Aminiya:
2025-10-13@15:49:50 GMT

Mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC ta rasu

Published: 18th, August 2025 GMT

Mama Lydia Yilwatda, mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ta rasu.

Mai magana da yawun jam’iyyar APC a Jihar Filato, Shittu Bamaiyi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Jos ranar Lahadi.

Jirgin ruwa ya nutse da mutum 30 a Sakkwato Adam A. Zango ya auri jarumar Kannywood

A cewar Bamaiyi, Mama Lydia ta rasu ne da safiyar ranar Lahadi a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos tana da shekaru 83.

Ya ce, rasuwarta babban rashi ne ba ga Shugaban APC kawai ba, har ma da iyalinsa da kuma jam’iyyar APC a Jihar Filato da Najeriya baki ɗaya.

Bamaiyi, ya bayyana Mama Lydia a matsayin mace mai tsantseni wajen ibada, jajirtacciyar shugabar mata a Cocin Christ in Nation.

Ya ce tare da mijinta marigayi Fasto Toma Goshewe Yilwatda sun yi ƙoƙari wajen bunƙasa coci a jihohin Borno, Yobe, Bauchi da Filato.

Ya ƙara da cewa Mama Lydia ta bar tarihi mai kyau ta hanyar gina ’ya’yanta da kuma hidimar da ta yi wa coci da al’umma.

Jam’iyyar ta yi addu’ar Ubangiji Ya jiƙan ta kuma ya bai wa Farfesa Yilwatda da iyalinsa haƙuri da juriyar wannan babban rashi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mahaifiyar Shugaban Jam iyyar APC jam iyyar APC

এছাড়াও পড়ুন:

Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

 

Li ya ce kasar Sin za ta ci gaba da nuna goyon baya ga jam’iyyar WPK, don ta bayar da jagoranci ga al’ummun kasar Koriya ta Arewa, wajen neman ci gaba bisa halin da kasar take ciki. A sa’i daya kuma, kasar Sin tana fatan karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannoni da dama, kamar aiwatar da ra’ayi daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, tare da kara musayar manyan jami’ai, da mu’amala kan manyan tsare-tsare, ta yadda za a inganta fahimtar siyasa a tsakanin kasashen biyu, tare da cimma sakamako mai kyau bisa hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Koriya ta Arewa. (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza October 10, 2025 Daga Birnin Sin Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya October 10, 2025 Daga Birnin Sin CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar
  • Yadda Ake Gurasa Ta Semovita
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida