowa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe