Mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC ta rasu
Published: 18th, August 2025 GMT
Mama Lydia Yilwatda, mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ta rasu.
Mai magana da yawun jam’iyyar APC a Jihar Filato, Shittu Bamaiyi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Jos ranar Lahadi.
Jirgin ruwa ya nutse da mutum 30 a Sakkwato Adam A. Zango ya auri jarumar KannywoodA cewar Bamaiyi, Mama Lydia ta rasu ne da safiyar ranar Lahadi a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos tana da shekaru 83.
Ya ce, rasuwarta babban rashi ne ba ga Shugaban APC kawai ba, har ma da iyalinsa da kuma jam’iyyar APC a Jihar Filato da Najeriya baki ɗaya.
Bamaiyi, ya bayyana Mama Lydia a matsayin mace mai tsantseni wajen ibada, jajirtacciyar shugabar mata a Cocin Christ in Nation.
Ya ce tare da mijinta marigayi Fasto Toma Goshewe Yilwatda sun yi ƙoƙari wajen bunƙasa coci a jihohin Borno, Yobe, Bauchi da Filato.
Ya ƙara da cewa Mama Lydia ta bar tarihi mai kyau ta hanyar gina ’ya’yanta da kuma hidimar da ta yi wa coci da al’umma.
Jam’iyyar ta yi addu’ar Ubangiji Ya jiƙan ta kuma ya bai wa Farfesa Yilwatda da iyalinsa haƙuri da juriyar wannan babban rashi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Mahaifiyar Shugaban Jam iyyar APC jam iyyar APC
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa
Daya daga cikin ‘ya’yan babban malamin addinin musulunci a Najeriya Sayyid Ali Dhahiru Usman Bauchi ne ya tabbatar wa da jaridar “Daily Trust” rasuwar malamin.
Sayyadi Ali ya furta cewa: ” Tabbas Shehi ya koma ga mahaliccinsa, mu duka daga Allah muke, kuma zuwa gare shi za mu koma.”
Haka nan kuma ya kara da cewa, Lokaci ya yi da shehun malamin zai huta,kuma mun gode wa Allah da ya yi mana komai, ya tsawaita rayuwar shehi har zuwa wannan lokacin.
Shi dai Shehu Dhariu Usman Bauchi an haife shi ne a 29 ga watan Yuni na 1927, ya kuma rasu yana dan shekaru 97 a wannan Alhamis din 27/ ga watan Nuwamba 2025.
Gabanin rasuwarsa ya kasance daya daga cikin fitattun malaman addinin musulunci a Najeriya da ma fadin Afirka wanda ya kare rayuwarsa wajen koyar da alkur’ani mai girma da sauran ilimomin addinin musulunci. Haka nan kuma yana cikin manyan malaman darikar Tijjaniyya a cikin kasar da ma Afirka.
Kuma a madadin Radiyo Hausa na Muryar jamhuriyar musulunci ta Iran da dukkanin ma’aikatanta muna mika ta’aziyya ga iyalansa da dukkanin almajiransa da masoyansa.
Allah ya ji kansa ya yi masa rahama.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC November 27, 2025 HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin November 27, 2025 Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta November 27, 2025 An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki November 27, 2025 Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan November 27, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza November 26, 2025 Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa November 26, 2025 Sojoji Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar Guinea Bissau November 26, 2025 Larijani Iran Tana Maraba Da Tattaunawa Ta Gaskiya Amma Ba Tsararren Sakamako Ba November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci