AMA Foundation Da FGC Kaduna Sun Hada Kai Domin Tallafawa Ilimin Marayu A Jihar Kaduna
Published: 17th, August 2025 GMT
Kungiyar AMA Foundation, tare da hadin gwiwar Kwalejin Gwamnatin Tarayya FGC Kaduna, sun hada karfi da karfe wajen ilmantar da marayu a jihar Kaduna.
Ta wannan hadin gwiwa, marayu da suka kammala makarantar firamare a Hauwa’u Memorial School, wadda AMA Foundation ta kafa a Tudun Wada, Kaduna, suna samun damar shiga Makarantar Sakandare na Gwamnatin Tarayya kai tsaye.
Yayin taron Annual Speech and Prize-Giving Ceremony na makarantar, Shugaban makarantar Hauwa’u Memorial, Nasir Musa, wanda ya wakilci AMA Foundation, ya bayyana cewa yanzu haka ana daukar nauyin marayu 120 a makarantar firamare, wasu 120 a Makarantar Sakandare na FGC Kaduna, sannan dalibai 16 sun samu gurbin shiga Jami’ar Jihar Kaduna (KASU).
Ya jinjina wa wanda ya assasa wannan makarantara Alhaji Musa Bello, saboda kafa wannan gagarumin aikin da ke mayar da hankali wajen kula da marayu, yana mai cewa hakan zai basu damar cika burinsu.
Babban malamin makarantar FGC Kaduna, Prince Adewale Adeyanju, shi ma ya yaba wa AMA Foundation saboda daukar nauyin karatun marayu daga firamare har jami’a, yana mai bayyana shi a matsayin kyawawan abubuwan da mutum zai iya bayarwa ga al’umma.
Ya bayyana cewa dukkan daliban da aka dauki nauyi a wannan shekara sun kammala da sakamako mai kyau, wanda zai ba su damar samun gurbi a manyan jami’o’i a duniya.
A nashi jawabin, a madadin Shugabar Asibitin Ido na Tarayya dake Kaduna, Dr. Amina Hassan, Dr. Sadiq Muhammad ya bayyana gamsuwarsa da irin ilimin da aka ba wa wadannan marayun.
Ya kuma yi kira ga sauran masu hali su yi koyi da wannan irin wannan kyautatawa.
Shugaban Daliban Maza wato Head Boy, Ibrahim Usman Waziri, da ta bangaren mata, Hafsat Adam Waziri, sun nuna farin cikinsu da kasancewa cikin daliban da suka kammala.
Sun yi kira ga iyaye su tabbatar da ganin ‘ya’yansu sun samu ilimin addinin Musulunci da na zamani tare.
Iyaye da ‘yan uwa na wasu daga cikin daliban da suka kammala, ciki har da Asmau Ahmed da Sabi Yusuf (uwa da kawu), sun gode wa AMA Foundation saboda damar da ta ba ‘ya’yansu wajen canza rayuwarsu.
A yayin bikin kaddamar da littafi da aka gudanar a wajen taron, Babban Daraktar na AMA Foundation, Aisha Yusuf Mamman, wacce ba ta samu halarta ba ta aiko da sakon fatan alheri, yayin da Mataimakiyar Babban Darakta, Fatima Bala Jafar, ta bada gudunmawar naira ₦50,000.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jihar Kaduna Marayuy Tallafawa
এছাড়াও পড়ুন:
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Garin Girfa (cinnamon), Garin kaninfari Clove)
Yadda za a hada:
Za’a samu garin girfa kamar cokali 5 garin kaninfari cokali 7 za a hade waje daya, sai a rika diban rabin karamin cokali ana zubawa a ruwan shayi ana sha sau 2 a rana ayi kamar sati daya.
Za a samu waraka da yardar Allah.
Ciwon Sanyi
Abubuwan bukata:
Hulba, Bagaruwa, Man Habbatussauda
yadda za a hada:
A hada Bagaruwa da Hulba a tafasa su, sai idan ya dan huce sai a zauna a ciki, sannan kuma za a shafa man Habbatussauda a gaban, a sashi kamar yadda za’a yi matsi.
In sha Allah za a samu sauki.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA