Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe
Published: 19th, May 2025 GMT
Ana zargin wasu makiyaya sun kashe mutane 15 a yankunan Ogwumogbo da Okpo’okpolo na ƙaramar hukumar Agatu dake jihar Benuwe.
Majiyoyinmu sun bayyana cewa waɗanda aka kashe sun kasance ‘yan kasuwa ne da ke dawowa daga kasuwar Oweto a Agatu lokacin da maharan suka fito daga daji suka harbe su, inda suka kashe 15 nan take.
Tsohon mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Agatu, John Ikwulono, ya tabbatar da harin da aka kai wa ‘yan kasuwar a ranar Asabar da yamma, inda ya bayyana cewa maharan sun kwace kuɗaɗe da kayayyakin waɗanda aka kashe kafin su gudu cikin daji.
“Har yanzu wasu mutane sun ɓace ba a same su ba, yayin da waɗanda suka jikkata an kai su wani asibiti a yankin,” in ji Ikwulono.
Kakakin Ƴansandan jihar, Catherine Anene, ta ce har yanzu ba a sanar da ita cikakken bayani kan lamarin ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Makiyaya
এছাড়াও পড়ুন:
Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta
Gwamnati dai ta nisanta kanta daga labarin na karya, inda ta kwatanta batun da cewa, “mai tada hankali da rashin izini”.
Gwamnatin jihar ta kuma gargadi dukkan masu rike da mukaman siyasa da su daina bayyana ra’ayoyinsu da sunan Gwamnati kan wasu muhimman batutuwan da suka shafi siyasa ba tare da tantancewa ba.
LEADERSHIP ta fahimto cewa, wannan matakin ya biyo bayan wani labari ne da aka yada da cewa, Sanata Kwankwaso ya ki amincewa da tayin da shugaba Tinubu ya yi masa na tsunduma shi cikin jam’iyyar APC, inda ake zargin Sanatan ya bayyana cewa, ya gwammace ya bar siyasa maimakon ya koma jam’iyya mai mulki.
Ba da dadewa ba, wannan labarin na karya ya samu karbuwa a shafukan sada zumunta wanda Kwankwaso da gwamnatin Kano, tuni suka yi martani a kai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp