Nukiliya: MDD ta sake ƙaƙaba wa Iran takunkuman karayar tattalin arziki
Published: 28th, September 2025 GMT
Majalisar Dinkin Duniya ta sake ƙaƙaba wa Iran takunkumai na karayar tattalin arziki bayan gaza cimma matsaya a tattaunawar ƙarshe kan shirin nukiliyarta da manyan ƙasashen yammacin Turai.
Birtaniya, Faransa da Jamus ne suka bijiro da batun maido da waɗannan takunkuman a taron kwamitin Sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya, wanda aka yi kan saɓa yarjejeniyar nukiliyar shekarar 2015 da Iran ta yi.
Haka kuma, ƙasashen uku sun gargaɗi Tehran kan ɗaukar matakan da za su ƙara dagula lamarin.
“Sake ƙaƙaba takunkuman Majalisar Dinkin Duniya ba yana nufin ƙarshen diflomasiyya ba ne,” in ji ministocin harkokin wajen ƙasashen uku na Turai, da aka fi sani da E3, a cikin wata sanarwa ta haɗin gwiwa a ranar Lahadi.
“Muna kira ga Iran da ta guji ɗaukar matakan da za su ƙara dagula lamarin, sannan ta koma bin ƙa’idojin da suka zama dole a ƙarƙashin yarjejeniyoyin tsaron da suka shafi doka,” kamar yadda suka ƙara da cewa.
An dai maido da ɗimbim takunkuman karayar tattalin arziki kan Iran a karon farko cikin shekaru 10 kamar yadda RFI ya ruwaito.
Takunkuman, waɗanda ke zuwa watanni biyu bayan fito na fito tsakanin Iran da Isra’ila, lamarin da ya sa Amurka ta kai wani gagarumin harin bam a tashoshin nukiliyarta, zai haifar da koma-baya ga tattalin arzƙin Iran, wanda ke fuskantar ƙalubale.
Iran ta yi tir da maido da takunkuman, tana mai bayyana matakin a matsayin abin da bai dace ba, inda ta yi kira ga ƙasashen duniya da kada su aiwatar da su.
Wata sanarwa daga ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Iran wadda ta bayyana hakan, ta ce babu adalci a wannan matakin, wanda ta ce ya saɓa ƙa’ida.
A halin da ake ciki, tuni Iran ta janye jakadunta a ƙsashen Birtaniya, Faransa da Jamus.
Manyan ƙasashen duniya dai na zargin Iran ne da ƙoƙarin ƙera makaman nukiliya, duba da yadda take ci gaba da tacewa, tare da inganta ma’adinan uranium, zargin da Iran ta sha musantawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Birtaniya Faransa Iran Majalisar Dinkin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa
’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu sun yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, afuwa bayan da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.
Kungiyar ’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu maso Gabas ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya yi amfani da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi, wajen yi wa Nnamdi Kanu afuwa wanda kotu ta same shi da laifin ta’addanci.
Alƙali James Omotosho na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ne ya yanke hukuncin, inda ya same shi da laifi a kan tuhumar da ake masa guda bakwai, sannan ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.
Tuni aka tura Nnamdi Kanu zuwa gidan yari a Jihar Sakkwato inda yake zaman waƙafi.
Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke FuskantaA cikin sanarwa bayan taron gaggawa da suka gudanar a Abuja, ’yan majalisar sun ce duk da cewa suna girmama kotu da tsarin shari’a, lamarin ya rikiɗe zuwa matsalar ƙasa mai tasiri ga rayuwar jama’a, tattalin arziki da tsaro.
Da yake karanta sanarwar, Hon. Iduma Igariwey ya ce yin afuwa zai taimaka wajen rage tashin hankali da dawo da zaman lafiya a yankin.
Sun lissafa dalilai guda huɗu da suka sa suka yi wannan kira.
Dalilan da suke bayyana su ne ƙaruwa da rashin tsaro da tashin hankali da ke da alaƙa da tsare Kanu; Wahalar rayuwa da tattalin arziki da jama’a ke fuskanta da kuma buƙatar shugabanci mai tausayawa wajen shawo kan matsalolin ƙasa.