Kano: NNPP ta yi watsi da sakamakon zaɓen Ghari/Tsanyawa
Published: 17th, August 2025 GMT
Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano, ta ƙi amincewa da sakamakon zaɓen ɗan majalisar jiha da aka gudanar a mazaɓar Ghari/Tsanyawa.
Jam’iyyar ta ce Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da wasu ’yan siyasa sun yi maguɗi.
Jauro Jatau: Al’umma sun roƙi gwamnati ta samar musu da wutar lantarki APC ta lashe zaɓen cike gurbi a ZariyaShugaban jam’iyyar na jihar, Kwamared Hashimu Sulaiman Dungurawa, ya shaida wa ’yan jarida cewa INEC ta “tauye wa jama’a haƙƙinsu” bayan ta bayyana ɗan takarar jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen.
Ya ce zaɓen ya kamata a gudanar da shi ne a rumfunan zaɓe 10 da kotun ɗaukaka ƙara ta soke.
NNPP ta ce INEC ta ƙwace sakamakon da aka gudanar a rumfunan 10, tare da yin amfani da tsohon sakamakon da kotu ta riga ta soki.
“A Ghari, jama’a sun yi zaɓe lafiya a rumfunan 10, amma saboda maguɗi da wasu ’yan siyasa da jami’an INEC suka shirya, sai aka bayyana ɗan takarar APC a matsayin wanda ya yi nasara,” in ji jam’iyyar.
NNPP ta kuma zargi INEC da bayyana sakamakon a hedikwatarta ta Kano maimakon a cibiyar tattara sakamako na mazaɓar, abin da ta ce ya bayar da damar tafka maguɗi.
Jam’iyyar ta yi alƙawarin ci gaba da ƙalubalantar abin da ta kira rashin adalci da nuna son kai.
Ta kuma ce sakamakon da jami’an rumfunan zaɓe suka sanya hannu a kai shi ne ya kamata a tabbatar da shi.
Sai dai NNPP ta yaba da zaɓen cike gurbi da aka yi a Shanono/Bagwai inda ɗan takararta ya yi nasara.
Jam’iyyar ta bayyana zaɓen a matsayin mai inganci, ta kuma gode wa jami’an tsaro da kuma jama’a da suka fito ƙwansu da kwarkwata suka kaɗa ƙuri’a.
“Muna girmama jarumtar jama’armu da suka tsaya tare da mu, suka kuma zaɓi ’yan takarar NNPP a dukkanin zaɓukan da aka gudanar,” in ji shugaban jam’iyyar.
INEC da APC ba su ce komai ba tukuna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Zaɓen Cike Gurbi
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza.
Rahotanni sun tabbatar da cewa bababn jami’in kungiyar Hamas Basen Naim yayi watsi da duk wani kokor nai ya yiyuwar sanya hannu tsohon fira ministan birtaniya Tony Blair a gwamnatin da za’a kafa a yankin gaza bayan sanar da dakatar da bude wuta da aka yi a baya bayan nan.
Har ila yau Basem ya kara da cewa kungiyar tana maraba da kokarin da shugaban Amurka Donal trump yake yi na kawo karshen kisan kiyashin da Isra’ila ta kwashe shekaru 2 tana yi a yankin Gaza, sai dai sun yi gargadin cewa basa maraba da tony Blair game da taka wata rawa a sabuwar gwamnatin Gaza da za’a kafa bayan tsagaita wuta. Yace idan aka zo batun Blair kila mu falasdinawa da larabawa da sauran kasahen musulmi muna da mummunan sura akansa, har yanzu muna iya tunawa rawar da ya taka wajen kashen dubban mutane a Afghanistan ko kuma miliyoyin fararen hula a kasar Iraki da Afghanistan.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga Dan Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa October 11, 2025 Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref October 11, 2025 Iran Ta Bukaci HKI Ta Aiwatar Da Yarjeniya Da Gaza Kamar Yadda Take October 11, 2025 HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta October 11, 2025 Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza October 11, 2025 Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci