Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-27@21:16:46 GMT

Tinubu Ya Taya Wadanda Suka Yi Nasara A Zaben Cike Gurbi Murna

Published: 18th, August 2025 GMT

Tinubu Ya Taya Wadanda Suka Yi Nasara A Zaben Cike Gurbi Murna

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya murna ga waɗanda suka yi nasara a zaɓukan cike gurbi da aka gudanar a ranar Asabar a mazabu 16 a jihohi 12 na ƙasar nan.

Mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa shugaban ƙasa ya yaba wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) bisa gudanar da zaɓen lafiya ba tare da wata matsala ko tashin hankali ba.

A cewar sakamakon da INEC ta bayyana, jam’iyyar APC ta lashe kujeru 12, yayin da jam’iyyar APGA ta samu biyu. Jam’iyyar PDP da jam’iyyar NNPP kowanne ya samu kujera ɗaya.

Shugaba Tinubu ya taya sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda murna, yana bayyana nasarorin a matsayin babban ci gaba na farko a ƙarƙashin jagorancinsa.

Haka kuma ya yaba wa gwamnoni da shugabannin jam’iyyar APC bisa rawar da suka taka wajen samun wannan nasara.

Da yake nakalto shugaban ƙasa, Onanuga ya ce: “Shugaba Nentawe Yilwatda ya nuna ƙarfin jagoranci, ya kuma tabbatar da abin da za a iya cimmawa idan aka tsayar da ‘yan takara da jama’a suka yarda da su tare da haɗin kai tsakanin shugabannin jam’iyya.”

Shugaba Tinubu ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki don cika manufofin Renewed Hope Agenda.

Shugaban ƙasa ya kuma yaba wa dukkan jam’iyyun siyasa da ‘yan takara da suka shiga zaɓen, yana roƙon su da su ci gaba da rungumar akidar siyasa bisa gaskiya ba da gaba ba domin dorewar  dimokuraɗiyya.

 

Daga Bello Wakilo

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu

Yan Majalisar Tarayya daga yankin Kudu sun yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, afuwa bayan da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.

Kungiyar ’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu maso Gabas ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya yi amfani da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi, wajen yi wa Nnamdi Kanu afuwa wanda kotu ta same shi da laifin ta’addanci.

Alƙali James Omotosho na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ne ya yanke hukuncin, inda ya same shi da laifi a kan tuhumar da ake masa guda bakwai, sannan ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

Tuni aka tura Nnamdi Kanu zuwa gidan yari a Jihar Sakkwato inda yake zaman waƙafi.

A cikin sanarwa bayan taron gaggawa da suka gudanar a Abuja, ’yan majalisar sun ce duk da cewa suna girmama kotu da tsarin shari’a, lamarin ya rikiɗe zuwa matsalar ƙasa mai tasiri ga rayuwar jama’a, tattalin arziki da tsaro.

Da yake karanta sanarwar, Hon. Iduma Igariwey ya ce yin afuwa zai taimaka wajen rage tashin hankali da dawo da zaman lafiya a yankin.

Sun lissafa dalilai guda huɗu da suka sa suka yi wannan kira.

Dalilan da suke bayyana su ne ƙaruwa da rashin tsaro da tashin hankali da ke da alaƙa da tsare Kanu; Wahalar rayuwa da tattalin arziki da jama’a ke fuskanta da kuma buƙatar shugabanci mai tausayawa wajen shawo kan matsalolin ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya : Ana ci gaba da alhinin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu