Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Neja
Published: 26th, September 2025 GMT
Dakarun rundunar sojoji ta 22 Armored Brigade da ke aiki a ƙarƙashin Operation Park Strike V tare da haɗin gwiwar Jami’an tsaron gandun daji sun kashe wasu ’yan ta’adda da ba a tantance adadinsu ba a dajin Kainji da ke Ƙaramar hukumar Borgu a Jihar Neja.
Hakazalika an samu nasarar ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda 3 da babura 4 daga hannun maharan.
Muƙaddashin Daraktan hulɗa da jama’a na rundunar soji ta 22 da ke Ilorin, Captain Stephen Nwankwo, a wata sanarwa ne ya tabbatar da faruwar lamarin ya kuma ce, ɗaya daga cikin jami’an da suke kula da gandun dajin yankin ya samu raunuka a harbin bindiga, amma ya fara samun sauƙi.
Wannan farmakin na daga cikin ƙoƙarin da ake yi na samar da tsaro a dajin Kainji (KLNP) daga wuraren da ke da ’yan tada ƙayar baya.
Ya ƙara da cewa, an samu nasarar ne a safiyar ranar Alhamis 25 ga watan Satumba, 2025, lokacin da jami’an tsaro na haɗin gwiwa suka yi wa ’yan tada ƙayar bayan kwanton ɓauna a dajin Kainji.
Ya ce, “A ci gaba da ƙoƙarin da ake na samar da tsaro a dajin Kainji (KLNP) daga miyagu da ke haddasa rashin tsaro a yankin, sojojin na 22 Armored Brigade, da ke aiki a ƙarƙashin Operation Park Strike Ɓ, tare da jami’an gandun dajin Park Rangers, sun gudanar da wani samame na kwantan ɓauna a safiyar ranar Alhamis, 25 ga Satumba, 2025.
“A bisa sahihan bayanan sirri, sojojin sun yi kwanton ɓauna a mashigar ’yan tada ƙayar bayan a Tungan Talle, Sashen Zugurma na wurin shaƙatawa da misalin ƙarfe 1:15 na safe.
“A yayin arangamar, sojojin sun yi artabu da ’yan ta’addan da musayar wuta, inda suka kashe wasu da ba a tabbatar da adadinsu ba, yayin da wasu suka samu raunuka, inda suka samu nasarar ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda 3 da kuma babura 4.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
Ya bayyana cewa an riga an hada wadanda aka ceto da iyalansu, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike da aikin ceton domin gano wadanda suka aikata laifin da kuma kubutar da sauran wadanda ake tsare da su, idan suna nan.
A halin da ake ciki kuma, kwamandan Runduna ta 6 ta Sojan Nijeriya, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba da saurin daukar mataki da hadin kai tsakanin sojoji da ‘yansanda wanda ya kai ga nasarar aikin ceton.
Ya sake jaddada kudirin rundunar wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a Jihar Taraba.
Sai dai, ya bukaci jama’a da su ci gaba da bai wa sojoji da sauran hukumomin tsaro goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai a kan lokaci domin taimaka wa a ayyukan tsaro da ake gudanarwa a fadin jihar.
A wani labari mai nasaba da haka, Kungiyar Matan Sojoji da ‘Yansanda (DEPOWA) ta yaba da jajircewa da sadaukarwar dakarun rundunonin sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaro, wadanda ke ci gaba da sadaukar da rayuwarsu domin kare kasar.
Kungiyar ta kuma yi addu’a ga Allah domin kare mazajensu, wadanda ke kwana suna tashi a kan bakin aiki domin tabbatar da tsaron ‘yan Nijeriya.
Shugabar kungiyar DEPOWA, kuma matar Babban Hafsan Tsaro na Kasa (CDS), Mrs. Oghogho Musa, ta bayyana wannan godiya tare da yin addu’o’i a birnin Abuja yayin gudanar da wasan motsa jiki na rawa (Dance Aerobics Edercise) da aka gudanar a makarantar DEPOWA da ke sansanin Mogadishu.
Shugabar DEPOWA ta kuma jaddada kudirin kungiyar na gudanar da yakin addu’a da godiya na tsawon shekara guda ga dakarun da ke bakin daga, domin nuna yabo da godiya ga jajircewarsu wajen kare kasar Nijeriya, duk da hadarin da ke tattare da aikin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA