AMA Foundation Da FGC Kaduna Sun Hada Kai Domin Tallafawa Ilimin Marayu A Jihar Kaduna
Published: 17th, August 2025 GMT
Kungiyar AMA Foundation, tare da hadin gwiwar Kwalejin Gwamnatin Tarayya FGC Kaduna, sun hada karfi da karfe wajen ilmantar da marayu a jihar Kaduna.
Ta wannan hadin gwiwa, marayu da suka kammala makarantar firamare a Hauwa’u Memorial School, wadda AMA Foundation ta kafa a Tudun Wada, Kaduna, suna samun damar shiga Makarantar Sakandare na Gwamnatin Tarayya kai tsaye.
Yayin taron Annual Speech and Prize-Giving Ceremony na makarantar, Shugaban makarantar Hauwa’u Memorial, Nasir Musa, wanda ya wakilci AMA Foundation, ya bayyana cewa yanzu haka ana daukar nauyin marayu 120 a makarantar firamare, wasu 120 a Makarantar Sakandare na FGC Kaduna, sannan dalibai 16 sun samu gurbin shiga Jami’ar Jihar Kaduna (KASU).
Ya jinjina wa wanda ya assasa wannan makarantara Alhaji Musa Bello, saboda kafa wannan gagarumin aikin da ke mayar da hankali wajen kula da marayu, yana mai cewa hakan zai basu damar cika burinsu.
Babban malamin makarantar FGC Kaduna, Prince Adewale Adeyanju, shi ma ya yaba wa AMA Foundation saboda daukar nauyin karatun marayu daga firamare har jami’a, yana mai bayyana shi a matsayin kyawawan abubuwan da mutum zai iya bayarwa ga al’umma.
Ya bayyana cewa dukkan daliban da aka dauki nauyi a wannan shekara sun kammala da sakamako mai kyau, wanda zai ba su damar samun gurbi a manyan jami’o’i a duniya.
A nashi jawabin, a madadin Shugabar Asibitin Ido na Tarayya dake Kaduna, Dr. Amina Hassan, Dr. Sadiq Muhammad ya bayyana gamsuwarsa da irin ilimin da aka ba wa wadannan marayun.
Ya kuma yi kira ga sauran masu hali su yi koyi da wannan irin wannan kyautatawa.
Shugaban Daliban Maza wato Head Boy, Ibrahim Usman Waziri, da ta bangaren mata, Hafsat Adam Waziri, sun nuna farin cikinsu da kasancewa cikin daliban da suka kammala.
Sun yi kira ga iyaye su tabbatar da ganin ‘ya’yansu sun samu ilimin addinin Musulunci da na zamani tare.
Iyaye da ‘yan uwa na wasu daga cikin daliban da suka kammala, ciki har da Asmau Ahmed da Sabi Yusuf (uwa da kawu), sun gode wa AMA Foundation saboda damar da ta ba ‘ya’yansu wajen canza rayuwarsu.
A yayin bikin kaddamar da littafi da aka gudanar a wajen taron, Babban Daraktar na AMA Foundation, Aisha Yusuf Mamman, wacce ba ta samu halarta ba ta aiko da sakon fatan alheri, yayin da Mataimakiyar Babban Darakta, Fatima Bala Jafar, ta bada gudunmawar naira ₦50,000.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jihar Kaduna Marayuy Tallafawa
এছাড়াও পড়ুন:
Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu.
Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya dawo Abuja daga birnin Luanda na Angola, inda ya halarci taron AU–EU karo na 7 a madadin Shugaba Bola Tinubu.
Ya wakilci shugaban kasa a taron G20 na 2025 da aka yi a Johannesburg, Afirka Ta Kudu.
A Angola, Shettima ya karanta sakon Shugaba Tinubu wanda ya sake jaddada bukatar Afrika na samun kujerun dindindin da ikon zartarwa a Majalisar Dinkin Duniya.
Ya kuma bukaci Tarayyar Turai su hada kai da Afrika wajen samar da tsare-tsaren zaman lafiya da tsaro.
Shugaba Tinubu ya tabbatar da kudirin Nijeriya na ci gaba da inganta zaman lafiya, tsaro da mulki na gari a Afrika, tare da yin aiki da Tarayyar Turai domin samun daidaito da kwanciyar hankali.
A taron G20 da aka yi a Afirka Ta Kudu, Tinubu ya bukaci shugabannin duniya su samar da tsarin kudi na kasa da kasa, tare da magance matsalolin bashi.
Ya ce tsarin da ake amfani da shi a yanzu ya zama tsohon yayi, kuma bai dace da kalubalen wannan zamani ba. ya kuma nemi a samar da ka’idojin duniya da za su tabbatar da cewa kasashen da ke samar da muhimman ma’adanai ciki har da Nijeriya, suna amfana da su.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa November 26, 2025 Sojojin Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar Guinea Bissau November 26, 2025 Larijani Iran Tana Maraba Da Tattaunawa Ta Gaskiya Amma Ba Tsararren Sakamako Ba November 26, 2025 November 26, 2025 Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza November 26, 2025 Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe November 26, 2025 Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta November 26, 2025 Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki November 26, 2025 Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin November 26, 2025 Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci