Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya yi ta’aziyya ga gwamnatin Jihar Kebbi da al’ummar jihar bisa rasuwar Sarkin Zuru, Mai Martaba, Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (Gomo II).

A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasan shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar, ya bayyana rasuwar Sarkin  a matsayin “babban rashi ga ƙasa,” inda ya tuno irin hidimar da marigayin ya yi a matsayinsa na tsohon gwamnan soja na Jihar Bauchi da kuma  hidimarsa a matsayin basarake.

Shugaba Tinubu ya lura cewa Najeriya za ta daɗe tana tuna gudummawar tsohon janar ɗin, wanda kuma ya yi yaƙi a matsayin ƙaramin hafsan soja lokacin Yaƙin Basasa.

Shugaban ƙasa ya kuma yabawa jagorancin marigayin, wanda ya ce ya kawo zaman lafiya da cigaba a masarautar Zuru da Jihar Kebbi baki ɗaya.

Ya yi addu’a ga Allah Madaukakin Sarki da ya jikan sarkin da rahama, ya kuma ba iyalansa da jama’arsa haƙurin jure wannan babban rashi.

Daga Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sarkin Zuru

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

Tinubu ya kara da cewa tun bayan karbar mulkinsa, gwamnatinsa ta bayar da fifiko wajen samun damar kudi kuma ta yi alkawarin tallafa wa harkokin kasuwanci da zai habbaka samar da ayyuka da samun kwarewa da kuma masana’antu.

Ya yaba wa gwamnatin Kuros Ribas kan kirkiro shirin tattaunawa da fasahar zamani a harkokin kasuwancin jihar, yana mai cewa wannan ya sa jihar ta yi fice a bangaren fasahar zamani.

“Fasahar zamani zai bai wa harkokin kassuwanci kanana da matsakaita samun damar intanet mai sauri da mai arha da kayayyakin aiki na zamani da samun hadin gwiwa don koyo da ingantawa, tare da tunawa cewa duniya ta kasance wani fage na bunkasa harkokin kasuwanci a zamanance.

“’Yan kasuwa da ke habaka kasuwancinsu a zamanance suna da wuri a Ikom da masu yin kayan daki a Kalabar da masu zanen kaya a Ogoja, Ugep, ko Odukpani.

“Wannan shi ne dalilin da ya sa tsare-tsaren gwamnatina na sabuwar fata ke nufin samar da yanayi mai kyau ga kanana da matsakaitan karkokin domin su samu damar habaka.

“Kudurinmu ba shi ne, ba kawai bayar da rance ko tallafi ba, gina wani tsarin da zai samar da ababen more rayuwa da kuma karfafa basirar ‘yan kasuwa,” in ji shi.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kuros Ribas, Bassey Otu ya bayyana taron harkokin kasuwanci kanana da matsakaita karo na 8 a matsayin matsayin wata manufa mai matukar muhimmanci a tsakanin jihar da gwamnatin tarayya.

Otu ya ce manufar ita ce inganta ruhin harkokin kasuwanci na ‘yan kasa da kuma bunkasa tattalin arzikin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Taya Wadanda Suka Yi Nasara A Zaben Cike Gurbi Murna
  • Mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa ta rasu
  • Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar rasuwar Sarkin Zuru
  • Sarkin Zuru: Muhammadu Sani Sami (1943-2025)
  • Sarkin Zuru ya rasu yana da shekara 81
  • Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu
  • An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons
  • Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
  • ASCSN Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Nada Muhammad Dagaceri Shugaban Ma’aikata