Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar
Published: 26th, September 2025 GMT
Shugaban a kasidar da ya gabatar a wajen taron mai taken: “Ingantattun Sauye-Sauyen da Nijeriya ta kirkiro da su domin cin gajiyar albarkatun da ke a Man Fetur da Iskar Gas”, ya jaddada mahimmancin da ke a fannin Makamashi, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasa da kuma yadda Afirka, za ta amfana.
Ya ci gaba da cewa, sabon sauyen da aka samar a kasar nan a karkashin dokar Masana’antar Man Fetur ta 2021 ta samar da sabon sauyi, a bangaren gudanar da shugabanci na gari.
Shugaban ya kara da cewa, Hukumar musamman a karkashin shugabancin shugaba Tinubu, ta kara zagayewa wajen sanya ido sosai a fannin na sarrafa Mai da Iskar Gas.
Ya ce, Hukumar kusana a cikin shekaru hudu da suka gabata, ta samar da sabbin ka’idoji sanya ido guda 24 a fannin sarrafa Mai da Iskar Gas, inda ya zuwa yanzu, guda 19, aka sanya su a cikin kundin gudanar da ayyuka.
A cewarsa, Hukumar ta kuma kaddamar da cikakken shiri na RAP, wanda ya yi daidai da tsarin dokar ta Masana’antar Man Fetur ta 2021, wanda hakan ya taimaka wajen magance kalubalen da ake fuskanta da kuma tabbatar da ana samar sa Lasisi, a cikin sauki.
Ya kara da cewa, an samu sakamako mai kyau a shirye-shiryen da Hukumar ta kirkiro da su, inda Jaren Ruwan dakon Man suka karu daga takwa zuwa 43 daga watan Satumbar 2021 zuwa watan Satumbar 2025.
“A 2025 kadai Hukumar ta amince da sabbin ayyukan bunkasa FDP guda 28 domin a ci gajiyar gangunan Mai miliyan 1.4 da kuma Iskar Gas 5.4, inda kuma ake sa ran samun gangunan Mai guda 591,000 a kullum da kuma karin wani Iskar Gas 2.1,” A cewarsa.
“Wannan ayyukan na FDP wanda ya kai na dala biliyan 18.2 hakan ya nuna kokarin da ake yin a janyo masu zuba hannun jari a fannin hako da Man na kan Tudu,” Inji Shugaban.
Ya kara da cewa, sauran sun hada da, aikin dala biliyan biyar na FID wanda ake gudanarwa a arewacin Bonga da kuma aikin dala miliyan 500 na Gas da ake yi a yankin Ubeta tare da kuma karin wani akin ne FID kamar na yankunan Ima Gas, Owowo da kuma na Preowei.
Ya ci gaba da cewa, bayan da shugaba Tinubu ya zama shugaban kasa, ya amince da wasu manyan ayyuka guda biyar da suka kai na sama da dala biliyan biyart, wanda hakan ya kara bayar da dama ga masu ruwa da tsaki, na cikin gida da ke a fannin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: da Iskar Gas
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
Al’ummomin dake garin Warwade da kewaye a karamar hukumar Dutse ta jihar Jigawa sun yi kira ga gwamnatin jihar da ta yashe madatsar ruwa ta Warwade wanda ta kasance daya daga cikin hanyar samun aikin dogaro da kai ga Mazauna yankin.
Wakilinmu Usman Mohammed Zaria ya ziyarci al’ummomin da ke zaune a kusa da mmadatsr ruwan wanda aka gina ta sama da shekaru hamsin da suka gabata.
Madatsar ruwan ta Warwade ta kasance hanyar samun sana’o’in dogaro da kai ga mazauna yankin, wadanda suke kamun kifi da noman rani domin samun na yau da kullum.
Malam Umar Sani, wanda masunci ne a Warwade, yace da abin da yake samu daga kamun kifi yake kula da iyalan shi da kuma sauran bukatun yau da kullum.
Yace ana samun ribar kimanin naira dubu goma zuwa ashirin a kowace rana daga siyar da kifin ga matafiya da kuma baki masu kai ziyara garin.
A don haka, Umar yayi kira ga gwamnatin jihar Jigawa da ta yi yashen madatsar ruwan saboda a samu karin kifaye da kuma ruwa da za a iya amfani da shi domin noman rani.
Shi ma a yayin tattaunawa da Dagacin Warwade, Malam Musa Ado, ya ce madatsar ruwan tana samar da ayyukan yi ga matasan yankin, tare da hana tafiya zuwa cirani a sauran yankunan kasar nan da sunan yin sana’o’i.
Ya ce matasan yankin suna gudanar da sana’ar kamun kifi da kuma nomar rani da ta damina.
Sai dai kuma, Malam Musa ya koka kan rashin samar da injinan noman rani da kuma Malaman gona kamar yadda ake yi a gwamnatocin baya.
Kazalika, yace a ‘yan kwanakin baya gwamnatin jihar Jigawa ta kai ziyara kauyen inda ta sanar da cewar Bankin duniya zai samar da wasu kudade ta hannun gwamnatin tarayya wanda za’a baiwa gwamnatocin jihohi domin yashewa tare da gina burtuloli da hanyoyin noman rani.
Bisa haka ne dagacin yayi kira ga gwamnatin jihar da ta fara yin garambawul a madatsar ruwan domin a baiwa mazauna yankunan damar amfani da shi.
A shekarun baya dai, gwamnatin jihar Jigawan ta samar da irin kifaye guda dubu Dari uku domin inganta samar da kifi a yankin.
Usman Mohammed Zaria