Aminiya:
2025-10-13@17:45:11 GMT

Yadda A ‘Daidaita Sahu’ ya ƙwace kasuwar bas da tasi

Published: 27th, September 2025 GMT

Gabanin shekarar 2005 da gwamnatin Kano ta hana sana’ar haya da babur saboda matsalar tsaro da ta kunno kai jihar, jigilar fasinjoji ta ta’allaƙa ne da motocin haya na hayis, ko tasi, a kuma farashi mai sauƙi.

Sai dai sannu a hankali, waɗannan motocin hayar suna neman zama tarihi musamman a birane saboda zuwan babura masu ƙafa uku, waɗanda aka fi sani da ‘A Daidaita Sahu’ a lunguna da saƙo.

Wata ƙididdiga da Hukumar Samar da Kuɗaɗen Shiga ta Jihar Kano ta fitar, na nuna gwamnatin jihar tana samun aƙalla Naira miliyan shida a kullum daga harajin Naira 100 da ta sanya wa masu sana’ar A Daidata Sahu — wanda a shekara ya kai Naira biliyan 2.1.

Haka kuma rahoton da Hukumar Kula da Titunan Kano (KAROTA) ta fitar a shekarar 2021 ya nuna sama da baburan A Daidata Sahu 60,000 ne ta yi wa rajista a jihar.

Ƙasashen duniya sun ƙaurace wa Isra’ila a Babban Taron MƊD Me ya sa wasu ƙasashen Afirka ba sa goyon bayan kafa ƙasar Falasɗinu?

Sai dai ƙungiyar masu sana’ar ta musanta alƙaluman, inda ta yi iƙirarin cewa adadin na iya ninka hakan saboda ba duka ne aka yi wa rajista ba.

A hannu guda kuma ƙididdigar Ƙungiyar Ma’aikatan Sufuri ta Ƙasa (NURTW) reshen Jihar Kano, ta nuna a tsakanin shekarar 2015 zuwa 2023, an rufe sama da kashi 65% na tashoshin bas a jihar sakamakon ƙarancin fasinjoji da tsadar kula da motocin haya.

Wannan ya bayar da gudummawa wajen ƙaruwar matasan da suka ajiye sana’ar haya da bas suka rungumi A Daidaita Sahu, wasu kuma suka durƙushe baki ɗaya.

Abdullahi Gadanya, tsohon direban bas ne da ya shafe shekaru yana sana’ar a Kano. A tattaunawarsa da Aminiya ya bayyana halin ha’u’la’in da durƙusheawar sana’ar ta jefa su cikin halin ƙaka-na-ka-yi.

“Samun A Daidaita ya taka rawa wajen mayar da sana’armu koma-baya. A da nakan iya ɗaukar fasinja 15 a sa’a ɗaya, amma yanzu kuwa sai godiyar Allah kawai. Jama’a sun fi karkata zuwa A Daidaita.

“A shekarun baya nakan samu N20,000 a sa’a ɗaya zuwa biyu, amma yanzu sai dai idan na shiga tashar da ake yin lodi zuwa wasu jihohin na ɗauki fasinja wuni guda nake iya samun rabin hakan.

“Motata ta tsufa, saboda haka lodi ɗaya kawai nake yi, ba ta riƙe ni saboda ina da iyali. Sai ka ga a rana bai fi ka yi N10,000 ba saɓanin a baya da kuɗin ya ninka haka, kuma a cikin gari ne.”

Gadanya ya ce a dalilin wannan tasgaron, dole ta sanya shi bai wa mai ɗakinsa jari inda take cinikin kayyakin girki kamar su man gyaɗa da daddawa.

Ya fi sauƙi — Fasinja

Habiba Sabo guda ce daga cikin fasinjojin da har yanzu suke hawabas, ta kuma ce ba wani abu ne ya sanya ta rungumar motar hayar ba face kasancewarta mafi arhar hanyar sufuri har a yanzu.

“Ni daga Ƙarfi nake zuwa Kano domin sayar da masara. Idan na hau A Daidaita, ribar sana’a takan ɓace saboda tsada. Amma idan muka haɗu da abokan sana’ata muka hau bas, bayan kuɗin bai kai na A Daidaita ba, ana ƙara yi mana ragi sosai.”

Sai dai a ɓangaren Harira Ado da ita ma ’yar kasuwa ce, lalura ce kaɗai ke tilasta ta hawa bas a yanzu.

“Idan kana sauri, bas ɓata maka lokaci za ta yi. Sau da yawa gara na hau A Daidaita. Amma idan zan saro kaya daga Kura ko Bata, bas nake hawa saboda N300 kacal ta ishe ni zuwa da dawowa tare da lodin kayana. Amma a A Daidaita sai na kashe wajen N1,500 a zuwa kaɗai saboda kayana.”

Matsalar tsaro da asarar rai

Rahoton Bloomberg na shekara (2022) ya nuna cewa ƙasashe masu tasowa kamar Nijeriya na fama da matsalar amfani da ƙananan ababen hawa musamman baburan A Daidata wajen aikata laifuka saboda rashin rajista da rashin tsauraran matakan tsaro daga ɓangaren gwamnati.

Haka kuma, Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) ta ce yawaitar A Daidata Sahu ya haifar da ƙaruwar haɗari a tituna, inda ta ce a Kano kaɗai, sama da kashi 60 na haɗuran shekarar 2023 na A Daidaita Sahu ne.

Kazalika matsalar tsaro a baburan A Daidaita, musamman ƙwacen waya, na ci gaba da yawaita a jihohin Arewacin Nijeriya, har ta kai al’umma suna ɗaukar matakin kamawa da kuma duka, wani lokacin ma har da kisa na waɗanda aka kama da baburan suna ƙwace.

A watan Nuwambar 2022, kafafen watsa labarai da dama sun rawaito yadda aka yi amfani da bubur mai ƙafa uku wajen satar mutum a Jihar Katsina. Haka ma a shekarar 2023, inda rundunar ’yan sanda ta kama wasu matasa da ke amfani da nau’in baburin wajen aikata ƙwacen waya, sata, da ma kisa, musamman a jihohin Kano da Kaduna.

A Jihar Kano, rundunar ’yan sanda ta tabbatar da cewa a cikin watanni shida na 2024, an samu rahoton fashi sama da 400 da aka yi da babur ɗin.

Sai dai, duk da haka, yawan tsayawa jiran fasinjoji ya sa mutane da dama karkata ga A Daidaita.

Ra’ayin jama’ar gari

Isa Abubakar Goje ya ce shi ba ya iya hawa bas saboda yawancinsu ba su shiga cikin unguwanni sosai, kuma duk da haka za iya kashe kuɗi mai yawa kafin buƙatarsa ta biya.

“Misali ni da ke Ɗorayi, sai na sake biyan A Daidaita daga bakin titi. Farashin babu bambamci sosai da na ɗau A Daidaita kai tsaye zuwa gida. Ga shi na ɓata lokaci a hanya. To, gara kawai in biya sau ɗaya a kai ni akan lokaci.”

Amma ga wasu, kamar Hassan Musa Sharaɗa naganin mafita ita ce a dawo da bas, domin ci baya ne mutuwar sana’ar ko a ƙasashen da suka ci gaba.

“Gaskiya, idan gwamnati ta dawo da tsarin bas da tasi, za mu ji daɗi sosai. Bas ta fi arha kuma ba a cika jin rahoton satar mutane ko fashi ba. A kasashen da suka ci gaba ma. Bas ce a kan gaba wajen jigilar jama’a. Kuma nasu ma sun fi namu girma domin irin Macopolo ɗin nan ne da su jiragen ƙasa.

“Don haka raguwar bas a Kano ba matsala ce kawai ta sufuri ba, illa ce har ma ga tattalin arziki, tsaro, da walwalar jama’a.” in ji shi.

Yayin da A Daidaita ya kawo sauƙi da sauƙin shiga lungu da saƙo, tsadar rayuwa da barazanar tsaro na dabaibaye da shi.

A don haka ne ma ya sa al’umma ke kira ga gwamnati da hukumomi da su yi duba na tsanaki domin dawo da tsarin bas da ya fi araha, da tsaro domin samar wa da jama’a sauƙi a dadai wannan lokacin da ake fama da matsalolin tattalin arziki.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka

Kasashe hudu da suka fi kokari a cikin wadanda suka kare a mataki na hudu za su fafata wasannin raba-gardama, sai wadanda suka samu nasara su sake raba-gardama da wasu kasashen na waje.

 

A yanzu daI manyan kasashen nahiyar ta Afirka irin su Kamaru da Nijeriya suke fuskantar barazanar rasa gurbi, duk da haka suna da wasu damarmakin da idan suka yi sa’a za su iya tsintar kansu a gasar a badi.

 

Kasar Masar ta wuce Burkina Faso da maki biyar, sannan idan ta samu nasara a kan Djibouti shikenan ta samu tikiti. Ita kuma kasar Djibouti tana can karshen teburi ne, domin maki daya tak take da shi a wasa takwas da ta buga.

 

Idan ma Masar ta yi rashin nasara a wasan, za ta fatata da Guinea-Bissau a ranar Lahadi. Burkina Faso kuma wadda take kokarin zuwa ta biyu za ta buga wasa ne da kasar Saliyo, sai kuma kasar Habasha, amma tana bukatar samun nasara a wasannin kafin samun gurbin buga wasannin raba-gardama.

 

A rukunin (B) kuwa nasarar da Senegal ta samu a kan DR Congo ce ta ba ta damar darewa teburin rukunin, inda yanzu ta ba da tazarar maki daya. Tawagar ta Teranga Lions za ta je wasa da Sudan ta Kudu wadda ke karshen teburi, sai ta buga wasan karshe da Mauritania, inda take bukatar nasara biyu domin samun shiga gasar.

 

DR Congo dai na fatan Senegla ta yi rashin nasara, ita kuma ta samu nasara a wasannin biyu a gidan Togo da kuma Sudan a gida. Sudan na bukatar nasara a duka wasanninta, sannan Senegal ta yi rashin nasara wasanninta biyu domin samun gurbin zama ta daya a teburi, amma tana da damar zuwa ta biyu idan ta doke Congo.

 

A wannan rukunin kuma bayan hukuncin da FIFA ta dauka a kan kasar Afirka ta Kudu na cire mata maki uku saboda sanya dan wasan da bai cancanta ba a wasanta da kasar Lesotho.

 

Yanzu Benin ce kan gaba a rukunin, inda take saman Afirka ta Kudu da bambancin kwallaye, sai Nijeriya da Rwanda suke da maki da na hudu, amma duk suna da damar samun gurbi.

 

Benin na da wasa a gidan Rwanda da Nijeriya, sai tawagar Afirka ta Kudu za ta buga da Zimbabwe, sai Rwanda a gidanta. Nijeriya tana da wasa a gidan Lesotho sai Benin, kuma dole ne ta ci wasanninta guda biyu, amma ko da ta lashe wasannin, sai yadda ta wakana a sauran wasannin kafin sanin matsayarsa.

 

Nasarar da Cape Berde ta samu a kan Kamaru da ci daya mai ban haushi a watan jiya ta sa kasar ta kama hanyar kafa tarihin zuwa gasar cin Kofin Duniya na farko a tarihinta.

 

Yanzu kasar na bukatar nasara daya kacal a wasanta da Libya ko kuma a wasanta a gida da kasar da ke karshen teburi, wato tawagar ‘yan wasan kasar Eswatini. Kamaru za ta iya samun nasara da bambancin zura kwallaye idan ta doke Mauritus da Angola, ita kuma Cape Berde ta yi canjara a wasannin biyu, ko kuma idan Kamaru ta samu maki hudu a wasannin biyu,

 

ita kuma Cape Berde ta yi rashin nasara. Sai kuma Libya ce ta uku, kuma maki uku ne tsakaninta da Kamaru, kuma za ta iya bayar da mamaki.

 

Kasar Morocco ta riga ta samu gurbin shiga gasar cin kofin duniyar.

 

A cikin rukuni na E kuma kasashen Tanzania da Nijar da Zambia ne sauran kasashen da ke rukunin, kuma yanzu suna ta fafatawa ne domin samun gurbi na biyu wanda zai iya buga wasan raba-gardama.

 

A cikin rukuni na (F) kuwa, Ibory Coast na gaba da Gabon da maki daya bayan canjaras da ta yi da kasar Gabon a Francebille a watan Satumba. Kasar za ta je gidan Seychelles a ranar Juma’a, sai kuma ta fafata da Kenya a ranar Talata. Gabon za ta je gidan Gambia, sai kuma Burundi ta bakunce ta.

 

A cikin rukuni na G kuwa Algeria ita ma ta ba da tazarar maki hudu a saman teburi, kuma tana bukatar maki uku ne a wasanta da kasar Somalia wadda ta riga ta fita ko kuma ta biyu Uganda zai ta ba gurbi. Uganda ta zarce Mozambikue ne kawai da bambancin zura kwallo a matakin na biyu.

 

Can kuwa a cikin rukuni na H, Tunisia ta riga ta tsallake bayan samun gurbi duk da cewa akwai sauran wasaNNI biyu da za ta buga, inda ita kuma Namibia ta dage wajen neman zama ta biyu a rukunin. Namibia za ta je gidan Liberia a ranar Alhamis kafin ta karkare a birnin Tunis.

 

Daga rukuni na I kuma kasashe uku ne ke fafutikar samun gurbin na kai-tsaye, amma Ghana ce a sama da tazarar maki uku a saman Madagascar da Comoros. Ghana za ta samu gurbi idan ta yi nasara sannan Madagascar ta gaza samun maki uku. Wasan karshe na Ghana shi ne a gida da Comoros, ita kuma Madagacar za ta je gidan Mali a wasan na karshe.

 

Kamar yadda FIFA ta tsara, kasashe hudu da suka fi maki a cikin kasashen da suka kare a na biyu daga rukunoni tara din ne za su fafata wasannin raba-gardama a watan Nuwamba.

 

Zuwa yanzu dai kasashen Gabon da Madagascar da DR Congo da Burkina Faso ne a gaba a cikin tawagogi na biyu. Sakamakon za su iya canjawa bayan wasanni biyu na karshe, sannan kuma ba a riga an sanar da tsarin wasannin na raba-gardama ba.

 

Amma kasashen da suka samu nasara a wasannin na raba-gardama ne za su sake fafatawa a wasanin na raba-gardama da wasu kasashen na duniya kafin samun gurbi a gasar ta duniya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola October 12, 2025 Wasanni Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0 October 9, 2025 Wasanni Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane October 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza
  • Iran Ba Zata Halarci Zaman Taron Sharm El-Sheikh Ba Saboda Wasu Dalilai Da Ta Byyana
  • An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara