Tinubu Ya Taya Wadanda Suka Yi Nasara A Zaben Cike Gurbi Murna
Published: 18th, August 2025 GMT
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya murna ga waɗanda suka yi nasara a zaɓukan cike gurbi da aka gudanar a ranar Asabar a mazabu 16 a jihohi 12 na ƙasar nan.
Mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa shugaban ƙasa ya yaba wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) bisa gudanar da zaɓen lafiya ba tare da wata matsala ko tashin hankali ba.
A cewar sakamakon da INEC ta bayyana, jam’iyyar APC ta lashe kujeru 12, yayin da jam’iyyar APGA ta samu biyu. Jam’iyyar PDP da jam’iyyar NNPP kowanne ya samu kujera ɗaya.
Shugaba Tinubu ya taya sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda murna, yana bayyana nasarorin a matsayin babban ci gaba na farko a ƙarƙashin jagorancinsa.
Haka kuma ya yaba wa gwamnoni da shugabannin jam’iyyar APC bisa rawar da suka taka wajen samun wannan nasara.
Da yake nakalto shugaban ƙasa, Onanuga ya ce: “Shugaba Nentawe Yilwatda ya nuna ƙarfin jagoranci, ya kuma tabbatar da abin da za a iya cimmawa idan aka tsayar da ‘yan takara da jama’a suka yarda da su tare da haɗin kai tsakanin shugabannin jam’iyya.”
Shugaba Tinubu ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki don cika manufofin Renewed Hope Agenda.
Shugaban ƙasa ya kuma yaba wa dukkan jam’iyyun siyasa da ‘yan takara da suka shiga zaɓen, yana roƙon su da su ci gaba da rungumar akidar siyasa bisa gaskiya ba da gaba ba domin dorewar dimokuraɗiyya.
Daga Bello Wakilo
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
Sojojin Nijeriya a Lokoja, tare da haɗin gwuiwar sauran hukumomin tsaro, sun kuɓutar da mutane shida da aka yi garkuwa da su a yankin Obajana na Jihar Kogi. Cikin waɗanda aka ceto akwai Sarkin Fulani na Asinwe a ƙaramar hukumar Okehi, wanda aka sace a gidansa, tare da wasu mutum huɗu da aka sace a ranar 12 ga Agusta, da kuma mutum biyu da aka sace a ranar 28 ga Yuli a Apata, Lokoja.
Kwamandan bataliya ta 12, kuma Kwamandan Operation Accord III, Birgediya Janar Kasim Sidi, wanda Commanding Officer na bataliya ta 126, Laftanar Kanal Francis Nwoffiah ya wakilta, ya ce an samu nasarar kuɓutar da fursunonin ne bayan samun sahihan bayanan leƙen asiri, inda dakarun suka bi sawun ƴan bindigar har cikin daji. Ya ce ƴan bindigar sun tsere da raunuka bayan fuskantar ƙarin ƙarfin Soji, suka bar waɗanda suka sace da kuma kayan su, ciki har da alburusai.
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata ’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar KogiYa ƙara da cewa, an kuɓutar da dukkan waɗanda aka sace ba tare da wani rauni ba, kuma za a haɗa su da iyalansu bayan sun sami kulawar likita. Janar Sidi ya gargaɗi ƴan ta’adda da masu garkuwa da mutane a Kogi da jihohin makwabta su tuba, in ba haka ba za su fuskanci mummunar sakamako.
Wani daga cikin waɗanda aka ceto, Sarkin Fulani na Asinwe, Malam Adamu Zage, ya gode wa Sojojin da sauran jami’an tsaro bisa jarumtar da suka nuna. Gwamnan jihar, Ahmed Usman Ododo, ya ce gwamnati ba za ta lamunci aikata laifuka a Kogi ba, tare da bayyana cewa ana ci gaba da kai farmaki kan masu aikata miyagun laifuka a jihar da kewaye.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp