Aminiya:
2025-10-13@17:53:42 GMT

Nukiliya: MDD ta sake ƙaƙaba wa Iran takunkuman karayar tattalin arziki

Published: 28th, September 2025 GMT

Majalisar Dinkin Duniya ta sake ƙaƙaba wa Iran takunkumai na karayar tattalin arziki bayan gaza cimma matsaya a tattaunawar ƙarshe kan shirin nukiliyarta da manyan ƙasashen yammacin Turai.

Birtaniya, Faransa da Jamus ne suka bijiro da batun maido da waɗannan takunkuman a taron kwamitin Sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya, wanda aka yi kan saɓa yarjejeniyar nukiliyar shekarar 2015 da Iran ta yi.

NECO ta sake jaddada nasarar ɗaliban Kano a jarrabawar bana Matatar Dangote ta ci gaba da sayar da man fetur a naira

Haka kuma, ƙasashen uku sun gargaɗi Tehran kan ɗaukar matakan da za su ƙara dagula lamarin.

“Sake ƙaƙaba takunkuman Majalisar Dinkin Duniya ba yana nufin ƙarshen diflomasiyya ba ne,” in ji ministocin harkokin wajen ƙasashen uku na Turai, da aka fi sani da E3, a cikin wata sanarwa ta haɗin gwiwa a ranar Lahadi.

“Muna kira ga Iran da ta guji ɗaukar matakan da za su ƙara dagula lamarin, sannan ta koma bin ƙa’idojin da suka zama dole a ƙarƙashin yarjejeniyoyin tsaron da suka shafi doka,” kamar yadda suka ƙara da cewa.

An dai maido da ɗimbim takunkuman karayar tattalin arziki kan Iran a karon farko cikin shekaru 10 kamar yadda RFI ya ruwaito.

Takunkuman, waɗanda ke zuwa watanni biyu bayan fito na fito tsakanin Iran da Isra’ila, lamarin da ya sa Amurka ta kai wani gagarumin harin bam a tashoshin nukiliyarta, zai haifar da koma-baya ga tattalin arzƙin Iran, wanda ke fuskantar ƙalubale.

Iran ta yi tir da maido da takunkuman, tana mai bayyana matakin a matsayin abin da bai dace ba, inda ta yi kira ga ƙasashen duniya da kada su aiwatar da su.

Wata sanarwa daga ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Iran wadda ta bayyana hakan, ta ce babu adalci a wannan matakin, wanda ta ce ya saɓa ƙa’ida.

A halin da ake ciki, tuni Iran ta janye jakadunta a ƙsashen Birtaniya, Faransa da Jamus.

Manyan ƙasashen duniya dai na zargin Iran ne da ƙoƙarin ƙera makaman nukiliya, duba da yadda take ci gaba da tacewa, tare da inganta ma’adinan uranium, zargin da Iran ta sha musantawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Birtaniya Faransa Iran Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya, ta gargaɗi Ƙungiyar Malaman Kami’o’i ta Ƙasa (ASUU), cewa za ta aiwatar da dokar “babu aiki, babu albashi” idan malaman suka ci gaba da yajin aikin da ka iya zai kawo cikas ga harkokin karatu.

A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta fitar da yammacin ranar Lahadi, Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, da Ƙaramar Ministan Ilimi, Suwaiba Sa’id Ahmed, sun ce gwamnati tana da niyyar magance ƙorafe-ƙorafen ASUU ta hanyar tattaunawa cikin lumana.

Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja

“Gwamnati ta nuna gaskiya, haƙuri da kyakkyawar niyya a tattaunawarta da ƙungiyar,” in ji sanarwar.

Ministocin sun bayyana cewa yawancin buƙatun ASUU, kamar ƙarin kuɗin koyarwa da inganta yanayin aiki an riga an biya musu.

Sauran matsalolin kuma suna ƙarƙashin kulawar kwamitocin gudanarwar jami’o’i, waɗanda gwamnati ta sake kafawa don su kula da batutuwan da suka rage.

Sai dai duk da waɗannan matakan, ASUU ta zaɓi shiga yajin aiki.

Ministocin sun ce wannan mataki bai nuna haɗin kai ko adalci ga ɗalibai da jama’a ba.

Sun ƙara da cewa: “Gwamnati ta yi tsayin daka wajen tabbatar da zaman lafiya da daidaita karatu a jami’o’i.

“Amma sun yi gargaɗi cewa, dokar “babu aiki, babu albashi” tana nan daram a tsarin dokokin ƙwadago na Najeriya, kuma gwamnati za ta yi amfani da ita idan aka katse harkokin karatu.

Gwamnati ta roƙi ASUU da ta sake tunani tare da dawowa teburin sulhu, inda ta ce ƙofarta a buɗe ta ke don tattaunawa da yin sulhu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
  • Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa