Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya ce a matsayin Sin na babbar kasa mai tasowa dake sauke nauyin dake wuyanta, ba za ta nemi wani sabon matsayi na musamman, ko fifiko yayin tattaunawar cimma matsaya ta yanzu, da ma ta nan gaba, dangane da harkokin kungiyar cinikayya ta duniya WTO.

Li, ya yi wannan tsokaci ne yayin taron manyan jami’ai dangane da shawarar nan ta tsarin shugabanci da Sin ta gabatar, a gefen babban taron MDD karo na 80 dake gudana yanzu haka.

A yau Laraba, ma’aikatar cinikayya ta Sin ta kira taron manema labarai, inda mataimakin ministan cinikayya na Sin Li Chenggang, ya bayyana wannan muhimmiyar matsaya ta Sin, a matsayin alkawari dake mayar da hankali ga yanayi da ake ciki a cikin gidan Sin, da ma alakarta da sauran sassan kasa da kasa.

Li Chenggang, ya ce hakan muhimmin mataki ne da Sin ta dauka da nufin goyon bayan cudanyar cinikayya tsakanin mabanbantan sassan kasa da kasa, da aiwatar da shawarar tsarin shugabanci na duniya, wanda zai ingiza salon cinikayya da zuba jari mai ‘yanci da ci gaba, wanda ke karkata ga karfafa zuciya, da shigar da kuzari a salon gudanar da sauye-sauye ga tsarin jagorancin raya tattalin arzikin kasa da kasa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

UNGA: Yau Shettima zai gabatar da jawabin Najeriya a MDD

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima a ranar Laraba zai gabatar da jawabin Najeriya a taron Babban Zauren Majalisar Dinkin duniya (UNGA) karo na 80 da ke gudana a birnin New York na Amurka.

Zai yi jawabin ne a madadin Shugaban Kasa Bola Tinubu tsakanin karfe 3:00 na yamma zuwa 9:00 na dare agogon birnin New York.

Mun ci ribar Naira biliyan 601 a watanni shidan farkon 2025 – Bankin GT Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa ana sa ran Najeriya za ta bayyana sabbin kudurorinta na kasa (NDCs) da aka sabunta a karkashin yarjejeniyar Paris yayin wannan jawabi.

A baya, Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya halarci zaman bude taron Majalisar Dinkin Duniya, inda Shugaban Amurka, Donald Trump, ya gabatar da jawabi na musamman, yana maraba da shugabannin duniya zuwa taron.

Da yake magana da NAN kan muhimmancin jawabin na Najeriya Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai da Sadarwa (Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa), Stanley Nkwocha, ya ce ana sa ran sakon Najeriya ya karade duniya.

“Ko a fannin diflomasiyyar ilimi, al’adu, wasanni, tsaro, ko diflomasiyyar tattalin arziki, Shugaba Tinubu ya sauya yadda Najeriya ke mu’amala da al’ummar duniya.

“Ya gyara salon manufofin kasashen waje na Najeriya.

“Idan kana son auna karfin muryar Najeriya a matakin duniya, ka tuna da jawabin da ya gabatar a UNGA na shekarar 2024.

“Jawabi ne mai karfi da ya bukaci a yi sauye-sauye, ciki har da karin kujeru ga kasashen Afrika a Kwamitin Tsaro na MDD,” in ji Nkwocha.

(NAN)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a gudanar da taron kiwon lafiya na farko a Gombe
  • Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Babban Taro Kan Shawarar Samar Da Ci Gaban Duniya
  • UNGA: Yau Shettima zai gabatar da jawabin Najeriya a MDD
  • Firaministan Sin Ya Isa New York Don Halartar Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
  • Pezeshkiyan Ya Ce Tattaunawa Da Kasashe Masu Nuna Karfi Kan Wasu Ba Zai Taba Yi Yuwa Ba
  •   Nato Na Yin Taron Tattaunawa Keta Hurumin Samaniyar Kasar Estonia Da Rasha Ta Yi
  • Sin Tana Maraba Da Kwararru Daga Bangarori Daban Daban Na Kasa Da Kasa Su Zo Kasar
  • NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa
  • Kasar Sin Za Ta Shirya Taron Mata Na Duniya A Beijing Yayin Cika Shekaru 30 Da Taron Mata Na 1995