Aminiya:
2025-10-13@17:47:12 GMT

Siyasa ba ta yiwuwa da rowa — Gwamna Buni

Published: 25th, September 2025 GMT

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ya shawarci matasa da ’yan siyasa masu tasowa da su fahimci cewa harkar siyasa ba ta tafiya da rowa, illa juriya da sadaukarwa da biyayya.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da yake rantsar da sabon Alƙalin alƙalai na jihar (Grand Khadi) tare da wasu Masu Ba da Shawara na Musamman, Memba na dindindin a hukumar SUBEB, da kuma Sabbin sakararorin dindindin guda 13 a wani taro da aka gudanar a babban ɗakin taro na gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu.

An gurfanar da malamai kan zargin lalata da ɗalibarsu a Zariya Hajjin 2025: Mun samu nasarori a Yobe — Mai Aliyu Biriri

A jawabinsa, Gwamna Buni ya ce matasa da ’yan siyasa masu neman gina makoma a wannan fage dole ne su yi haƙuri da biyayya ga shugabanni, tare da nuna ƙwarewa da ɗa’a domin su samun ci gaba.

A cewarsa “siyasa aiki ne na haƙuri, biyayya da sadaukarwa”, ba za a cimma nasara da rowa ko gaggawa ba. Idan matasa suka rungumi juriya, gobe suma za su zama shugabanni a matakai daban-daban.”

Ya ƙara da cewa, siyasa tana buƙatar haɗin kai, fahimta da tsayin daka wajen bautar da al’umma, ba don amfanin kai kaɗai ba. A cewarsa wannan shi ne ginshiƙin da ya kamata kowanne ɗan siyasa ya yi koyi da shi.

Gwamnan ya kuma ja hankalin sabbin jami’an da aka rantsar da su kasance masu gaskiya, nagarta da aiki tuƙuru domin tabbatar da kyakkyawan tsarin mulki a Jihar Yobe.

“Aikin da aka ba ku nauyi ne daga Allah da kuma al’umma. Ku tabbatar da cewa kun yi shi da gaskiya, aminci da sadaukarwa. Idan kuka yi haka, za ku bar tarihi mai kyau ga al’ummar Jihar Yobe,” in ji Buni.

Wannan taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya, malamai da ɗimbin jama’a daga sassa daban-dabam na jihar, inda aka yaba wa Gwamna Buni bisa ga ƙoƙarinsa na gina al’umma mai dogaro da kai, tare da cusa nagarta a cikin shugabanci nagari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa

Kungiyar ‘Yan Dako ta kasa reshen jihar Jigawa ta kaddamar da Malam Muhammad Tajudeen Maigatari a matsayin sakataren kungiyar na jihar.

Da yake jawabin a lokacin bikin kaddamawar a garin Maigatari, Shugaban kungiyar na jihar Malam Nasiru Idris Sara, ya bayyana shugabanci a matsayin rikon amana a maimakon hanyar tara dukiya da alfahari, a don haka akwai bukatar sakataren ya yi aiki tukuru dan kare martabar sana’ar dako da masu yin ta.

Yana mai cewar shugabancin kungiyar zai hada kai da shugabannin kananan hukumomi da masu rike da sarautu da jami’an tsaro a matsayin abokan kawo cigaba wajen daga likkafar sana’ar dako.

Nasiru Idris Sara ya kuma yi kira ga daukacin ‘yan dako a fadin jihar da su yi rijista da kungiyar domin kasacewa a karkashin inuwa daya ta yadda za su ci moriyar tanade tanaden ta, sannan su kasance masu mutunta shugabanci da kuma bin doka da oda domin inganta rayuwar su.

Ya ce yayin da kungiyar ta ke da ‘yan dako kimanin dubu 20 a karkashin ta, akwai bukatar duk ‘yan dakon da ba su da katin zabe su karbi sabo ko kuma su sabunta wanda ya bata ko ya lalace domin amfani da damar su wajen zaben shugabanni.

A sakon sa, Hakimin Maigatari Alhaji Sani Alhassan Muhammad wanda ya sami wakilcin Sarkin Kasuwar Maigatari Alhaji Muhammadu Sarkin Kasuwa, ya bukaci sabon sakataren kungiyar Malam Muhammad Tajudeen ya kasance mai nuna gaskiya da adalci wajen huldar sa da ‘yan dako da sauran masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci, inda ya bayyana murnar samun wannan mukamin.

Cikin wadanda suka halarci taron sun hada da Sarkin hatsin Maigatari, Malam Mu’azu Bako da Shugaban leburorin Dingas na Jamhuriyar Nijar Malam Lawwali Hassan.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato