Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar
Published: 26th, September 2025 GMT
Shugaban a kasidar da ya gabatar a wajen taron mai taken: “Ingantattun Sauye-Sauyen da Nijeriya ta kirkiro da su domin cin gajiyar albarkatun da ke a Man Fetur da Iskar Gas”, ya jaddada mahimmancin da ke a fannin Makamashi, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasa da kuma yadda Afirka, za ta amfana.
Ya ci gaba da cewa, sabon sauyen da aka samar a kasar nan a karkashin dokar Masana’antar Man Fetur ta 2021 ta samar da sabon sauyi, a bangaren gudanar da shugabanci na gari.
Shugaban ya kara da cewa, Hukumar musamman a karkashin shugabancin shugaba Tinubu, ta kara zagayewa wajen sanya ido sosai a fannin na sarrafa Mai da Iskar Gas.
Ya ce, Hukumar kusana a cikin shekaru hudu da suka gabata, ta samar da sabbin ka’idoji sanya ido guda 24 a fannin sarrafa Mai da Iskar Gas, inda ya zuwa yanzu, guda 19, aka sanya su a cikin kundin gudanar da ayyuka.
A cewarsa, Hukumar ta kuma kaddamar da cikakken shiri na RAP, wanda ya yi daidai da tsarin dokar ta Masana’antar Man Fetur ta 2021, wanda hakan ya taimaka wajen magance kalubalen da ake fuskanta da kuma tabbatar da ana samar sa Lasisi, a cikin sauki.
Ya kara da cewa, an samu sakamako mai kyau a shirye-shiryen da Hukumar ta kirkiro da su, inda Jaren Ruwan dakon Man suka karu daga takwa zuwa 43 daga watan Satumbar 2021 zuwa watan Satumbar 2025.
“A 2025 kadai Hukumar ta amince da sabbin ayyukan bunkasa FDP guda 28 domin a ci gajiyar gangunan Mai miliyan 1.4 da kuma Iskar Gas 5.4, inda kuma ake sa ran samun gangunan Mai guda 591,000 a kullum da kuma karin wani Iskar Gas 2.1,” A cewarsa.
“Wannan ayyukan na FDP wanda ya kai na dala biliyan 18.2 hakan ya nuna kokarin da ake yin a janyo masu zuba hannun jari a fannin hako da Man na kan Tudu,” Inji Shugaban.
Ya kara da cewa, sauran sun hada da, aikin dala biliyan biyar na FID wanda ake gudanarwa a arewacin Bonga da kuma aikin dala miliyan 500 na Gas da ake yi a yankin Ubeta tare da kuma karin wani akin ne FID kamar na yankunan Ima Gas, Owowo da kuma na Preowei.
Ya ci gaba da cewa, bayan da shugaba Tinubu ya zama shugaban kasa, ya amince da wasu manyan ayyuka guda biyar da suka kai na sama da dala biliyan biyart, wanda hakan ya kara bayar da dama ga masu ruwa da tsaki, na cikin gida da ke a fannin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: da Iskar Gas
এছাড়াও পড়ুন:
Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
’Yan wasan tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya ta Mata, Super Falcons, sun yi barazanar ƙaurace wa wasannin sada zumunta da Najeriya za ta buga a watan Disamba mai kamawa.
’Yan wasan sun ce za su ƙaurace wa wasannin ne idan har Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta ci gaba da jinkirta biyan kuɗaɗen alawus-alawus da suke biyo tun na Gasar Olympics da aka yi a birnin Paris a 2024.
Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaroWasu majiyoyi daga ƙungiyar sun tabbatar cewa ’yan wasan na ci gaba da jiran a biya su haƙƙoƙinsu na wasannin da suka buga, ciki har da alawus na nasarar da suka samu a gasar Olympics, duk da cewa Najeriya ta fice tun a matakin rukuni bayan shan kashi a hannun Brazil da Spain da Japan.
Wani jami’in tawagar, wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya ce ’yan wasan gaba ɗaya sun amince cewa ba za su halarci kowanne wasa ba muddin ba a biya su haƙƙoƙinsu ba.
Ana sa ran Najeriya za ta buga jerin wasannin sada zumunta daga ranar 2 zuwa 10 ga watan Disamba, a wani ɓangare na shirye-shiryen Super Falcons domin tunkarar gasar cin Kofin Afrika ta Mata na 2026.
A halin yanzu, NFF ba ta fitar da jerin sunayen ’yan wasan da za su wakilci Najeriya a wasannin ba.