Aminiya:
2025-10-13@17:49:59 GMT

’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa

Published: 18th, May 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Jigawa, ta ceto wata tsohuwa mai shekaru 80 da aka sace a Jihar Kano, bayan wani samame da suka kai Ƙaramar Hukumar Garki.

A yayin samamen, sun kashe mutane biyar da ake zargi masu garkuwa da mutane ne, sannan sun kama wasu biyar.

Yadda ’ya’yan shugabanni ke musu yaƙi da ’yan adawa Abba ya dakatar da hadiminsa saboda furta kalamai a kan Kwankwaso

Rahoton ya ce samamen ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na daren ranar 16 ga watan Mayu, 2025 bayan samun sahihan bayanan sirri.

Waɗanda suka sace tsohuwar, Hajiya Hajara daga Ƙaramar Hukumar Minjibir, a Jihar Kano, su 12 ne ɗauke da bindigogi, kuma sun zo ne a kan babura.

Rundunar ta haɗa kai da jami’an ’yan sanda daga Gagarawa, Gumel, Garki, da Sule-Tankarkar tare da ‘yan banga da mafarauta, ƙarƙashin jagorancin ACP Bala Umar, kwamandan ’yan sandan yankin Gumel.

Sun kai farmaki maɓoyar ’yan ta’addan da ke Wadi Fulani, GGW Tagwayen Fage, Wusada Fulani da Katoro Fulani duka a Garki.

A nan ne suka kashe mutum biyar da ake zargi, sannan suka kama wasu biyar ciki har da sarkin Fulanin Katoro mai suna Yahaya mai shekara 35.

Sun ceto Hajiya Hajara cikin ƙoshin lafiya, sannan sun ƙwato bindigogi guda uku (AK-47 biyu da LAR daya), harsashi 14, babura biyu da wayoyin hannu biyu.

Gawarwakin waɗanda aka kashe an kai su asibitin Gumel don gudanar da bincike, kuma babu jami’in tsaron da ya rasa ransa.

Majiyoyi sun ce ba a biya kuɗin fansa ba kafin ceto tsohuwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Yan Sanda Jigawa Tsohuwa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta

 

Rundunar ‘yansanda ta tabbatar da cewa ana gudanar da cikakken bincike domin gano ainihin musabbabin mutuwarta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara October 5, 2025 Tsaro Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ October 4, 2025 Tsaro Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina September 22, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta
  • ’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi 
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara