Leadership News Hausa:
2025-10-13@17:47:12 GMT

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

Published: 25th, September 2025 GMT

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

Daga nan sai ya jaddada aniyar Sin, ta ci gaba da goyon bayan matsayi da ikon MDD, tare da mara baya ga sassan kasa da kasa wajen cimma nasarar amfani da dandalin MDDr a matsayin fagen karfafa shawarwari da hadin gwiwa, da tsare-tsare da aiwatar da matakai yadda ya kamata.

 

Haka kuma, a yayin zantawarsa da shugabar taron MDD karo 80 Annalena Baerbock, a gefen babban taron muhawarar majalissar dake gudana a halin yanzu, firaministan kasar Sin Li Qiang, ya ce Sin na goyon bayan gina MDD mai karin inganci da hangen nesa, ta hanyar gudanar da sauye-sauyen kyautata karko da nagartar ayyukanta.

Ya kuma bayyana kakkarfan goyon bayan Sin ga ikon MDD, da rawar da take takawa a harkokin kasa da kasa.

 

Bugu da kari, a jiya Laraba, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gana da shugabar hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Turai ta EU Ursula von der Leyen a birnin New York.

 

Yayin ganawar tasu Li Qiang ya ce, a bana ake cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da kungiyar EU, kuma kasar Sin na fatan kungiyar EU za ta dauki matakai yadda ya kamata, da nufin inganta hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu don tallafa wa al’umma. Haka kuma, ya ce, kasar Sin na fatan kungiyar EU za ta cika alkawarinta na bude kasuwannin cinikayya da zuba jari, da kuma bin ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO, da kaucewa shigar da siyasa da batun tsaron kasa cikin harkokin cinikayya.

 

Ya ce a matsayisu na manyan bangarori guda biyu a harkokin duniya, ya kamata kasar Sin da kungiyar EU, su sauke nauyin dake wuyansu, tare da ba da gudummawa a harkokin kasa da kasa, domin kare moriyarsu da ta gamayyar kasa da kasa.

 

A nata bangare, Ursula von der Leyen ta ce, kungiyar EU tana fatan aiwatar da ra’ayi daya da shugabannin bangarorin biyu suka cimma a yayin ganawarsu a bana, da kuma warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari, ta yadda za a cimma sabbin sakamako a fannonin zuba jari, da kiyaye muhalli, da taimakawa kasashe masu tasowa da dai sauransu. Ta kuma kara da cewa, kungiyar EU ta yaba wa kasar Sin bisa himmarta a fannin fuskantar sauyin yanayi, tana kuma fatan zurfafa hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu a fannin, domin gaggauta aikin kwaskwarimar neman ci gaba ta hanyoyin kare muhalli, da tabbatar da dauwamammen ci gaban duniya.

 

A wannan rana kuma, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gana da shugaban asusun Gates na kasar Amurka wato Bill Gates a birnin New York. Yayin da suke zantawa, Li Qiang ya ce cikin ’yan shekarun nan, kasar Sin ta samu gaggarumin ci gaba a fannin kiwon lafiya, ta kuma halarci hadin gwiwar raya kasashen duniya cikin himma da kwazo.

 

Ya ce kasar Sin tana fatan karfafa hulda tsakaninta da asusun Gates, domin habaka shirye-shiryen hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya a duk fadin duniya, ta yadda za a tallafawa al’ummomin sassa daban daban, yayin da ake ba da gudummawar raya kasa da kasa. Haka kuma, ya ce, ya kamata kasashen Sin da Amurka su karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu, da kyautata tsarin gudanar da harkokin duniya, ta yadda za a tabbatar da bunkasuwar duniya cikin lumana.

 

A nasa bangare kuma, Bill Gates ya ce, dangantakar dake tsakanin kasar Sin da Amurka ita ce dangantaka mafiya muhimmanci a duniya, kuma asusun Gates da shi kansa, suna son ba da gudummawa ga aikin karfafa mu’amala tsakanin kasashen biyu, da kuma fuskantar kalubalolin duniya cikin hadin gwiwa. (Masu Fassara: Saminu Alhassan, Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: hadin gwiwa kungiyar EU Li Qiang ya

এছাড়াও পড়ুন:

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

A yau Jumma’a 10 ga watan Oktoba, an kaddamar da wani shiri na aikin hadin gwiwa mai lakabin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” na rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) na shekarar 2026 a birnin Beijing.

 

Shen Haixiong, babban darektan CMG, ya gabatar da jawabi a wajen taron, inda ya bayyana cewa, CMG ya samu damar zamowa kan gaba a fagen yada labarai na kasa da kasa bisa kayayyakin aiki da ma’aikata, kuma shi ne muhimmin dandali na tallata kayayyakin kasar Sin. Kamfanin a shirye yake ya dauki shirin a matsayin wata damar yin aiki kafada da kafada da abokan kawance daga kowane bangare na rayuwa, tare da rubuta sabon babi a fagen gina kasa mai kunshe da kayayyakin kamfanonin da suka kasance a kan gaba. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka October 10, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata   October 10, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh
  • China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100%
  • An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa
  • Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya