Leadership News Hausa:
2025-11-27@21:37:23 GMT

Shugaban Cuba Ya Yi Bayani Kan Nazarin Fasahohin Sin A Fannoni Shida

Published: 28th, September 2025 GMT

Shugaban Cuba Ya Yi Bayani Kan Nazarin Fasahohin Sin A Fannoni Shida

A kwanakin baya, shugaban kasar Cuba Miguel Díaz-Canel ya yi hira da wakilin rukunin gidajen rediyo da telebijin na kasar Sin wato CMG, inda ya bayyana cewa, kasarsa ta Cuba ta yi nazari kan kwaskwarimar da kasar Sin ta yi, kamar su yadda kasar Sin ta mika iko ga kananan gwamnatocin kasar don sa kaimi ga daidaita harkokin sassan kasar, da daukar jerin matakai wajen yin kwaskwarima a kauyuka don tabbatar da wadatar abinci, da daidaita huldar dake tsakanin manyan tsare-tsare da mika iko ga kananan gwamnatoci, da kuma kasuwanci, da sa kaimi ga raya kimiyya da fasaha da yin kirkire-kirkire, da bunkasa sha’anin al’adu da yawon bude ido a kasar don maida al’adu su zama jigon sha’anin yawon bude ido, da kuma kiyaye maida hankali ga tunawa da tarihi yayin da jam’iyyar Kwaminis ta Sin take jagorancin kasar wajen samun ci gaba.

A ganin shugaba Díaz-Canel, wadannan fannoni shida suna zama matsayi mai muhimmanci da ma’ana, suna bin tunanin raya tsarin gurguzu, kana sun samar da fasahohin Sin ga kasar Cuba wajen sa kaimi ga samun ci gaba a kasar Cuba. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya sauka sheƙa daga jam’iyyar SDP zuwa jami’yyar haɗaka ta ADC.

Komawar El-Rufai jam’iyyar ADC a hukumance wani mataki ne da ake ganin zai kawo sabon salo a siyasar adawa wajen ƙalubalantar jam’iyyar APC mai mulki a Zaɓen 2027.

An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da Olympiacos

A wannan Alhamis ɗin ce El-Rufai ya kammala rajistar zama mamba na jam’iyyar ADC a mazaɓarsa ta Unguwar Sarki da ke birnin Kaduna, inda ya yi alƙawarin amfani da jam’iyyar ADC wajen fuskantar abin da ya kira rashin ƙwarewa a jagorancin gwamnatin jihar.

“Ina da cikakkiyar rajista a jam’iyyar African Democratic Congress,” in ji shi a gaban manyan jami’an jam’iyyar, ciki har da Mataimakin Shugaban ADC na Arewa maso Yamma, Jafaru Sani, da Sakataren Yi wa Mambobi Rajistar Jam’iyyar na Ƙasa, Sanata Sadiq Yar’adua.

A watan Maris na bana ne dai El-Rufai ya sauya sheƙa daga APC zuwa SDP a wani yunƙuri na shirya haɗin gwiwar adawa, sai dai ya ce tattaunawar da suke yi a SDP ɗin ta gaza haifar da ɗa mai ido wajen cimma muradinsu saboda “tsoma bakin gwamnati da kuma cin hanci da wasu shugabannin jam’iyyar ke yi.”

Da yake jawabi kan siyasar Jihar Kaduna, El-Rufai ya yi kira ga jama’a da su yi rajista da ADC domin “maimaita abin da muka yi a 2015,” yana mai zargin gwamnatin APC mai ci da sakaci da jagorancin al’umma.

“Ina kira ga dukkan ’yan Kaduna masu shekaru 18 zuwa sama da su fito su yi rajista. Da ikon Allah, zamu sake kawar da gwamnatin da ta nuna gazawa.

“Mu da muka taimaka muka ɗora su a kujerar mulki, za mu taimaka wajen dawo da su gida… kafin su wuce kotu,” in ji El-Rufai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta