Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Neja
Published: 26th, September 2025 GMT
Dakarun rundunar sojoji ta 22 Armored Brigade da ke aiki a ƙarƙashin Operation Park Strike V tare da haɗin gwiwar Jami’an tsaron gandun daji sun kashe wasu ’yan ta’adda da ba a tantance adadinsu ba a dajin Kainji da ke Ƙaramar hukumar Borgu a Jihar Neja.
Hakazalika an samu nasarar ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda 3 da babura 4 daga hannun maharan.
Muƙaddashin Daraktan hulɗa da jama’a na rundunar soji ta 22 da ke Ilorin, Captain Stephen Nwankwo, a wata sanarwa ne ya tabbatar da faruwar lamarin ya kuma ce, ɗaya daga cikin jami’an da suke kula da gandun dajin yankin ya samu raunuka a harbin bindiga, amma ya fara samun sauƙi.
Wannan farmakin na daga cikin ƙoƙarin da ake yi na samar da tsaro a dajin Kainji (KLNP) daga wuraren da ke da ’yan tada ƙayar baya.
Ya ƙara da cewa, an samu nasarar ne a safiyar ranar Alhamis 25 ga watan Satumba, 2025, lokacin da jami’an tsaro na haɗin gwiwa suka yi wa ’yan tada ƙayar bayan kwanton ɓauna a dajin Kainji.
Ya ce, “A ci gaba da ƙoƙarin da ake na samar da tsaro a dajin Kainji (KLNP) daga miyagu da ke haddasa rashin tsaro a yankin, sojojin na 22 Armored Brigade, da ke aiki a ƙarƙashin Operation Park Strike Ɓ, tare da jami’an gandun dajin Park Rangers, sun gudanar da wani samame na kwantan ɓauna a safiyar ranar Alhamis, 25 ga Satumba, 2025.
“A bisa sahihan bayanan sirri, sojojin sun yi kwanton ɓauna a mashigar ’yan tada ƙayar bayan a Tungan Talle, Sashen Zugurma na wurin shaƙatawa da misalin ƙarfe 1:15 na safe.
“A yayin arangamar, sojojin sun yi artabu da ’yan ta’addan da musayar wuta, inda suka kashe wasu da ba a tabbatar da adadinsu ba, yayin da wasu suka samu raunuka, inda suka samu nasarar ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda 3 da kuma babura 4.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
A cikin shekarun nan, matsalolin tsaro a Najeriya—kamar ta’addanci, da garkuwa da mutane, da rikicin manoma da makiyaya, da kuma ayyukan ’yan bindiga—suna kara ta’azzara, lamarin da ya sanya al’umma da masana tsaro ke tambayar wace hanya ta fi dacewa gwamatani ta yi amfani da shi wajen kawo karshen wadannan matsaloli da suka ki ci suka ki cinyewa tsawon shekaru.
Yayin da wasu ke ganin amfani da karfin soji ne kadai hanyar da zai kawo karshen wannan matsala, wasu na ganin tattaunawa ne kadai mafita, wasu har ila yau na ganin idan aka yi amfani da gaurayen biyun zai fi dacewa.
NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?Ko wanne daga cikin wadannan hanyoyi ne idan gwamnati ta yi amfai dashi ko da su don magance wannan matsala?
Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan