Aminiya:
2025-10-13@15:47:18 GMT

Naɗin Olubadan: Tinubu da manyan jami’ai sun ziyarci Ibadan

Published: 26th, September 2025 GMT

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci birnin Ibadan, a yau Juma’a domin halartar bikin miƙa sandar sarauta ga sabon Olubadan na Ibadan, Oba Rashid Adewolu Ladoja na 44 da ake kan gudanarwa yanzu haka.

Shugaba Tinubu da tawagarsa sun sauka a filin jiragen sama na Ladoke Akintola da ke Ibadan ne da misalin ƙarfe 1:30 PM na rana inda Gwamna Seyi Makinde na Jihar Oyo ya yi masa maraba.

Yadda ’yan haya za su samu ragin N500,000 a shekara  Babu wata jam’iyya dana ke shirin komawa — Kwankwaso

Aminiya ta ruwaito cewa, tun kafin isowar Shugaba Tinubu aka fara gudanar da bukukuwan al’adun gargajiya da suka danganci miƙa sandar sarauta ga sabon Olubadan Oba Rashid Adewolu Ladoja.

Juma’a a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo ya samu halartar manyan mutane da suka haɗa da Sarakuna da tsofaffin Gwamnoni da wakilan Majalisun Tarayya daga Jihohi daban daban na ƙasa.

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar IIIda Alaafin na Oyo Oba, Abimbola Owoade da Soun na Ogbomoso Oba Ghandi Afolabi Olaoye suna daga cikin manyan Sarakunan da suka bayyana a zauren taro na Mapo da ke tsakiyar birnin Ibadan, inda ake yin wannan taro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Oba Rashid Adewolu Ladoja

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Na farko, hada kai don samar da yanayi mai kyau ga ci gaban mata. Na biyu, a karfafa abubuwan da za su habaka ingancin ayyukan mata cikin hadin kai. Kana na uku, a gina tsarin kare hakkin mata tare. Sai na hudu, a bude sabon babin hadin gwiwa tsakanin mata a duniya.

 

Za a gudanar da taron kolin mata na duniya a yau da gobe Talata a birnin Beijing. Kuma tuni shugaban kasar Sin Xi Jinping da uwargidansa Peng Liyuan, suka yi musafaha da shugabannin tawagogin kasashe, da kungiyoyin duniya da suka halarci taron, tare da daukar hotuna tare da su. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina October 12, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth October 12, 2025 Daga Birnin Sin An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
  • Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
  • Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata