Aminiya:
2025-10-13@17:45:10 GMT

Gwamnatin Kebbi ta sake jaddada goyon bayanta ga hukumomin tsaro

Published: 26th, September 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Kebbi ta sake jaddada ƙudirinta na ci gaba da tallafawa dukkan hukumomin tsaro da ke yaƙar ’yan bindiga da ta’addanci a jihar.

Kwamishinan yaɗa labarai da al’adu na Jihar, Alhaji Yakubu Ahmed Birnin Kebbi, ne ya tabbatar da hakan lokacin da ya tarbi Daraktan Yaɗa Labaran Sojoji, Birgediya Janar T.

I. Gusau, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa da ke Birnin Kebbi.

Naɗin Olubadan: Tinubu da manyan jami’ai sun ziyarci Ibadan Sojoji sun kashe ’yan ta’adda tare da ƙwato makamai a Neja

Alhaji Yakubu ya bayyana irin muhimman tallafin da Gwamna Nasir Idris ke bayarwa tun daga lokacin da ya fara mulki shekaru biyu da suka gabata, wanda ya haɗa da kayayyakin aiki da alawus da kuma bayanan sirri ga jami’an tsaro.

Ya ce, gwamnatin za ta ci gaba da ɗaukar nauyi domin ƙara ƙarfafa ƙoƙarin yaƙi da ’yan bindiga.

Ya kuma shawarci hidikwatar tsaro da ta shirya taron tattaunawa tare da manyan masu ruwa da tsaki kamar sarakunan gargajiya da shugabannin addini da shugabannin al’umma da ƙungiyoyin matasa domin samar da haɗin kai da zai taimaka wajen samar da bayanan sirri ga jami’an tsaro.

Kwamishina ya ƙara da cewa, ma’aikatarsa a shirye take ta yi aiki tare da sashen yaɗa labaran sojoji wajen shirya wannan taro, domin amfani da tasirin shugabannin gargajiya wajen samun goyon bayan jama’a.

A nasa jawabin, Birgediya Janar Gusau ya shaida wa Kwamishinan cewa, ya zo jihar tare da tawagarsa domin ganin tasirin haɗin gwiwar da suka shiga da wasu kafafen yaɗa labarai, wanda manufarsa ita ce ƙarfafa dangantaka tsakanin sojoji da al’umma wajen yaƙi da ’yan bindiga a Jihar Kebbi da ma Arewa maso Yamma baki ɗaya.

Ya jaddada muhimmancin haɗin kai tsakanin jami’an tsaro da jama’a a dukkan wuraren da ake yaƙi da miyagun laifuka.

Haka kuma, ya yaba wa Gwamna Nasir Idris bisa irin goyon bayan da yake bayarwa ga rundunar sojoji, yana mai cewa hakan ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarorin da aka samu har zuwa yanzu.

Birgediya Janar Gusau ya kuma isar da saƙon godiyar babban hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Christopher Musa, ga Gwamnatin Jihar Kebbi bisa jajircewarta wajen ganin an dawo da zaman lafiya a Jihar Kebbi musamman da kuma yankin Arewa maso Yamma baki ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Kebbi

এছাড়াও পড়ুন:

A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato

Tukur Muhammad Fakum, daya daga cikin jagororin al’ummar ya shaida wa BBC cewa an riga an kai makura, don haka a yanzu fatan su kawai bai wuce neman wa kai mafita ba.

 

Ya ce ”Mu yanzu muna nan muna gangami, mai ‘yar karamar gona ya sayar, mai dan karamin gida ya sayar, in muka sayi bindigogi a ba matasa su ma su yi kokari su kare mu.

 

”Gwamnati ta ba mu kariya, idan kuma ba ta iyawa to ta bamu makamai a ba matasa, su matasa na iya kare rayukansu da garuruwan su,” in ji Tukur Muhammad Fakum.

Dangane da halin da irin barnar da ‘yan bindigar suka yi masu kuwa, Tukur Muhammad Fakum ya ce ”Babu dai abinci, wanda bai taba kwana masallaci ba ya yi, ka tashi ka tafi garin da ba ka taba kwana ba, ka kwana dole. Bala’in ya baci.”

Ya kuma ce lamarin rusa kusa duk wata harkar tattalin arziki a yankin.

BBC dai ta yi kokari jin halin da ake ciki daga bangaren gwamnati da jami’an tsaro, amma hakan ba ta samu ba.

Jihar Sokoto na daga cikin jihohin da matsalar ‘yan bindiga ta addaba sosai a shekarun nan, inda suke aikata barna, musamman a kananan hukumomin Isa da Sabon Birni da kuma Kebbe.

Bayan ‘yan bindiga masu biyayya ga Bello Turji da suke ayyukan su a jihar, an kuma samu bulluwar mayakan Lakurawa, wata sabuwar kungiyar da masu sharhi a kan harkokin tsaro ke gargadin cewa za ta iya zama sabuwar annoba ga jihar da ma yankin Arewa maso Yamma baki daya.

A jihar Kebbi da ke makwabtaka da Sokoto ma wasu ‘yan bindigar sun kai hari a kan jami’an tsaro, a Garin Dirin Daji da ke Karamar Hukumar Sakaba ta jihar.

Wata mazauniyar garin ta ce ”Sun kai hari a kan sansanin sojoji da na ‘yansanda, wanda ke gadi a sansanin sojojin sun harbe shi, kuma nan take Allah ya mashi cikawa.”

Ta kara da cewa ”Daga baya an turo jami’an tsaro, wadanda suka kawo dauki cikin gaggawa, kuma da alama kura ta lafa.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno October 11, 2025 Tsaro Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe October 11, 2025 Tsaro Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida