Hajji: Gwamnatin Katsina ta biya wa maniyyata 2000 kuɗin hadaya
Published: 19th, May 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Dikko Umar Radda, ta biya wa maniyyatan jihar 2,047 kuɗin hadaya domin sauƙaƙa musu wajen hidimomin aikin Hajji na shekarar 2025.
Amirul Hajji kuma Mataimakin gwamnan jihar, Malam Faruk Lawal Jobe, ne ya bayyana haka a ranar Lahadi yayin da yake yi wa mahajjatan jirgin farko bankwana kafin tashin zuwa ƙasa mai tsarki.
Ya ce an biya wa kowane maniyyaci Riyal 600.
Mahajjatan da za su fara tafiya sun fito ne daga ƙananan hukumomin kudancin jihar, kuma za su tashi a jirgin kamfanin Max Air.
Gwamna Radda ya ja hankalin maniyyata da su kiyaye dokoki da ƙa’idojin aikin Hajji.
Haka kuma ya roƙe su da su yi addu’a don samun zaman lafiya da ci gaban Jihar Katsina da ma Najeriya baki ɗaya.
A shekarar da ta gabata ma, Gwamna Radda ya biya wa maniyyatan jihar kuɗin hadaya domin rage musu kashe kuɗi a aikin Hajji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati Hadaya maniyyata
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Nada Kwamishina Na Farko A Ma’aikatar Cigaban Kiwon Dabbobi
Gwamna Malam Umar Namadi na jihar Jigawa ya bayyana harkar kiwon dabbobi a matsayin babbar harkar tattalin arziki ta biyu a jihar baya ga noma.
Ya bayyana haka ne yayin rantsar da kwamishina na farko na ma’aikatar ci gaban kiwon dabbobi da aka kafa kwanan nan, Farfesa Salim Abdurrahman Lawal, a zauren majalisar zartarwa na gidan gwamnati da ke Dutse.
A cewarsa, baya ga noma, kiwon dabbobi shi ne babban abin da mutanen jihar Jigawa suka sanya a gaba.
Malam Umar Namadi ya kara da cewa kafa wannan ma’aikata na cikin shirin gwamnati na bude manyan damarmaki da ke cikin wannan bangare.
“Mun dauki mataki na musamman domin ingantawa da bunkasa bangaren kiwon dabbobi. Mun yi hadin gwiwa da dama, mun yi tuntuba da dama, kuma nan gaba kadan za a fara ganin sakamakon wannan tuntuba. Bisa wannan dalili muka ga ya dace mu kafa ma’aikatar da za ta jagoranci wannan aiki gaba.”
Game da zaben kwamishina na farko, Gwamna Namadi ya bayyana kwarin gwiwa a kan kwarewar Farfesa Salim Abdurrahman.
“Mutumin da aka rantsar a matsayin kwamishina na kiwon dabbobi, kwararre ne kuma masanin a wannan fannin. Daga digirinsa na farko zuwa na biyu har na uku (PhD), duk ya yi su ne akan ilimin dabbobi. Don haka babu wani da ya fi dacewa da wannan aiki fiye da Farfesa Salim.”
Yayin da yake taya Farfesa Salim Abdurrahman murna, Gwamnan ya tunasar da shi muhimmancin wannan mukami na farko da yake rike da shi, yana mai kira gare shi da ya yi aiki domin amfanin jama’ar jihar Jigawa.
“Ina sanar da kai cewa kana daf da kafa tarihi domin kai ne kwamishina na farko na wannan ma’aikata. Don haka idan ma’aikatar ta yi tasiri ga rayuwar mutanen jihar Jigawa, tarihi zai yi alfahari da kai”.
Namadi ya yi addu’ar samun nasarar wannan ma’aikata wajen inganta rayuwar al’umma a fadin jihar.
Usman Mohammed Zaria