PENGASSAN ta tsunduma yajin aiki kan korar ma’aikata a kamfanin Dangote
Published: 28th, September 2025 GMT
Ƙungiyar Ma’aikata Masu Aikin Mai da Gas ta Najeriya (PENGASSAN), ta fara yajin aiki saboda korar wasu ma’aikata a Matatar Mai ta Dangote da ke Jihar Legas.
Sakataren ƙungiyar, Lumumba Okugbawa, ya ce sun fara yajin aikin ne daga ranar Lahadi, 28 ga watan Satumba, 2025.
Jami’ar Bayero ta sallami ɗalibai 57 kan maguɗin jarrabawa ‘Yan fashi sun sace mutum 17 a mahadar tekun Akwa Ibom da Kuros RibaDa misalin ƙarfe 6 na safe, mambobin ƙungiyar da ke aiki a ɗakunan kula da na’urori suka daina aiki.
Umarnin ya shafi mambobin da ke ofisoshi, kamfanoni, da hukumomin gwamnati a faɗin Najeriya, waɗanda za su daina aiki da misalin ƙarfe 12:01 na daren ranar Litinin, 29 ga watan Satumba.
Okugbawa, ya ce ba za a yi wani aiki a wuraren da abin ya shafa ba sai dai idan ya shafi tsaron rayuka ko kayan aiki, kuma sai da amincewar babban ofishin ƙungiyar.
Ƙungiyar ta kuma umarci a dakatar da dakon ɗanyen mai da gas zuwa matatar man Dangote.
Ta buƙaci mambobin da ke aiki a manyan kamfanonin mai na ƙasa da ƙasa (IOCs) su rage yawan dadin gaske da ake kai wa matatar Dangote.
A cikin sanarwarta, PENGASSAN ta nemi mambobinta da su yi addu’a “don Allah ya bai wa shugabanni ƙarfin gwiwa su tilasta Dangote da sauran ’yan kasuwa su girmama dokokin ƙasa.”
Yajin aikin ya biyo bayan korar ma’aikata sama da 800 daga matatar, wanda kamfanin ya tabbatar a ranar Juma’a a matsayin wani ɓangare na sake tsara harkokinsa.
Kamfanin ya ce “’yan kaɗan ne abin ya shafa,” amma ƙungiyar ta ce hakan rashin adalci ne, ta kuma buƙaci a dawo da dukkanin ma’aikatan da aka kora.
A martaninta, matatar Dangote ta zargi PENGASSAN da yunƙurin lalata harkar samar da makamashi a ƙasar na ta hanyar umartar a dakatar da kai mata ɗanyen mai da gas.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Matatar Dangote Yajin aiki
এছাড়াও পড়ুন:
Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
Ana fargabar cewa wata mata mai suna Success ta kashe wata yarinya mai shekaru bakwai, Alicia Olajumoke, a unguwar Rumueme da ke birnin Fatakwal na Jihar Ribas.
Mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa matar da ake zargin tana da kusanci da dangin mahaifiyar yarinyar, wacce ita kaɗai ce a wurin iyayenta.
El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin NijeriyaBayanai sun ce ita ma matar ta caka wa kanta wuƙa a wuya bayan kashe yarinyar, kuma bayan an garzaya da duk su biyun asibiti, likitoci suka tabbatar da cewa sun riga mu gidan gaskiya.
Lamarin wanda ya faru a ranar Talata ya ɗimauta mazauna yankin, la’akari da zargin cewa matar ta kashe yarinyar ce a gidanta bayan ta je har makarantarsu ta ɗauko ta ba tare da izinin mahaifiyarta ba.
Jami’ar hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sanda a Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis, inda ta ce an kai gawar yarinyar ɗakin ajiye gawa domin bai wa likitoci damar kammala bincikensu na kimiyya gabanin soma nasu binciken.
“Mun ziyarci wurin da abin ya faru, mun ɗauki hotuna, kuma an garzaya da su asibiti inda aka tabbatar da mutuwarsu.”