Shugaban Syria ya yi jawabi a taron MDD karon farko cikin kusan shekaru 60
Published: 25th, September 2025 GMT
Shugaban gwamnatin riƙon ƙwaryar Syria Ahmed al-Sharaa ya shaida wa babban taron Majalisar Dinkin Duniya cewa ƙasarsa ta sake ƙwato matsayinta a idon duniya.
Wannan ne karon farko cikin kusan shekaru 60 da wani shugaban Syria ya yi jawabi a taron MDD.
Siyasa ba ta yiwuwa da rowa — Gwamna Buni Za a gudanar da taron kiwon lafiya na farko a GombeAl-Sharaa ya zama shugaban Siriya na farko da ya yi jawabi a Majalisar Dinkin Duniya tun bayan da Noureddine Attasi ya yi jawabi a shekara ta 1967, jim kaɗan bayan yaƙin Larabawa da Isra’ila, a lokacin da Damashka ta rasa iko da tuddan Golan wanda Isra’ila ta ƙwace a shekarar 1981.
Al Sharaa ya ce yaƙin basasa ya ɗaiɗaita Syria, amma ya alƙawarta gudanar da zaɓuka a ƙasar.
Jawabin da ya yi a taron na MDD da ke gudana a New York ya ɗauki hankalin mahalarta taron a Amurka, ƙasar da a baya ta sanya tukwicin dala miliyan 10 ga wanda ya taimaka aka kama shi.
A watan Disamban da ya gabata ne aka kawo ƙarshen mulkin kama-karya da iyalan Assad suka shafe kusan rabin ƙarni suna yi a Siriya, bayan da aka kifar da Shugaba Bashar al-Assad a wani gagarumin samame da dakarun ’yan tawaye ƙarƙashin jagorancin al-Sharaa suka kai.
Kifewar Assad ta kawo ƙarshen daular mulkin da ta mamaye Siriya na tsawon shekaru 50, tare da kawo ƙarshen yaƙin basasa da ya shafe fiye da shekaru 14 yana addabar ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bashar al Assad Syria ya yi jawabi a
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
Kazalika, duk dai a jiya Jumma’ar, yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai game da taron, Chen Binhua, mai magana da yawun Ofishin Harkokin Taiwan na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin ya ce taron wanda ya gudana shekaru goma da suka gabata ya karfafa muhimmiyar rawar da Yarjejeniyar 1992 ta taka a matsayin ginshikin siyasa ta bunkasa zaman lumana a dangantakar bangarori biyu na mashigin tekun, kana matukar an ci gaba da amincewa da Yarjejeniyar 1992 kuma aka nuna adawa da batun “‘yancin kai na Taiwan”, to dangantakar bangarorin biyu za ta iya bunkasa cikin lumana kuma za a iya kara inganta muradun ‘yan kasa da ke bangarorin biyu na mashigin tekun. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA