Aminiya:
2025-10-13@15:47:13 GMT

Ana zargin mai shagon kemis da ya yi wa ’yar shekara 14 fyaɗe a Filato

Published: 25th, September 2025 GMT

Dangin wata yarinya ’yar shekara 14 a unguwar Gangare da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato, sun nemi a bi musu haƙƙi bisa zargin fyaɗen da wani mazaunin unguwar ya yi mata.

Bayanai sun ce tun farko an cafke mutumin da ake zargi, Ibrahim Rawi, wanda da fi sani da Baban Siyama, amma daga bisani aka sake shi bayan wasu dattawan unguwar sun sa baki.

Matashi ya kashe kakanninsa saboda abinci a Kano An kashe ’ya’yan magoya bayan Gwamna Zulum

Budurwar da abin ya faru da ita da ke koyon sana’a a wajen mutumin da ake zargi, ta ce lamarin ya faru ne tsakanin ƙarfe 7 zuwa 8 na daren ranar Lahadi yayin da ake ruwan sama.

A cewarta: “A ranar Lahadin da ta gabata ce bayan ruwan sama ya fara sauka, sai kawai ya rufe ƙofar shagonsa ne kemis inda nake koyan sayar da magani.

“Ya yi barazanar zai kashe ni da almakashi, ya tube min kaya da ƙarfi, sannan ya tilasta min yin jima’i da shi.”

Wata babbar yayar budurwar wadda ke yawan zuwa rako ta gida idan ta tashi daga shagon sayar da magungunan, ta bayyana yadda ta tarar da ’yar uwarta a wani yanayi na daban bayan ta dawo gida da kanta.

Ta ce: “Ni nake zuwa na rako ta gida, amma ranar da ne je ban same ta ba, ashe mun yi sabanin hanya don ta riga ni komawa gida.

“Da misalin ƙarfe biyu muna kwance sai na ji tana kuka, sai na tambaye ta abin da ya faru, inda ta shaida min cewa Ibrahim ya yi mata fyaɗe.

“Da safe kuwa muka garzaya ofishin ‘yan sanda na C Division muka kai rahoto. Don haka babu abin da muke nema face a yi mata adalci.”

Duk da mai unguwar Gangare, Hassan Guda, ya tabbatar da lamarin, sai dai ya ce: “iyayenta ba su kawo rahoton kai tsaye wurina ba, sai dai na ji labari daga maƙwabci.

“A matsayina na shugaba, za mu tabbatar da cewa an kama wanda ake zargi, an kuma gurfanar da shi a kotu. Muna kira ga jama’a su kwantar da hankali.”

Sai dai har yanzu wanda ake zargi yana gudunmawa, lamarin da ya sa jama’ar unguwar suka yi barazanar rufe unguwar baki ɗaya idan aka sake watsi da batun.

Haka kuma, ofishin ‘yan sanda na C Division dake Jos ya bai wa shugabannin unguwar awanni 24 su mika wanda ake zargi a hannunsu, in ba haka ba za a ɗauki mataki na doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: budurwa fyaɗe Jihar Filato yarinya da ake zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya, ta gargaɗi Ƙungiyar Malaman Kami’o’i ta Ƙasa (ASUU), cewa za ta aiwatar da dokar “babu aiki, babu albashi” idan malaman suka ci gaba da yajin aikin da ka iya zai kawo cikas ga harkokin karatu.

A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta fitar da yammacin ranar Lahadi, Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, da Ƙaramar Ministan Ilimi, Suwaiba Sa’id Ahmed, sun ce gwamnati tana da niyyar magance ƙorafe-ƙorafen ASUU ta hanyar tattaunawa cikin lumana.

Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja

“Gwamnati ta nuna gaskiya, haƙuri da kyakkyawar niyya a tattaunawarta da ƙungiyar,” in ji sanarwar.

Ministocin sun bayyana cewa yawancin buƙatun ASUU, kamar ƙarin kuɗin koyarwa da inganta yanayin aiki an riga an biya musu.

Sauran matsalolin kuma suna ƙarƙashin kulawar kwamitocin gudanarwar jami’o’i, waɗanda gwamnati ta sake kafawa don su kula da batutuwan da suka rage.

Sai dai duk da waɗannan matakan, ASUU ta zaɓi shiga yajin aiki.

Ministocin sun ce wannan mataki bai nuna haɗin kai ko adalci ga ɗalibai da jama’a ba.

Sun ƙara da cewa: “Gwamnati ta yi tsayin daka wajen tabbatar da zaman lafiya da daidaita karatu a jami’o’i.

“Amma sun yi gargaɗi cewa, dokar “babu aiki, babu albashi” tana nan daram a tsarin dokokin ƙwadago na Najeriya, kuma gwamnati za ta yi amfani da ita idan aka katse harkokin karatu.

Gwamnati ta roƙi ASUU da ta sake tunani tare da dawowa teburin sulhu, inda ta ce ƙofarta a buɗe ta ke don tattaunawa da yin sulhu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano