Aminiya:
2025-11-27@21:54:58 GMT

Gwamnatin Kebbi ta sake jaddada goyon bayanta ga hukumomin tsaro

Published: 26th, September 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Kebbi ta sake jaddada ƙudirinta na ci gaba da tallafawa dukkan hukumomin tsaro da ke yaƙar ’yan bindiga da ta’addanci a jihar.

Kwamishinan yaɗa labarai da al’adu na Jihar, Alhaji Yakubu Ahmed Birnin Kebbi, ne ya tabbatar da hakan lokacin da ya tarbi Daraktan Yaɗa Labaran Sojoji, Birgediya Janar T.

I. Gusau, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa da ke Birnin Kebbi.

Naɗin Olubadan: Tinubu da manyan jami’ai sun ziyarci Ibadan Sojoji sun kashe ’yan ta’adda tare da ƙwato makamai a Neja

Alhaji Yakubu ya bayyana irin muhimman tallafin da Gwamna Nasir Idris ke bayarwa tun daga lokacin da ya fara mulki shekaru biyu da suka gabata, wanda ya haɗa da kayayyakin aiki da alawus da kuma bayanan sirri ga jami’an tsaro.

Ya ce, gwamnatin za ta ci gaba da ɗaukar nauyi domin ƙara ƙarfafa ƙoƙarin yaƙi da ’yan bindiga.

Ya kuma shawarci hidikwatar tsaro da ta shirya taron tattaunawa tare da manyan masu ruwa da tsaki kamar sarakunan gargajiya da shugabannin addini da shugabannin al’umma da ƙungiyoyin matasa domin samar da haɗin kai da zai taimaka wajen samar da bayanan sirri ga jami’an tsaro.

Kwamishina ya ƙara da cewa, ma’aikatarsa a shirye take ta yi aiki tare da sashen yaɗa labaran sojoji wajen shirya wannan taro, domin amfani da tasirin shugabannin gargajiya wajen samun goyon bayan jama’a.

A nasa jawabin, Birgediya Janar Gusau ya shaida wa Kwamishinan cewa, ya zo jihar tare da tawagarsa domin ganin tasirin haɗin gwiwar da suka shiga da wasu kafafen yaɗa labarai, wanda manufarsa ita ce ƙarfafa dangantaka tsakanin sojoji da al’umma wajen yaƙi da ’yan bindiga a Jihar Kebbi da ma Arewa maso Yamma baki ɗaya.

Ya jaddada muhimmancin haɗin kai tsakanin jami’an tsaro da jama’a a dukkan wuraren da ake yaƙi da miyagun laifuka.

Haka kuma, ya yaba wa Gwamna Nasir Idris bisa irin goyon bayan da yake bayarwa ga rundunar sojoji, yana mai cewa hakan ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarorin da aka samu har zuwa yanzu.

Birgediya Janar Gusau ya kuma isar da saƙon godiyar babban hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Christopher Musa, ga Gwamnatin Jihar Kebbi bisa jajircewarta wajen ganin an dawo da zaman lafiya a Jihar Kebbi musamman da kuma yankin Arewa maso Yamma baki ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Kebbi

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Gombe ta ƙaddamar da sabbin matakan ƙarfafa tsaro a makarantu bayan wani taron tattaunawa da aka gudanar tsakanin Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar, Bello Yahaya, da shugabannin Ƙungiyar Malaman Sakandare reshen jihar.

An gudanar da taron ne a Hedikwatar Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Gombe, bisa umarnin Sufeton ’Yan Sanda na Ƙasa, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, na ƙara tsaurara tsaro a makarantu a faɗin ƙasar nan.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya bayyana cewa tattaunawar ta mayar da hankali kan duba tsarin tsaro na yanzu a makarantu, musamman waɗanda ke yankunan da ke da ƙalubale, tare da gano wuraren da ake buƙatar gaggawar gyara.

CP Bello Yahaya ya tabbatar da kudirin Rundunar ’Yan Sanda ta Najeriya na ci gaba da kare cibiyoyin ilimi, yana mai cewa makarantu dole ne su kasance wurare masu aminci domin koyo da koyarwa.

Ya jaddada muhimmancin yin nazarin tsaro a kai a kai, tsara matakan rigakafi, da kuma tabbatar da ci-gaba da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin makarantu, Ma’aikatar Ilimi da hukumomin tsaro.

Kwamishinan ya bayyana cewa rundunar ta ƙara karfafa sintiri, sa ido, da kuma gaggawar amsa kira a yankunan makarantu da aka fi ganin haɗarin tsaro.

Ya kuma bukaci shugabannin makarantu su riƙa kasancewa a shirin tuntuɓar ofisoshin ’yan sanda mafi kusa, tare da hanzarta ba da rahoton duk wani abin da ya haifar da zargi.

Ya yaba wa shugabannin ANCOPSS bisa jajircewarsu wajen aiki tare da hukumar ’yan sanda domin ƙarfafa tsaro a makarantu.

A nasu ɓangaren, shugabannin ANCOPSS sun gode wa rundunar ’yan sanda bisa ƙoƙarin da take yi na tabbatar da lafiyar dalibai da malamai, tare da alƙawarin yin aiki kafada da kafaɗa da rundunar da Ma’aikatar Ilimi domin ƙarfafa duk tsare-tsaren tsaro a makarantun sakandare.

Rundunar ta kuma yi kira ga iyaye, malamai, shugabannin al’umma, da mazauna unguwanni da su kasance masu lura da faɗakarwa, tare da tallafa wa duk wani yunƙurin inganta tsaro a makarantu, domin kiyaye rayuwar ɗalibai nauyi ne da ya rataya a kan kowa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe