Aminiya:
2025-10-13@15:52:55 GMT

PENGASSAN ta tsunduma yajin aiki kan korar ma’aikata a kamfanin Dangote

Published: 28th, September 2025 GMT

Ƙungiyar Ma’aikata Masu Aikin Mai da Gas ta Najeriya (PENGASSAN), ta fara yajin aiki saboda korar wasu ma’aikata a Matatar Mai ta Dangote da ke Jihar Legas.

Sakataren ƙungiyar, Lumumba Okugbawa, ya ce sun fara yajin aikin ne daga ranar Lahadi, 28 ga watan Satumba, 2025.

Jami’ar Bayero ta sallami ɗalibai 57 kan maguɗin jarrabawa ‘Yan fashi sun sace mutum 17 a mahadar tekun Akwa Ibom da Kuros Riba

Da misalin ƙarfe 6 na safe, mambobin ƙungiyar da ke aiki a ɗakunan kula da na’urori suka daina aiki.

Umarnin ya shafi mambobin da ke ofisoshi, kamfanoni, da hukumomin gwamnati a faɗin Najeriya, waɗanda za su daina aiki da misalin ƙarfe 12:01 na daren ranar Litinin, 29 ga watan Satumba.

Okugbawa, ya ce ba za a yi wani aiki a wuraren da abin ya shafa ba sai dai idan ya shafi tsaron rayuka ko kayan aiki, kuma sai da amincewar babban ofishin ƙungiyar.

Ƙungiyar ta kuma umarci a dakatar da dakon ɗanyen mai da gas zuwa matatar man Dangote.

Ta buƙaci mambobin da ke aiki a manyan kamfanonin mai na ƙasa da ƙasa (IOCs) su rage yawan dadin gaske da ake kai wa matatar Dangote.

A cikin sanarwarta, PENGASSAN ta nemi mambobinta da su yi addu’a “don Allah ya bai wa shugabanni ƙarfin gwiwa su tilasta Dangote da sauran ’yan kasuwa su girmama dokokin ƙasa.”

Yajin aikin ya biyo bayan korar ma’aikata sama da 800 daga matatar, wanda kamfanin ya tabbatar a ranar Juma’a a matsayin wani ɓangare na sake tsara harkokinsa.

Kamfanin ya ce “’yan kaɗan ne abin ya shafa,” amma ƙungiyar ta ce hakan rashin adalci ne, ta kuma buƙaci a dawo da dukkanin ma’aikatan da aka kora.

A martaninta, matatar Dangote ta zargi PENGASSAN da yunƙurin lalata harkar samar da makamashi a ƙasar na ta hanyar umartar a dakatar da kai mata ɗanyen mai da gas.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Matatar Dangote Yajin aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya, ta gargaɗi Ƙungiyar Malaman Kami’o’i ta Ƙasa (ASUU), cewa za ta aiwatar da dokar “babu aiki, babu albashi” idan malaman suka ci gaba da yajin aikin da ka iya zai kawo cikas ga harkokin karatu.

A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta fitar da yammacin ranar Lahadi, Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, da Ƙaramar Ministan Ilimi, Suwaiba Sa’id Ahmed, sun ce gwamnati tana da niyyar magance ƙorafe-ƙorafen ASUU ta hanyar tattaunawa cikin lumana.

Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja

“Gwamnati ta nuna gaskiya, haƙuri da kyakkyawar niyya a tattaunawarta da ƙungiyar,” in ji sanarwar.

Ministocin sun bayyana cewa yawancin buƙatun ASUU, kamar ƙarin kuɗin koyarwa da inganta yanayin aiki an riga an biya musu.

Sauran matsalolin kuma suna ƙarƙashin kulawar kwamitocin gudanarwar jami’o’i, waɗanda gwamnati ta sake kafawa don su kula da batutuwan da suka rage.

Sai dai duk da waɗannan matakan, ASUU ta zaɓi shiga yajin aiki.

Ministocin sun ce wannan mataki bai nuna haɗin kai ko adalci ga ɗalibai da jama’a ba.

Sun ƙara da cewa: “Gwamnati ta yi tsayin daka wajen tabbatar da zaman lafiya da daidaita karatu a jami’o’i.

“Amma sun yi gargaɗi cewa, dokar “babu aiki, babu albashi” tana nan daram a tsarin dokokin ƙwadago na Najeriya, kuma gwamnati za ta yi amfani da ita idan aka katse harkokin karatu.

Gwamnati ta roƙi ASUU da ta sake tunani tare da dawowa teburin sulhu, inda ta ce ƙofarta a buɗe ta ke don tattaunawa da yin sulhu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • ASUU ta tsunduma yajin aikin mako 2
  • Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Yanzu-Yanzu: ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki Na Tsawon Mako Biyu
  • ASUU za ta fara yajin aikin mako 2 daga ranar Litinin
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida