Majalisar Jigawa ta amince da ƙarin kasafin kuɗi Naira biliyan 75
Published: 25th, September 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta amince da ƙarin kasafin kuɗi na shekarar 2025 na Naira biliyan 75 na kasafin kuɗin jihar da ƙananan hukumomi.
An amince da kasafin kuɗin ya zama doka ne a yayin zaman majalisar wanda mataimakin Shugaban Majalisar Hon. Sani Isiya ya jagoranta.
Ana zargin mai shagon kemis da ya yi wa ’yar shekara 14 fyaɗe a Filato An kashe ’ya’yan magoya bayan Gwamna ZulumMatakin ya biyo bayan amincewa da rahoton kwamitin kasafin kuɗi na Majalisar wanda Hon Ibrahim Hamza Adamu ya gabatar.
Ƙarin kasafin kuɗin da aka amince da shi ya ƙunshi Naira biliyan 58 na Gwamnatin Jiha da kuma Naira biliyan 17 na Ƙananan Hukumomi 27, wanda ya ƙunshi kashe kuɗaɗe na yau da kullum da na manyan ayyuka.
A cikin jawabinsa, Mataimakin Shugaban Majalisar ya bayyana cewa, bisa wata wasiƙa da aka samu daga ɓangaren zartarwa, an yi shirin ƙarin kasafin ne domin magance matsalolin kuɗi da suka kunno kai.
Yin hakan zai haɓaka ayyuka da shirye-shiryen da ke gudana a cikin fannoni masu mahimmanci kamar: ilimi da kiwon lafiya da ababen more rayuwa da noma.
Majalisar dai ta amince da ƙarin kasafin kuɗin na shekarar 2025, wanda ya kai Naira biliyan 689.3 kuma majalisar ta amince da shi tun a ranar 31 ga Disamba, 2024.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jigawa Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ƙarin kasafin Naira biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
Bayan an zabi kasar Iran a matsayin mamba a kwamitin zartarwa na hukumar yaki da makaman guba ta duniya, wato ‘ the Chemical Weapons Convention (CWC)’ da kuriun jimillar yan majalisar, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa Iran zata yi amfani da damar da ta samu na bin hakkin mutanen kasar Iran dangane da makaman guba wadanda Sadam Husain ya yi amfani da su a kan mutanen kasar a yakin shekaru 8 (1980-88).
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a taron CWC a birnin Hague a ranar Talatan da ta gabata. Ya kuma kara da cewa Iran zata bukaci a hukunta kasashen da suka taimakawa Sadam Husain a wajen amfani da iran wadan nan makamai wadanda suka kashe kuma suka raunata Iraniyawa da dama.
Ministan ya isa birnin Haque ne a ranar Talata da safi don halattan taron na yaki da amfani da makaman guba ta kasa da kasa. A jawabinsa ya ce binciken da gwamnatin kasar Jamus ta yi a bayan, wanda ya tabbatar da laifi kan mutum guda bai wadatarba. Saboda akwai wasu kamfanonin da kum mai yuwa Jami’an gwamnatin kasar Jamus da dama a lokacin suna da hannu a cikin wannan babban laifin da aka aikata kan kasar ta Iran.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin November 27, 2025 Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta November 27, 2025 An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki November 27, 2025 Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan November 27, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza November 26, 2025 Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa November 26, 2025 Sojoji Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar Guinea Bissau November 26, 2025 Larijani Iran Tana Maraba Da Tattaunawa Ta Gaskiya Amma Ba Tsararren Sakamako Ba November 26, 2025 November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci