Babu wata jam’iyya dana ke shirin komawa — Kwankwaso
Published: 26th, September 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa ya aike wasiƙar neman shiga wata jam’iyya ta daban.
A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso ya ce babu gaskiya a labaran, kuma ya shawarci jama’a da su yi watsi da su.
’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a Masallaci a Zamfara Ganduje ya gindaya wa Kwankwaso sharadin shiga APC“Mun samu bayanin wasu rubuce-rubucen da ke yawo a Intanet cewa mun miƙa wasiƙar neman shiga wata jam’iyya a ƙasar nan.
“Muna so mu fayyace wa jama’a cewa ba mu taɓa miƙa irin wannan wasiƙa ga kowace jam’iyya ba.
“Saboda haka mun shawarci jama’a da su riƙa neman duk wani bayani game da mu daga shafukanmu na gaskiya,” in ji shi.
Wannan na zuwa ne daidai lokacin da ake ta hasashen komawar Kwankwaso jam’iyyaar APC kafin zaɓen 2027.
Aminiya ta ruwaito cewa akwai alamun cewa Kwankwaso ya tattauna da Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, kan yiwuwar komawa jam’iyyar mai mulki.
Majiyoyi daga APC a Jihar Kano, sun yi iƙirarin cewa Kwankwaso ya aike wa sakatariyar jam’iyyar a Abuja wasiƙa, inda ya bayyana ƙudirinsa na sake shiga jam’iyyar.
Amma Aminiya ba ta tabbatar da wannan batu ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
Sai dai wata majiya daga sakatariyar APC a Abuja, ta ce Kwankwaso da shugaban jam’iyyar na ƙasa sun daɗe suna tattaunawa kan shirin sauya sheƙarsa, kuma shirye-shiryen sun yi nisa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwankwaso labaran ƙarya martani raɗi Sauya Sheƙa
এছাড়াও পড়ুন:
Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
‘Yan sa’o’i kafin sanarwar da Jam’iyyar ta RN ta yi ne dai, tsohon Firaministansa Edouard Philippe ya ce yana goyon bayan shirya sabon zaben shugaban kasa a gaggauce.
Wannan matsin lamba dai kari ne kan wadda shugaban na Faransa ke fusakanta daga bangaren masu sassaucin ra’ayi, wadanda su kuma bukatarsu ita ce a zabi sabon Firaminista daga cikinsu.
Sai dai a iya cewa akwai ragowar fatan kawo karshen rudanin da siyasar Faransar ta shiga, la’akari da bayanan da suka ce a dazu an shiga tattaunawa tsakanin jagoran jam’iyyar masu ra’ayin ‘yan mazan jiya Bruno Retailleau da Firaminista Lecournu, kwana guda bayan murabus din da ya yi. Yayin da kuma a gefe guda rahotanni suka ce a gobe Laraba wakilan masu sassaucin ra’ayi na jam’iyyar Socialist za su gana da Firaminista Lecournun mai murabus.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA