Sarkin Zuru: Muhammadu Sani Sami (1943-2025)
Published: 17th, August 2025 GMT
Sarkin Zuru, Alhaji Mohammed Sani Sami Gomo II, ya rasu a ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2025, a wani asibiti da ke birnin London bayan gajeruwar rashin lafiya. Ya rasu yana da shekaru 82.
A cewar majiyoyin danginsa, ana sa ran za a kawo gawarsa daga London zuwa Najeriya nan da gobe (Litinin), domin gudanar da jana’iza.
Marigayin ya bar mata hudu, ’ya’ya bakwai da jikoki biyu.
Daya daga cikin masu rike da sarautar gargajiya a Zuru, Muhammed Abba Zuru, ya bayyana cewa iyalan marigayin na jiran isowar gawarsa daga London kafin a kammala shirye-shiryen jana’iza.
An haifi Mohammed Sani Sami a Zuru, Jihar Kebbi, a ranar 24 ga Oktoba, 1943. Ya shiga Rundunar Sojin Najeriya a ranar 10 ga Disamba, 1962, inda ya samu horo tare da Ibrahim Babangida.
Daga bisani ya halarci Mons Officer Cadet School da ke Aldershot, Ingila, inda ya zama hafsan soji a ranar 25 ga Yuli, 1963.
Ya halarci yakin basasa na Najeriya, kuma ya jagoranci dakarun da suka fatattaki sojojin Chadi da suka kutsa Jihar Borno.
A watan Yuli 1975, Janar Murtala Mohammed ya naɗa shi kwamandan Brigade of Guards a matsayin Lieutenant Colonel.
Bayan juyin mulkin 31 ga Disamba, 1983 wanda ya kawo Janar Muhammadu Buhari kan mulki, an naɗa Sani Sami a matsayin Gwamnan Soja na Jihar Bauchi.
Ya riƙe wannan muƙamin har zuwa watan Agusta 1985 lokacin da Janar Ibrahim Babangida ya karɓi mulki daga hannun Buhari.
A lokacin mulkinsa a Bauchi, ya inganta cibiyoyin lafiya tare da kaddamar da babban shirin noma mai taken “Back to Land.”
Haka kuma ya jagoranci shirya gasar cin kofin duniya ta wasan handball a jihar.
A watan Oktoba 1984, lokacin da ake fuskantar ƙaruwa na matsalolin addini, Sani Sami ya jaddada haramcin wa’azin addini a fili.
Ya kuma bayyana cewa rushe wasu coci-coci domin gina sabon ring road ba ya nufin hari ne kan addinin Kirista, tare da ƙara da cewa gwamnati ta ware fili domin Katolika su gina sabon coci.
Ya yi ritaya daga rundunar soji a matsayin Manjo Janar a ranar 3 ga Satumba, 1990. A shekarar 1995, aka naɗa shi Sarkin Zuru na 11, mukamin da ya riƙe har zuwa rasuwarsa.
Kwamishinan Harkokin Kananan Hukumomi da Masarautu na Jihar Kebbi, Alhaji Garba Umar-Dutsinmari, ya mika ta’aziyyar gwamnatin jihar ga iyalan marigayin, Majalisar Masarautar Zuru, al’ummar Zuru da Jihar Kebbi baki ɗaya.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ya yi addu’ar Allah ya jikan marigayin da Aljannah Firdausi, tare da bai wa iyalansa haƙuri da juriyar rashin.
Sanarwar ta ƙara da cewa ana ci gaba da shirye-shiryen jana’iza yayin da ake jiran isowar gawarsa daga London.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
Sufeto Janar na ’Yan sandan Nijeriya, Olukayode Egbetokun, ya sanar da cewa sun aiwatar da umarnin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na janye dakarunsu daga gadin ɗaiɗaikun mutane da ake kira VIP.
IG Egbetokun ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai a yau Alhamis, yana mai cewa zuwa yanzu sun janye dakaru 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya.
Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da Olympiacos An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji“Wannan karon za mu aiwatar da umarnin da kyau saboda umarnin shugaban ƙasa ne,” in ji shi.
“Babu wani gwamna, ko minista, ko abokaina da za su kira su takura min saboda sun san cewa umarnin shugaban ƙasa ne. Ina kuma da tabbacin cewa ba za su uzzura wa kwamashinonin ’yan sanda ba ma.”
Ya ƙara da cewa za su tura jami’an da aka janye zuwa “wuraren da aka fi buƙatarsu, musamman a wannan lokaci mai muhimmanci.”
Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da aika ’yan sanda ga manyan mutane domin ba su tsaro na musamman, yana mai mayar da su zuwa aikin tsaro da ya shafi al’umma baki ɗaya.
Kazalila, a ranar Laraba, 26 ga watan Nuwamba ne Tinubun ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a faɗin ƙasar, inda ya bayar da umarnin a ɗauki matakan gaggawa domin magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.
Shugaban ya ce a ɗauki sababbin ’yan sanda 20,000, ƙari a kan guda 30,000 da ya fara amincewa a ɗauk, wanda za a yi amfani da sansanonin horar da masu yi wa ƙasa hidima wajen horar da sababbin ’yan sandan da za a ɗauka.