Ana zargin mai shagon kemis da ya yi wa ’yar shekara 14 fyaɗe a Filato
Published: 25th, September 2025 GMT
Dangin wata yarinya ’yar shekara 14 a unguwar Gangare da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato, sun nemi a bi musu haƙƙi bisa zargin fyaɗen da wani mazaunin unguwar ya yi mata.
Bayanai sun ce tun farko an cafke mutumin da ake zargi, Ibrahim Rawi, wanda da fi sani da Baban Siyama, amma daga bisani aka sake shi bayan wasu dattawan unguwar sun sa baki.
Budurwar da abin ya faru da ita da ke koyon sana’a a wajen mutumin da ake zargi, ta ce lamarin ya faru ne tsakanin ƙarfe 7 zuwa 8 na daren ranar Lahadi yayin da ake ruwan sama.
A cewarta: “A ranar Lahadin da ta gabata ce bayan ruwan sama ya fara sauka, sai kawai ya rufe ƙofar shagonsa ne kemis inda nake koyan sayar da magani.
“Ya yi barazanar zai kashe ni da almakashi, ya tube min kaya da ƙarfi, sannan ya tilasta min yin jima’i da shi.”
Wata babbar yayar budurwar wadda ke yawan zuwa rako ta gida idan ta tashi daga shagon sayar da magungunan, ta bayyana yadda ta tarar da ’yar uwarta a wani yanayi na daban bayan ta dawo gida da kanta.
Ta ce: “Ni nake zuwa na rako ta gida, amma ranar da ne je ban same ta ba, ashe mun yi sabanin hanya don ta riga ni komawa gida.
“Da misalin ƙarfe biyu muna kwance sai na ji tana kuka, sai na tambaye ta abin da ya faru, inda ta shaida min cewa Ibrahim ya yi mata fyaɗe.
“Da safe kuwa muka garzaya ofishin ‘yan sanda na C Division muka kai rahoto. Don haka babu abin da muke nema face a yi mata adalci.”
Duk da mai unguwar Gangare, Hassan Guda, ya tabbatar da lamarin, sai dai ya ce: “iyayenta ba su kawo rahoton kai tsaye wurina ba, sai dai na ji labari daga maƙwabci.
“A matsayina na shugaba, za mu tabbatar da cewa an kama wanda ake zargi, an kuma gurfanar da shi a kotu. Muna kira ga jama’a su kwantar da hankali.”
Sai dai har yanzu wanda ake zargi yana gudunmawa, lamarin da ya sa jama’ar unguwar suka yi barazanar rufe unguwar baki ɗaya idan aka sake watsi da batun.
Haka kuma, ofishin ‘yan sanda na C Division dake Jos ya bai wa shugabannin unguwar awanni 24 su mika wanda ake zargi a hannunsu, in ba haka ba za a ɗauki mataki na doka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: budurwa fyaɗe Jihar Filato yarinya da ake zargi
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
’Yan bindiga sun yi garkuwa da aƙalla mutum 11 mazauna garin Isapa da ke kusa da Eruku a Ƙaramar Hukumar Ekiti ta Jihar Kwara.
Harin ya faru ne sa’o’i kadan bayan sakin wasu masu ibada da aka yi garkuwa da su suna tsaka da ibada a coci.
An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a KebbiA cocin CAC da ke Ekuru, ana gudanar da bikin godiya domin murnar ’yantar da mambobi 18 da aka yi garkuwa da su kusan wata guda da ya gabata, sai ’yan bindiga suka kutsa suka yi garkuwa da mutum 38 bayan sun harbe uku har lahira.
Sabon harin, wanda ya faru da misalin ƙarfe 6:00 na yammacin Litinin, an ce ’yan bindiga kimanin 20 zuwa 30 ne suka kai shi.
Bayanai sun una cewa maharan su rika yin harbi ta ko’ina yayin da suke kutsa cikin garin, lamarin da ya sa mutane suka ranta a na kare.
Wata tsohuwa ta ji rauni sakamakon harbin kan mai uwa da wabi.
Wani jagoran al’umma da bai amince a bayyana sunansa ba, ya tabbatar da lamarin, inda ya ce: “Mutane 11 aka yi garkuwa da su, bakwai daga cikin su ’yan gida ɗaya. Waɗanda aka sace sun haɗa da mace mai juna biyu, masu shayarwa biyu da kuma kananan yara.”
Shaidar y ace sunaye mutanen sun hada da Talatu Kabiru, 20, Magaji, 6, Kande, 5, Hadiza, 10, Mariam, 6, Saima, 5, Habibat (mahaifiya), Fatima Yusufu (mahaifiya), Sarah Sunday, 22 (mai juna biyu), Lami Fidelis, 23 (uwa mai shayarwa) da kuma Haja Na Allah, ita ma uwa mai shayarwa.
Shaidun gani da ido sun ce ’yan bindigar sun bi wasu sassa na garin, inda suka bar alamun ramukan harsashin harbe-harbe a bangon gidaje da ƙofofi.
An gano harsashin bindiga AK-47 da aka harba daga wurare da dama bayan ’yan bindigar sun ja da baya tare da mutanen da suka yi garkuwa da su.
Lamarin ya haifar da tsananin tashin hankali a yankin da makotan garuruwa, yayin da jami’an tsaro da ’yan sa-kai ke ƙara ƙoƙari wajen gano maharan da ceto waɗanda aka sace.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kwara, Adekimi Ojo, ya tabbatar da lamarin ga yana mai cewa: “Eh, lamarin ya faru, amma ba zan iya cewa komai da yawa ba yanzu ba. Ina gab da shiga Isapa daga Ilorin. Zan ba da rahoto idan na isa.”
A yanzu haka dai Najeriya na fuskantar ɗaya daga cikin mafi munin matsalolin tsaro a tarihin ta. Hakan dai ya haifar da rufe makarantu da dama, musamman a Arewacin ƙasar.