Aminiya:
2025-05-19@01:12:59 GMT

An kashe ’yan kasuwa 15 a wani sabon hari a Binuwai

Published: 19th, May 2025 GMT

Aƙalla ’yan kasuwa 15 ne aka kashe a wani sabon hari da wasu ‘yan bindiga suka kai wasu garuruwa da ke Ƙaramar Hukumar Agatu a Jihar Binuwai.

’Yan kasuwar na kan hanyarsu ta komawa gida daga kasuwar Oweto da yammacin ranar Asabar lokacin da aka kai musu hari a kusa da garuruwan Ogwumogbo da Okpo’okpolo.

An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa

Tsohon mataimakin shugaban Ƙaramar Hukumar Agatu, John Ikwulono, ya tabbatar da faruwar harin, inda ya ce mutane da dama sun jikkata.

Ya ce mutum biyar aka kashe a kusa da wani ƙaramin rafin da ake kira Abekoko.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Agatu na yanzu, Melvin James, yana wajen jana’izar waɗanda aka kashe lokacin da manema labarai suka kira shi.

Hadiminsa ne, ya ɗauki waya, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ɗora laifin kan makiyaya masu ɗauke da makamai.

Da aka tuntuɓi sakataren Ƙungiyar Miyetti Allah na jihar, Ibrahim Galma, ya ce bai da masaniya game d harin ba amma zai bincika.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, bai yi wani ƙarin haske ba.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, CSP Catherine Anene, ta ce har yanzu ba ta samu rahoton harin ba.

Wannan hari ya ƙara yawan mutanen da aka kashe a Jihar Binuwai daga ranar 1 ga watan Afrilu zuwa 17 ga watan Mayu zuwa 174.

Sai dai mazauna yankin sun ce adadin na iya wuce haka, duba da yadda wasu hare-hare ba a kai rahotonsu ba ga hukumomin tsaro.

Yankuna da dama a jihar sun fuskanci hare-hare a baya-bayan nan, ciki har da Gwer ta Gabas, Guma, yankin Sankera (Katsina-Ala, Logo, Ukum), Otukpo, Gwer ta Yamma, Kwande, Apa, Agatu da Makurdi.

Yankin Sankera ne ya fi fuskantar hare-hare, inda aka kashe aƙalla mutum 83 tsakanin 17 zuwa 21 ga watan Afrilu kaɗai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan kasuwa Binuwai hari

এছাড়াও পড়ুন:

Iran : Hare-haren da Isra’ila ta kai kan Yemen babban laifin yaki ne

Iran ta yi kakkausan suka game da hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kaiwa kan kasar Yemen tana mai danganta su da babban laifin yaki.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kai wa kan ababen more rayuwa na tattalin arzikin kasar Yemen da kuma cibiyoyin jama’a sun zama “laifi na yaki da cin zarafin bil’adama.”

A cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Asabar, Esmail Baghai ya yi kakkausar suka kan hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kaiwa kan manyan tashoshin jiragen ruwa na kasar Yemen.

Ya kara da cewa hare-haren da aka kai a tashar jiragen ruwa ta Hudaydah, Ras Issa da kuma Salif na kasar Yemen, ya zama babban cin zarafi ga dokokin kasa da kasa da kuma tsarin Majalisar Dinkin Duniya.

Mista Baghai Ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila tana kai irin wadannan hare-hare ne a daidai lokacin da al’ummar kasar Yamen ke fama da matsanancin hali na jin kai.

Kakakin ya jaddada cewa Amurka da Birtaniya da wasu kasashen yammacin duniya suna da hannu a ci gaba da aikata laifukan da gwamnatin Isra’ila ke yi a Gaza da kuma ta’addancin da take yi kan kasashen musulmi a yankin.

Ya jaddada cewa goyon bayan da kasashen yammacin duniya ke baiwa Isra’ila, ya kara bai wa gwamnatin Isra’ilar karfin gwiwa wajen aiwatar da hare-haren wuce gona da iri da kisan kiyashin da take yi wa mata da kananan yara na Falastinawa wadanda ba su da kariya, kuma a halin yanzu  ga al’ummar Yemen da ake zalunta.

Jami’in na Iran ya kuma soki kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da yin shiru a kan hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke yi, Ya kara da cewa: Dole ne al’ummar musulmi su tashi tsaye wajen yakar zaluncin da gwamnatin ke yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato
  • ‘Yan Kasuwa 27 Sun Rasu A Wani Hatsarin Kwale-kwale A Kwara
  • Iran : Hare-haren da Isra’ila ta kai kan Yemen babban laifin yaki ne
  • ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno
  • Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya
  • Rikici Tsakanin Faransa Da Aljeriya Ya Shiga Wani Sabon Salo Na Koran ‘Yan Kasashen Juna Daga Kasashensu
  • Max Air Zai Yi Jigilar Alhazan Jihar Jigawa A Ranakun 20 Da 21 Ga Watan Mayu