Ya ce zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya zai tabbata ne kawai idan aka tabbatar da adalci.

Shugaban ya jaddada irin gyare-gyaren tattalin arziƙin Nijeriya, ciki har da cire tallafin man fetur da sauya dokokin musayar kuɗi.

Ya ce matakan suna da tsauri, amma dole ne a ɗauke su domin samar da ci gaba mai ɗorewa.

A kan tsaro, Tinubu ya ce yaƙin da ta’addanci ba wai da bindiga kaɗai ake cin nasara ba, sai da ra’ayoyi da ɗabi’u waɗanda ke haɗa al’umma.

Ya kuma jaddada aniyar Nijeriya ga zaman lafiya, ci gaba, da kare haƙƙin ɗan Adam, inda ya yi kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da ta yi canje-canjen da za a iya gani, tare da gargaɗin cewa idan ba haka ba, ƙungiyar za ta zama mara tasiri.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kira Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa

Wani mummunan rikicin ƙabilanci a ƙaramar hukumar  Birniwa ta jihar Jigawa ya yi ajalin mutane biyu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka.

Kakakin ’yan sanda ta jihar, DSP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin da yake zantawa da manema labarai. Ya ce tawagar jami’an tsaro ƙarƙashin Operation Salama sun garzaya wurin domin dawo da zaman lafiya tare da cafke wasu mutane bakwai da ake zargi da hannu a rikicin.

Ganau sun ce lamarin ya faru ne lokacin da wasu da ake zargin Fulani ne suka kai farmaki ƙauyen Dagaceri, inda suka ƙona gidaje tare da kai wa mazauna garin hari da kibau a lokacin da suke barci. Rahotanni sun ce gidaje da dama sun ƙone a harin da ya faru a tsakar dare.

DSP Shiisu ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun ƙwato wayoyin hannu da layu daga hannun waɗanda ake zargi.

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar Neja

Wannan lamari dai ya ƙara haifar da damuwa kan yadda rikicin ƙabilanci ke sake bayyana a wasu sassan jihar Jigawa.

A watan Satumbar 2024, akalla mutane 15 ne aka kashe a wani rikici makamancin wannan tsakanin kungiyoyin Fulani a ƙauyukan Zangon Maje da Yankunama a ƙaramar hukumar Jahun.

Sai dai duk da waɗannan matsalolin, Jihar Jigawa na daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Arewacin Najeriya.

Wani bincike mai zaman kansa da gwamnatin jihar ta gudanar a baya-bayan nan ya nuna cewa Jigawa na cikin jihohi biyar mafi kwanciyar hankali ta fuskar tsaro a cikin gida.

A watan Yuli 2025  Gwamna Umar Namadi ya gudanar da  bikin maido da zaman lafiya a ƙaramar hukumar  Guri, bayan shekaru da dama na rikicin manoma da makiyaya.

Yayin da hukumomin tsaro ke ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin harin, mazauna yankin na kira ga gwamnati da ta ƙara  tsaurara matakan tsaro da kuma samar da  tsarin gargadin gaggawa na al’umma domin hana ci gaba da  zubar da jini.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
  • Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a Masar ranar Litinin  
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza
  • Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya