Aminiya:
2025-07-03@02:03:05 GMT

’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa

Published: 18th, May 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Jigawa, ta ceto wata tsohuwa mai shekaru 80 da aka sace a Jihar Kano, bayan wani samame da suka kai Ƙaramar Hukumar Garki.

A yayin samamen, sun kashe mutane biyar da ake zargi masu garkuwa da mutane ne, sannan sun kama wasu biyar.

Yadda ’ya’yan shugabanni ke musu yaƙi da ’yan adawa Abba ya dakatar da hadiminsa saboda furta kalamai a kan Kwankwaso

Rahoton ya ce samamen ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na daren ranar 16 ga watan Mayu, 2025 bayan samun sahihan bayanan sirri.

Waɗanda suka sace tsohuwar, Hajiya Hajara daga Ƙaramar Hukumar Minjibir, a Jihar Kano, su 12 ne ɗauke da bindigogi, kuma sun zo ne a kan babura.

Rundunar ta haɗa kai da jami’an ’yan sanda daga Gagarawa, Gumel, Garki, da Sule-Tankarkar tare da ‘yan banga da mafarauta, ƙarƙashin jagorancin ACP Bala Umar, kwamandan ’yan sandan yankin Gumel.

Sun kai farmaki maɓoyar ’yan ta’addan da ke Wadi Fulani, GGW Tagwayen Fage, Wusada Fulani da Katoro Fulani duka a Garki.

A nan ne suka kashe mutum biyar da ake zargi, sannan suka kama wasu biyar ciki har da sarkin Fulanin Katoro mai suna Yahaya mai shekara 35.

Sun ceto Hajiya Hajara cikin ƙoshin lafiya, sannan sun ƙwato bindigogi guda uku (AK-47 biyu da LAR daya), harsashi 14, babura biyu da wayoyin hannu biyu.

Gawarwakin waɗanda aka kashe an kai su asibitin Gumel don gudanar da bincike, kuma babu jami’in tsaron da ya rasa ransa.

Majiyoyi sun ce ba a biya kuɗin fansa ba kafin ceto tsohuwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Yan Sanda Jigawa Tsohuwa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta kama wani mutum, mai shekaru 35 daga ƙauyen Kunji da ke Kwadon, bisa zargin mallakar jabun kuɗi.

Kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an kama Kawu ne a ranar 28 ga watan Yuni, 2025, a ofishin ’yan sanda na Lawanti, sannan aka kai shi ofishin Amada domin ci gaba da bincike.

Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba

Ya ce an samu dalar Amurka 1,000 da ake zargin na bogi ne (kimanin Naira miliyan 1.5), da kuma Naira 10,000 a cikin kayansa.

A yayin bincike, Kawu ya amsa cewa kuɗin na wani mutum ne.

’Yan sanda sun ce suna ci gaba da bincike domin gano wanda ya ba shi kuɗin.

Rundunar ta kuma ce za ta ci gaba da yaƙar masu ta’ammali da jabun kuɗi tare da tabbatar da cewa za ta sanar da jama’a yadda binciken ke tafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • ’Yan sanda sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa a Jigawa
  • Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kakkausar Suka Kan Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta IAEA
  • Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe
  • HOTUNA: Yadda Sarki da Gwamnonin Kano da Jigawa suka sauka a Madina domin jana’izar Dantata
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin
  • Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba
  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka