Aminiya:
2025-11-27@22:19:27 GMT

Babu wata jam’iyya dana ke shirin komawa — Kwankwaso

Published: 26th, September 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa ya aike wasiƙar neman shiga wata jam’iyya ta daban.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso ya ce babu gaskiya a labaran, kuma ya shawarci jama’a da su yi watsi da su.

’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a Masallaci a Zamfara Ganduje ya gindaya wa Kwankwaso sharadin shiga APC

“Mun samu bayanin wasu rubuce-rubucen da ke yawo a Intanet cewa mun miƙa wasiƙar neman shiga wata jam’iyya a ƙasar nan.

“Muna so mu fayyace wa jama’a cewa ba mu taɓa miƙa irin wannan wasiƙa ga kowace jam’iyya ba.

“Saboda haka mun shawarci jama’a da su riƙa neman duk wani bayani game da mu daga shafukanmu na gaskiya,” in ji shi.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da ake ta hasashen komawar Kwankwaso jam’iyyaar APC kafin zaɓen 2027.

Aminiya ta ruwaito cewa akwai alamun cewa Kwankwaso ya tattauna da Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, kan yiwuwar komawa jam’iyyar mai mulki.

Majiyoyi daga APC a Jihar Kano, sun yi iƙirarin cewa Kwankwaso ya aike wa sakatariyar jam’iyyar a Abuja wasiƙa, inda ya bayyana ƙudirinsa na sake shiga jam’iyyar.

Amma Aminiya ba ta tabbatar da wannan batu ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Sai dai wata majiya daga sakatariyar APC a Abuja, ta ce Kwankwaso da shugaban jam’iyyar na ƙasa sun daɗe suna tattaunawa kan shirin sauya sheƙarsa, kuma shirye-shiryen sun yi nisa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwankwaso labaran ƙarya martani raɗi Sauya Sheƙa

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna

Jami’an tsaro a Jihar Kaduna, sun fara gudanar da babban samame domin kawar da ’yan ta’adda da ’yan bindiga a wasu ƙananan hukumomin jihar.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce an gudanar da aikin tare haɗin gwiwar sojoji, DSS, NSCDC, KADVS, da kuma ƙungiyoyin sa-kai da mafarauta.

Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000

Aikin ya shafi ƙananan hukumomin Makarfi, Hunkuyi da Ikara.

Rundunar ta ce manufar wannan samame shi ne “share dukkanin maɓoyar miyagu, rushe sansanonin da suka kafa, da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.”

Wannan mataki ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, wanda ya umarci dukkanin rundunonin ’yan sanda a faɗin ƙasar nan su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da aikata laifuka.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Rabiu Muhammad, ya tabbatar wa jama’a cewa jami’an tsaro za su ci gaba da matsa wa miyagu lamba.

Ya ce za su ci gaba da yin gwiwa da rundunonin tsaro domin tabbatar da tsaro a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia