’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa
Published: 18th, May 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Jigawa, ta ceto wata tsohuwa mai shekaru 80 da aka sace a Jihar Kano, bayan wani samame da suka kai Ƙaramar Hukumar Garki.
A yayin samamen, sun kashe mutane biyar da ake zargi masu garkuwa da mutane ne, sannan sun kama wasu biyar.
Yadda ’ya’yan shugabanni ke musu yaƙi da ’yan adawa Abba ya dakatar da hadiminsa saboda furta kalamai a kan KwankwasoRahoton ya ce samamen ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na daren ranar 16 ga watan Mayu, 2025 bayan samun sahihan bayanan sirri.
Waɗanda suka sace tsohuwar, Hajiya Hajara daga Ƙaramar Hukumar Minjibir, a Jihar Kano, su 12 ne ɗauke da bindigogi, kuma sun zo ne a kan babura.
Rundunar ta haɗa kai da jami’an ’yan sanda daga Gagarawa, Gumel, Garki, da Sule-Tankarkar tare da ‘yan banga da mafarauta, ƙarƙashin jagorancin ACP Bala Umar, kwamandan ’yan sandan yankin Gumel.
Sun kai farmaki maɓoyar ’yan ta’addan da ke Wadi Fulani, GGW Tagwayen Fage, Wusada Fulani da Katoro Fulani duka a Garki.
A nan ne suka kashe mutum biyar da ake zargi, sannan suka kama wasu biyar ciki har da sarkin Fulanin Katoro mai suna Yahaya mai shekara 35.
Sun ceto Hajiya Hajara cikin ƙoshin lafiya, sannan sun ƙwato bindigogi guda uku (AK-47 biyu da LAR daya), harsashi 14, babura biyu da wayoyin hannu biyu.
Gawarwakin waɗanda aka kashe an kai su asibitin Gumel don gudanar da bincike, kuma babu jami’in tsaron da ya rasa ransa.
Majiyoyi sun ce ba a biya kuɗin fansa ba kafin ceto tsohuwar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Yan Sanda Jigawa Tsohuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Zaɓen Jigawa: Ministan Tsaro ya faɗi a rumfar zaɓensa
Ministan Tsaro, Muhammad Badaru Abubakar, ya sha kaye a rumfar zaɓensa yayin zaɓen cike gurbi na mazabar Garki-Babura a Jihar Jigawa ranar Asabar.
Ministan ya kaɗa ƙuri’arsa a rumfar Ɓaɓura Ƙofar Arewa Primary School 001, inda sakamakon da aka bayyana, jam’iyyar APC ta samu ƙuri’u 112, yayin da PDP ta samu 308 a rumfar zabensa.
Zaɓen cike gurbin na Babura-Garki ya fara ne da tsauraran matakan tsaro a fadin mazabar. Jami’an tsaro suka kasance a rumfunan zaɓe da wuraren da suka dace domin tabbatar da zaman lafiya.
A daidai ƙarfe 8:30 na safe, jami’an Hukumar Zaɓe ta Kasa (INEC) sun isa rumfar Garki-Kofar Fada (003) inda suka fara shirye-shiryen zaɓe. Mr Ibrahim Shehu, jami’in zaɓe a rumfar, ya shaida wa manema labarai cewa zaɓen ya gudana lafiya ba tare da wata matsala ta tsaro ko fasaha ba.
Sarkin Zuru ya rasu yana da shekara 81 APC ta lashe zaɓen cike gurbi na Ghari/Tsanyawa a KanoA rumfar Primary Yamma (005), Ministar Ƙasa ta Ilimi, Hajiya Suwaiba Ahmad, ta yaba da yadda zaɓen ke gudana cikin kwanciyar hankali. Ta kuma bukaci al’umma su fito su kada ƙuri’a domin jam’iyyar APC. Hajiya Suwaiba ta bayyana kwarin gwiwa cewa APC za ta yi nasara a ƙarshe.
Sai dai, a wasu sassan mazabar, an ga mazauna suna ci gaba da harkokinsu na yau da kullum, inda aka ga kasuwanci na gudana. Zaɓen ya samu fitowar jama’a mai yawa a yawancin rumfunan zaɓe.