Leadership News Hausa:
2025-11-27@21:16:48 GMT

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

Published: 25th, September 2025 GMT

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

Daga nan sai ya jaddada aniyar Sin, ta ci gaba da goyon bayan matsayi da ikon MDD, tare da mara baya ga sassan kasa da kasa wajen cimma nasarar amfani da dandalin MDDr a matsayin fagen karfafa shawarwari da hadin gwiwa, da tsare-tsare da aiwatar da matakai yadda ya kamata.

 

Haka kuma, a yayin zantawarsa da shugabar taron MDD karo 80 Annalena Baerbock, a gefen babban taron muhawarar majalissar dake gudana a halin yanzu, firaministan kasar Sin Li Qiang, ya ce Sin na goyon bayan gina MDD mai karin inganci da hangen nesa, ta hanyar gudanar da sauye-sauyen kyautata karko da nagartar ayyukanta.

Ya kuma bayyana kakkarfan goyon bayan Sin ga ikon MDD, da rawar da take takawa a harkokin kasa da kasa.

 

Bugu da kari, a jiya Laraba, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gana da shugabar hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Turai ta EU Ursula von der Leyen a birnin New York.

 

Yayin ganawar tasu Li Qiang ya ce, a bana ake cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da kungiyar EU, kuma kasar Sin na fatan kungiyar EU za ta dauki matakai yadda ya kamata, da nufin inganta hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu don tallafa wa al’umma. Haka kuma, ya ce, kasar Sin na fatan kungiyar EU za ta cika alkawarinta na bude kasuwannin cinikayya da zuba jari, da kuma bin ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO, da kaucewa shigar da siyasa da batun tsaron kasa cikin harkokin cinikayya.

 

Ya ce a matsayisu na manyan bangarori guda biyu a harkokin duniya, ya kamata kasar Sin da kungiyar EU, su sauke nauyin dake wuyansu, tare da ba da gudummawa a harkokin kasa da kasa, domin kare moriyarsu da ta gamayyar kasa da kasa.

 

A nata bangare, Ursula von der Leyen ta ce, kungiyar EU tana fatan aiwatar da ra’ayi daya da shugabannin bangarorin biyu suka cimma a yayin ganawarsu a bana, da kuma warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari, ta yadda za a cimma sabbin sakamako a fannonin zuba jari, da kiyaye muhalli, da taimakawa kasashe masu tasowa da dai sauransu. Ta kuma kara da cewa, kungiyar EU ta yaba wa kasar Sin bisa himmarta a fannin fuskantar sauyin yanayi, tana kuma fatan zurfafa hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu a fannin, domin gaggauta aikin kwaskwarimar neman ci gaba ta hanyoyin kare muhalli, da tabbatar da dauwamammen ci gaban duniya.

 

A wannan rana kuma, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gana da shugaban asusun Gates na kasar Amurka wato Bill Gates a birnin New York. Yayin da suke zantawa, Li Qiang ya ce cikin ’yan shekarun nan, kasar Sin ta samu gaggarumin ci gaba a fannin kiwon lafiya, ta kuma halarci hadin gwiwar raya kasashen duniya cikin himma da kwazo.

 

Ya ce kasar Sin tana fatan karfafa hulda tsakaninta da asusun Gates, domin habaka shirye-shiryen hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya a duk fadin duniya, ta yadda za a tallafawa al’ummomin sassa daban daban, yayin da ake ba da gudummawar raya kasa da kasa. Haka kuma, ya ce, ya kamata kasashen Sin da Amurka su karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu, da kyautata tsarin gudanar da harkokin duniya, ta yadda za a tabbatar da bunkasuwar duniya cikin lumana.

 

A nasa bangare kuma, Bill Gates ya ce, dangantakar dake tsakanin kasar Sin da Amurka ita ce dangantaka mafiya muhimmanci a duniya, kuma asusun Gates da shi kansa, suna son ba da gudummawa ga aikin karfafa mu’amala tsakanin kasashen biyu, da kuma fuskantar kalubalolin duniya cikin hadin gwiwa. (Masu Fassara: Saminu Alhassan, Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: hadin gwiwa kungiyar EU Li Qiang ya

এছাড়াও পড়ুন:

Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu

Daga Bello Wakili

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya karɓi labarin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi cikin alhini da jimami.

Fitaccen malamin da ke Bauchi ya rasu ne a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamban 2026, yana da shekaru 101.

Shugaban Ƙasan ya yi jimamin rasuwar jagoran Darikar Tijjaniyya, yana bayyana shi a matsayin ginshiƙin ɗabi’a wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyarwa da wa’azi.

Shugaba Tinubu ya ce rashinsa babban rashi ne ba ga iyalansa da dimbin mabiyansa kaɗai ba, har ma ga ƙasa baki ɗaya.

Shugaban Ƙasa ya tuna da albarka da goyon bayan da ya samu daga marigayi Sheikh Dahiru Bauchi a lokacin yakin zaɓen 2023.

“Sheikh Dahiru Bauchi malami ne, uba, mai cike da natsuwa da hikima. A matsayinaa na mai wa’azi kuma masani kan tafsirin Alƙur’ani Mai Girma, yana da’awar zaman lafiya da tsoron Allah. Rasuwarsa ta bar babban gibi,” in ji Shugaban Ƙasa.

Shugaba Tinubu ya yi ta’aziyya ga mabiyan Shehun a ci da wajen ƙasa  bisa wannan babban rashi.

Haka kuma ya ja hankalinsu da su girmama sunansa ta hanyar bin koyarwarsa ta zaman lafiya, ƙarfafa dangantakarsu da Allah, da kuma kasancewa masu taushin zuciya ga jama’a.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin