Aminiya:
2025-10-13@20:19:05 GMT

An kashe ’yan kasuwa 15 a wani sabon hari a Binuwai

Published: 19th, May 2025 GMT

Aƙalla ’yan kasuwa 15 ne aka kashe a wani sabon hari da wasu ‘yan bindiga suka kai wasu garuruwa da ke Ƙaramar Hukumar Agatu a Jihar Binuwai.

’Yan kasuwar na kan hanyarsu ta komawa gida daga kasuwar Oweto da yammacin ranar Asabar lokacin da aka kai musu hari a kusa da garuruwan Ogwumogbo da Okpo’okpolo.

An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa

Tsohon mataimakin shugaban Ƙaramar Hukumar Agatu, John Ikwulono, ya tabbatar da faruwar harin, inda ya ce mutane da dama sun jikkata.

Ya ce mutum biyar aka kashe a kusa da wani ƙaramin rafin da ake kira Abekoko.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Agatu na yanzu, Melvin James, yana wajen jana’izar waɗanda aka kashe lokacin da manema labarai suka kira shi.

Hadiminsa ne, ya ɗauki waya, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ɗora laifin kan makiyaya masu ɗauke da makamai.

Da aka tuntuɓi sakataren Ƙungiyar Miyetti Allah na jihar, Ibrahim Galma, ya ce bai da masaniya game d harin ba amma zai bincika.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, bai yi wani ƙarin haske ba.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, CSP Catherine Anene, ta ce har yanzu ba ta samu rahoton harin ba.

Wannan hari ya ƙara yawan mutanen da aka kashe a Jihar Binuwai daga ranar 1 ga watan Afrilu zuwa 17 ga watan Mayu zuwa 174.

Sai dai mazauna yankin sun ce adadin na iya wuce haka, duba da yadda wasu hare-hare ba a kai rahotonsu ba ga hukumomin tsaro.

Yankuna da dama a jihar sun fuskanci hare-hare a baya-bayan nan, ciki har da Gwer ta Gabas, Guma, yankin Sankera (Katsina-Ala, Logo, Ukum), Otukpo, Gwer ta Yamma, Kwande, Apa, Agatu da Makurdi.

Yankin Sankera ne ya fi fuskantar hare-hare, inda aka kashe aƙalla mutum 83 tsakanin 17 zuwa 21 ga watan Afrilu kaɗai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan kasuwa Binuwai hari

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.

Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta tabbatar wa al’ummar jihar a shirye ta ke ta ci gaba da kare mutuncin daidaikun mutane da kungiyoyin da suka sadaukar da kansu domin samar musu da sahihin bayanan sirri da za su kara kaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Nijar.

‘Yan sanda a jihar Neja da ma Nijeriya ƙwararru ne don haka za su ci gaba da aiki da kuma nuna basira da ƙwarewa tare da ƙa’idarta ta sirrin rashin bayyana tushen bayanansu don samun sakamako mafi girma.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja Adamu Abdullahi Elleman wanda ya bayar da wannan tabbacin a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Minna, ya bayyana cewa a kwanan baya ya halarci wani taron bita da hedkwatar ‘yan sanda ta shirya kan masu bada bayanai wato Informant domin kara kwarewarsa.

Sai dai Adamu Abdullahi Elleman ya danganta raguwar ayyukan aikata laifuka a Minna babban birnin jihar da sahihan bayanai da aka samu daga jama’a, goyon baya daga babban sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun da gwamnatin jihar Neja a karkashin jagorancin Gwamna Umar Bago, da sarakunan gargajiya da kuma matakin da ya dauka na cewa a mafi yawan lokuta yakan shiga sintiri a Minna, wanda DPO da kwamandojin yankin suka goyi bayansa.

A cewarsa sakamakon wannan yunkurin da aka yi da dama daga cikin miyagu da suka tsunduma cikin ayyukan ‘yan daba, an kama su, an kuma gurfanar da su a gaban kuliya, tare da daure su a matsayin misali ga wasu.

Adamu Abdullahi Elleman ya ci gaba da cewa, ya kuma gargadi Hakimai na yankin da su rika taimaka wa miyagu cewa duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban kuliya manta sabo.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja, ya kuma yabawa babbar mai shari’a ta jihar, Mai shari’a Halima Ibrahim bisa goyon bayan da ta bayar wajen ganin an samar da shari’a cikin gaggawa, tare da samun hadin kai tsakanin ‘yan sanda da sauran kungiyoyin tsaro baya ga sabon alkawari da jami’an sa da mazaje suke yi na yakar miyagun laifuka da aikata laifuka a duk lungu da sako na jihar.

Adamu Abdullahi Elleman ya kuma kara da cewa a karkashin sa a matsayinsa na sabon kwamishinan ‘yan sanda mai kula da jihar Neja, jin dadin jami’ansa da jami’an rundunarsa shi ne babban abin da ya fi ba da fifiko wajen kara musu kwarin gwiwa wajen gudanar da ayyuka masu inganci.

INT Aliyu Lawal.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta