Aminiya:
2025-10-13@17:58:47 GMT

Limami ya rasu a hannun ’yan sanda a Kano

Published: 28th, September 2025 GMT

Al’ummar unguwar Kuntau da ke Ƙaramar Hukumar Gwale a Jihar Kano, sun shiga  jimami bayan rasuwar wani matashin limami, Salim Usman, wanda ake zargin ya rasu a hannun ’yan sanda.

An kama Salim mai shekara 24 a gidansa a ranar 22 ga watan Satumba, jim kaɗan bayan jagorantar sallar Magariba.

2027: APC za ta ƙwace Kano ba tare da taimakon Kwankwaso ba – Jigon APC Sojoji sun kama mai yi wa Boko Haram safarar man fetur a Borno

An zarge shi da siyan buhun fulawa, wadda aka ce an sace a bara.

Mahaifinsa, Sheikh Adam Usman, ya bayyana cewa bidiyon na’urar CCTV ya nuna yadda jami’an ’yan sanda biyu suka yi wa ɗansa dukan tsiya a lokacin da suka zo su kama shi.

Ya ƙara da cewa an ci gaba da dukansa a ofishin ’yan sanda, wanda hakan ya yi sanadin mutuwarsa.

Sheikh Usman, ya ce wani abokin Salim ya bi jami’an zuwa ofishin ’yan sanda, sannan daga baya ya sanar da shi abin da ke faruwa.

Ya ce ya garzaya ofishin a daren da aka kama shi, amma aka hana shi ganin ɗansa, aka ce ya dawo washegari.

“Da na koma washegari, suka ce min ɗana ya yi rashin lafiya a daren da ya gabata aka kai shi asibiti. Amma daga baya na gano cewa tuni ya rasu.

“Da farko, an kai gawarsa Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhammad a matsayin gawar ‘wanda ba a sani ba,’ amma aka ƙi karɓa.

“Sai aka kai shi Asibitin Ƙwararru na Abdullahi Wase, inda aka ajiye shi a ɗakin ajiye gawarwaki,” in ji mahaifin matashin limamin.

Ya cw tuni suka kai ƙara hukumar ’yan sanda, kuma an shaida musu cewa an kama wasu jami’ai bisa rashin ƙwarewa a aikinsu, ana kuma gudanar da bincike.

An bayar da gawar Salim a ranar 26 ga watan Satumba, domin a binne shi bayan kotu ta bayar da umarnin a yi gwaji a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano.

Sakamakon gwajin zai fito cikin makonni huɗu.

Mutanen unguwar sun bayyana marigayin a matsayin mutum mai sauƙin kai da son zaman lafiya, inda suka ce mutuwarsa ta jefa su cikin  damuwa.

Ƙoƙarin samun jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ci tura zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Gawa zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ebonyi, ta kama wani mutum mai suna Chukwuma Onwe, ɗan Ƙaramar Hukumar Izzi, bisa zargin sayar da ɗan da aka haifa masa kwanaki biyar kan Naira miliyan 1.5.

An gano cewa Onwe ya sayar wa wata mata mai suna Chinyere Ugochukwu jaririn, wacce ake zargin tana cikin ƙungiyar safarar yara zuwa ƙasashen waje.

ASUU za ta fara yajin aikin mako 2 daga ranar Litinin Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja

Dukkaninsu suna hannun ’yan sanda.

Wata majiyar ’yan sanda ta bayyana cewa matar Onwe, mai suna Philomena Iroko, ce ta fallasa shi bayan ta samu labari daga maƙwabta cewa mijinta ya sayar da jaririn da suka haifa.

Da ta tabbatar da hakan, sai ta garzaya ta kai rahoto ofishin ’yan sanda, inda aka kama Onwe ba tare da ɓata lokaci ba.

Kakakin rundunar jihar Ebonyi, SP Joshua Ukandu, ya tabbatar da cewa an ceto jaririn daga hannun wacce ta saya shi.

Ya ce an kama Onwe da Chinyere Ugochukwu a ranar Juma’a a unguwar Azugwu, Ƙaramar Hukumar Abakaliki, kuma suna tsare a hannun ’yan sanda domin ci gaba da bincike.

Matar Onwe, Philomena, ta ce ta yi mamaki matuƙa cewa mijinta ya sayar da jaririn nasu.

Ta bayyana cewa tun bayan haihuwarta, Onwe, ya ce zai kai jaririn wajen ’yar uwarsa domin ta sa masa albarka, sai dai daga baya aka gano cewa ya sayar da shi.

Ta ce, “Yaronmu bai wuce kwanaki biyar da haihuwa ba, amma mijina ya sayar da shi.

“Ban taɓa tunanin zai yi haka ba. Ina roƙon jama’a da masu hannu da shuni su taimaka min a wannan hali da na tsinci kaina.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano