Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Gwamnatin Kebbi Bisa Rasuwar Sarkin Zuru
Published: 18th, August 2025 GMT
Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya yi ta’aziyya ga gwamnatin Jihar Kebbi da al’ummar jihar bisa rasuwar Sarkin Zuru, Mai Martaba, Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (Gomo II).
A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasan shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar, ya bayyana rasuwar Sarkin a matsayin “babban rashi ga ƙasa,” inda ya tuno irin hidimar da marigayin ya yi a matsayinsa na tsohon gwamnan soja na Jihar Bauchi da kuma hidimarsa a matsayin basarake.
Shugaba Tinubu ya lura cewa Najeriya za ta daɗe tana tuna gudummawar tsohon janar ɗin, wanda kuma ya yi yaƙi a matsayin ƙaramin hafsan soja lokacin Yaƙin Basasa.
Shugaban ƙasa ya kuma yabawa jagorancin marigayin, wanda ya ce ya kawo zaman lafiya da cigaba a masarautar Zuru da Jihar Kebbi baki ɗaya.
Ya yi addu’a ga Allah Madaukakin Sarki da ya jikan sarkin da rahama, ya kuma ba iyalansa da jama’arsa haƙurin jure wannan babban rashi.
Daga Bello Wakili
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarkin Zuru
এছাড়াও পড়ুন:
Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga Dan Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya.
Shugaban kasar Cuba miguiel Diaz –canel yayi tir da matakin da kwamitin dake bada kyautar noble a duk shekara ya dauka na bada kyatutar ta wannan shekarar ta 2025 ga dan adawan kasar venuzela maria corina machado inda ya bayyana shi a matsayin abin ban kunya .
Matakin na Diaz canel yana nuna irin yanayin zaman tankiya tsakanin gwamnatocin latin Amurka da kuma kasashen yamma , kuma yana nuna cewa rabuwar kawuna kan wanda aka amince shi a matsyin mai inganci a bangaren dimokuradiya kuma ya haifar da rashin zaman lafiya a yankin.
Yana mai cewa babban abin kunya ne ace kyutar Nobel ta zaman lafiya a mika ta ga wadda ta janyo tsoma bakin sojoji a kasarta,
Wannan yana nuna irin rarrabuwar kayi da aka samu a fadin latin Amurka game da maa’nar zaman lafiya da demokuradiya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa October 11, 2025 Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref October 11, 2025 Iran Ta Bukaci HKI Ta Aiwatar Da Yarjeniya Da Gaza Kamar Yadda Take October 11, 2025 HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta October 11, 2025 Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza October 11, 2025 Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci