Leadership News Hausa:
2025-11-27@21:14:28 GMT

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

Published: 26th, September 2025 GMT

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

Wanda duk zai gaya maka gaskiya musamman wanda yake zaune ko ya ke zuwa wuraren da aka samu matsalar tsaro a wasu kananan hukumomi na jihar Katsina zai fada maka cewar an samu zaman lafiya fiye da lokutan baya.

An sha ruwaito wadanda wannan bala’i ya shafa suna maida martani ga masu suka sulhu da cewa duk wanda baya goyon bayan wannan sulhu dan ba a wannan yanki yake da zama ba.

Sai dai kuma yin sulhu da barayin daji ba yana nufin an samu zaman lafiya dari-bisa-dari ba. Ana dai samun saukin kai hare-haren ‘yan bindigar amma ba wai an daina ba ne baki daya.

To, ta ya ya al’umma za su amfana da wannan yarjejeniyar zaman sulhu da barayin daji, ana iya cewa hakan zai taimaka ta wajen huldar kasuwancin kiwo da kuma noma da ya fara zama tarihi a wasu wurare da ake wannan ta’addanci.

Idan aka duba salon da barayin daji suke amfani da shi bayan kaddamar da yarjejeniyar zaman sulhu shi ne, duk karamar hukumar da aka wannan sulhu to za su rage kai hare-hare Sannan za su sako wadanda suke tsare da su.

Haka kuma su kan kai hari ne a sauran kananan hukumomin da ba a kulla wannan yarjejeniya ta zaman lafiya da su ba, su yi barna su yi kisa su kwashe kayayyakin da jama’a.

Irin haka na ci gaba da faruwa, misali an yi zaman sulhu da barayin daji a karamar hukumar Kankara amma a satin da ya gabata rahotanni sun bayyana cewa an je an sace mutum 60 a garin Zango da Kankara.

Haka abin yake a karamar hukumar Faskari inda suka je garin Tafoki suka kwashe mashinan jama’a a ya yin da suke cikin gona suna aiki.

Sannan abubuwan da suka bayyana shine ana cigaba da kai hare-hare jefi-jefi kuma ana cigaba da satar jama’a da neman kudin fansa tare da sauran abubuwa marasa dad’i.

A bangaren barayin daji kuwa tuni harkoki suka fara kankama inda yanzu haka suke shigowa gari cin kasuwa da zuwa asibiti domin neman lafiyar su da ta iyalan su.

Ita ma gwamnatin jihar Katsina ta bada tabbacin cewa zata tallafawa wadanda wannan iftila’i ya shafa da jari da makarantu da asibitoci da sauran kayayyakin more rayuwa.

Gwamna Malam Dikko Umar Radda ya jaddada cewa hatta ‘yan bindigar da suka rungumi zaman lafiya za a taimaka masu da jari domin yin sana’a da za su dogara da kan su.

Gwamnan dai ya sha soka akan yadda rana tsaka ya yi mi’ara koma baya akan matsayar da ta cewa ba zai taba yin sulhu da barayin daji ba, sai dai idan ‘yan bindigar suka sha wuta suka mika kai.

Haka kuma daya daga hadiman gwamna Radda Jamilu Isma’il Mabai ya bayyana cewa ‘yan bindiga ne da kan su suka sha wuta daga jami’an tsaro suka nemi ayi sulhun ba gwamnati ba ce.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: sulhu da barayin daji zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna

Jami’an tsaro a Jihar Kaduna, sun fara gudanar da babban samame domin kawar da ’yan ta’adda da ’yan bindiga a wasu ƙananan hukumomin jihar.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce an gudanar da aikin tare haɗin gwiwar sojoji, DSS, NSCDC, KADVS, da kuma ƙungiyoyin sa-kai da mafarauta.

Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000

Aikin ya shafi ƙananan hukumomin Makarfi, Hunkuyi da Ikara.

Rundunar ta ce manufar wannan samame shi ne “share dukkanin maɓoyar miyagu, rushe sansanonin da suka kafa, da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.”

Wannan mataki ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, wanda ya umarci dukkanin rundunonin ’yan sanda a faɗin ƙasar nan su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da aikata laifuka.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Rabiu Muhammad, ya tabbatar wa jama’a cewa jami’an tsaro za su ci gaba da matsa wa miyagu lamba.

Ya ce za su ci gaba da yin gwiwa da rundunonin tsaro domin tabbatar da tsaro a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi