Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?
Published: 28th, September 2025 GMT
Birnin Taicang dake lardin Jiangsu na kasar Sin birni ne da ake kiran shi da sunan birnin kamfanonin kasar Jamus a kasar Sin, domin kamfanonin kasar Jamus fiye da 560 suna aiwatar da harkokinsu a wurin, ciki har da kamfanoni fiye da 60 da suka fi samun ci gaba a wasu kananan fannoni. Watakila wadannan kamfanoni ba su yi girma ko yin suna sosai ba, amma sun zama matsayin gaba a duniya a matakan wasu kananan fannoni, me ya sa Sin ta jawo hankalinsu sosai?
Shugaban reshen kamfanin Knorr-Bremse AG dake kasar Sin Bi Guanghong ya yi bayanin cewa, masana’antun kasar Sin sun zama matsayin farko a duniya, kana babu bukatar kashe kudi da yawa, da daidaita matsaloli cikin sauri, da kuma shafar fannoni mafi yawa.
Manajan reshen kamfanin Wessel Household Appliances na kasar Jamus dake kasar Sin Francis Kremer ya yi nuni da cewa, ana iya gama bincike da nazari a cikin makwani 4 ko 6 ko 8 a kasar Sin, lokacin ya fi sauri idan aka kwantanta shi da sauran kasashen duniya. Kana ana iya samar da kayayyaki a kasar kai tsaye, inda lamarin yake da muhimmanci sosai. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: a kasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
Rahotanni sun tabbatar da rasuwar wasu sojoji huɗu, bayan ’yan ta’adda sun kai hari yankin Ngamdu na Jihar Borno.
Jihar Borno ta daɗe tana fama da hare-haren ta’addanci, musamman daga ƙungiyar Boko Haram.
Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno An yi jana’izar sojojin da ’yan bindiga suka kashe a KebbiKo da yake wasu mazauna yankin sun ce sojoji 10 ne suka mutu, sai dai mai magana da yawun rundunar Operation Haɗin Kai, Laftanar Kanar Sani Uba, bai tabbatar da hakan ba cikin sanarwar ya fitar a ranar Juma’a.
Amma rahotanni sun bayyana cewa sojoji huɗu ne suka mutu, yayin da wasu biyar suka jikkata a yayin harin.
A cewar Kanar Sani, ’yan ta’addan sun yi amfani da roka, jirage marasa matuƙa, da bama-bamai wajen kai harin.
Sai dai sojojin sun mayar da martani, inda suka kashe da dama daga cikin ’yan ta’addan.
Ya ƙara da cewa wasu motocin yaƙi na sojojin sun lalace, amma duk da haka dakarun sun yi tsayin daka wajen yaƙar maharan.
Bayan harin, ’yan ta’addan sun yi ƙoƙarin hana bin hanyar Ngamdu zuwa Damaturu, wanda hakan ya tilasta rufe hanyar na ɗan lokaci.
Daga baya,sojoji sun cire bama-bamai guda uku, sannan suka sake buɗe hanyar ga matafiya.
Laftanar Kanar Uba, ya ce an ƙara wa dakarun kayan yaƙi da harsasai domin ci gaba da fafatawa.
Rahotanni sun nuna cewa gawarwakin ’yan ta’adda kusan 15 aka samu a kusa da ƙauyen Bula Wura.
Rundunar Sojin Najeriya ta yaba wa jarumtar dakarun, tare da tabbatar wa jama’a cewa zaman lafiya ya samu a yankin.